• English
  • Business News
Saturday, July 12, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Nazari Kan Taraktoci 2,000 Da Tinubu Ya Kaddamar Don Bunkasa Noma

by Abubakar Abba
4 hours ago
in Noma Da Kiwo
0
Nazari Kan Taraktoci 2,000 Da Tinubu Ya Kaddamar Don Bunkasa Noma
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

A kokarin Nijeriya na samar da sauyi, domin inganta fannin aikin noma, a ranar 23 ga watan Yunin 2025 ne, gwamnatin shugaba Bola Tinubu, ta kaddamar da Taraktocin noma 2,000.

Ta kaddamar da Taraktocin ne, karkashin shirin nan na gwamnatinsa ‘Renewed Hope’, don aiwatar da noma zamani.

  • Rashin Ganin Shugabannin APC Yayin Ziyarar Shettima A Kano Ya Haifar Da Zazzafar Muhawara
  • 2027: Takarar Shugaban Kasa Zan Yi Ba Mataimaki Ba – Peter Obi

Gwamatin ta yi hakan ne, domin kara bunkasa aikin noma da samar da wadataccen abinci a fannin aikin noma, domin samun riba.

Kaddamar da Taraktocin, ya nuna irin kudurin gwamnatin; na komawa aikin noma tare kuma da amfani da kayan noman na zamani.

A cewar fadar shugaban kasa, gwamnatin ta samar da wannan dauki ne, domin cike gibin da kasar ke da shi na karancin kayan aikin noma na zamani tare kuma da kara habaka fannin aikin noma.

Labarai Masu Nasaba

Dalilin Ware Naira Biliyan 19.5 Da Asusun Bunkasa Aikin Noma Ya Yi

Dalilin Kwararru Na Bukatar Kafa Cibiyoyin Bincike Kan Nau’ikan Dabbobi A Nijeriya

Har ila yau, manufar ita ce; don rage yawan asarar da manoma ke tabkawa, bayan sun yi girbin farko da kuma jawo hankalin matasan kasar, domin su rungumi aikin na noma; musamman wanda za su yi, su samu riba.

Kaddamar da Taraktocin na zuwa ne, daidai da lokacin da kasar ke ci gaba da fuskantar hauhawar farashin kayan abinci, wanda ya kai sama da kashi 30 cikin 100, duba da cewa; noman da ake yi a karkara na ci gaba yin karanci.

Idan har an rabar da wadannan Taraktoci yadda ya dace tare da horar da manoman da za su amfana, an kuma tabbatar da ana bai wa Taraktocin kulawar da ta kamata da sayar da su cikin rahusa, hakan zai taimaka wajen samun kyakkyawan sauyi a fannin noman kasar, musamman a bangaren samun riba.

Sai dai, har yanzu; tambayar da ake ci gaba da yi ita ce, shin ko wannan shiri zai samar da kyakkyawan sauyi a fannin na aikin noman kasar?

Hakikanin Fannin Aikin Noma Don Samun Riba A Nijeriya:

Fannin aikin noman kasar, na samar da ayyukan yi sama da kashi 70 cikin 100, inda kuma fannin ya kasance kimanin kashi 34 cikin 100 na aikin da ake yi a kasar.

Amma duk da haka, har yanzu fannin kashi 26 kacal yake bayarwa a matsayin gudunmawa, don bunkasa tattalin arzikin kasar, wanda akasari hakan na faruwa ne, sakamakon yadda ake yin noma da kayan aiki na gargajiya.

Nijeriya da ke Afirka ta Kudu da Hamada, aikin nomanta ya yi kasa sakamakon rashin yin aiki da kayan noma na zamani. Ta kuma kasance, tana da kasa da karamin ma’auni na hekta da ya kimanin 0.3, wanda hakan ya saba da shawarar da Hukumar Kula da Abinci da Ayyukan Noma ta Majalisar Dinkin Duniya (FAO) ta bayar na bukatar samar da hekta 1.5 na yin noma.

Bugu da kari, an rawaito Mataimakin Shugaban Kasa, Sanata Kashim Shettima ya bayyana cewa; Nijeriya mai yawan al’umma sama da miliyan 210, amma abin takaici, kasar na da Taraktocin noma masu aiki daga tsakanin 7,000 zuwa 12,000 ne kacal.

A cewarsa, hakan ya sanya a shekaru da dama da suka gabata, aka gaza samun bukatar da ake da ita ta samar da yawan abincin da ya kai mililiyan 2.4, domin bukatar ‘yan kasar.

Sai dai, ana ganin bisa wannan sabon yunkuri na gwamnatin ta hanyar hadaka da kamfanin kera kayan aikin noma da ke Belarus, wanda aka kaddamar da aikin tare da AfTrade DMCC, hakan ya sa an samar da ingantattun Taraktocin noma 2,000 tare da samar da kayan haro 190 da sauran makamantansu.

A karkashin aikin, ana sa ran za a noma hektar noma sama da 550,000, wadanda za su samar da tan miliyan 2 na hatsi tare da samar da ayyukan yi, wadanda ba na kai tsaye ba kimanin 16,000 da kuma na kai tsaye kimanin sama da 550,000.

Kaddamar da Taraktocin da sauran kayan aiki, hakan zai taimaka wajen habaka aikin noma don samun riba da kara bunkasa samar da wadataccen abinci da rage shigo da kayan abinci cikin Nijeriya, wanda yanzu haka, wadanda ake shigo da su a duk shekara, kudinsu ya kai sama da dala biliyan 2.5

Samar Da Wadataccen Abinci Da Matsalar Samun Hauhawar Farashin Kayan Abinci A Nijeriya:

Duk da samar da albarkar hektocin noma da Nijeriya ke da su, wadanda suka kai miliyan 70.8 kuma ake noma amfanin gona kamar irin su; Masara, Rogo, Shinkafa da saurasu, amma kasar na ci gaba da fuskantar hauhawar farashin kayan abinci.

Fannin shi ne kusan kashin bayan bunkasa tattalin arzikin kasar, amma sama da ‘yan kasar miliyan 100 ne a yanzu ke fuskantar karancin abinci, kuma suna ci gaba da fuskantar hauhawar farashin kayan na abinci da kuma rashin wadatattun kudaden sayen kayan abincin.

Wannan adadin, ya nuna yadda yanayin hauhawar farashin ya yi kamari, musamman a Arewa ta Tsakiyar kasar, wanda ya kai kashi 29.43 a Arewa ta Gabas, ya kai kashi 29.72.

Bugu da kari, kididdiga ta nuna cewa; ‘yan Nijeriya miliyan 18.6 ke ci gaba da jure wa yunwa, inda kuma mutane miliyan 43.7, suka dauki matakin rage cin abincin da suke ciyar da iyalansu.

‘Yan Nijeriya miliyan 133 ke ci gaba da fuskantar karancin ababen more rayuwa tare da ci gaba da fuskantar hauhawar farashin kayan abinci, wanda a watan Mayun 2025 ya kai kashi 21.14 tare da kuma fuskantar matsananciyar yunwa.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: Noma
ShareTweetSendShare
Previous Post

Rashin Ganin Shugabannin APC Yayin Ziyarar Shettima A Kano Ya Haifar Da Zazzafar Muhawara

Next Post

Dalilin Ware Naira Biliyan 19.5 Da Asusun Bunkasa Aikin Noma Ya Yi

Related

Wa’adin Da Tinubu Ya Bai Wa Manoman Da Suka Ci Bashin ‘Anchor Borrowers’ Ya Cika
Noma Da Kiwo

Dalilin Ware Naira Biliyan 19.5 Da Asusun Bunkasa Aikin Noma Ya Yi

2 hours ago
Dalilin Kwararru Na Bukatar Kafa Cibiyoyin Bincike Kan Nau’ikan Dabbobi A Nijeriya
Noma Da Kiwo

Dalilin Kwararru Na Bukatar Kafa Cibiyoyin Bincike Kan Nau’ikan Dabbobi A Nijeriya

1 week ago
Tinubu Ya Kaddamar Da Sabon Shirin Aikin Noma Don Samar Da Wadataccen Abinci
Noma Da Kiwo

Tinubu Ya Kaddamar Da Sabon Shirin Aikin Noma Don Samar Da Wadataccen Abinci

1 week ago
Madarar Shanu Da Nijeriya Ke Samarwa Ta Karu Da Tan Miliyan 1.4 A Shekara Biyar
Noma Da Kiwo

Madarar Shanu Da Nijeriya Ke Samarwa Ta Karu Da Tan Miliyan 1.4 A Shekara Biyar

2 weeks ago
Abin Da Ya Sa Ilimi Yake Da Muhimmanci Ga Rayuwar Al’umma (6)
Noma Da Kiwo

Nijeriya Da Brazil Sun Ƙulla Yarjejeniyar Horar Da Matasa Kiwon Dabbobi

3 weeks ago
Abin Da Ya Sa Ilimi Yake Da Muhimmanci Ga Rayuwar Al’umma (6)
Noma Da Kiwo

Hikimar Yunƙurin Sake Farfaɗo Da Noman Filanten A Jihar Nasarawa

3 weeks ago
Next Post
Wa’adin Da Tinubu Ya Bai Wa Manoman Da Suka Ci Bashin ‘Anchor Borrowers’ Ya Cika

Dalilin Ware Naira Biliyan 19.5 Da Asusun Bunkasa Aikin Noma Ya Yi

LABARAI MASU NASABA

‘Yansanda Sun Ceto Mutum 21 Da Aka Sace, Sun Kwato N4.8m Kuɗin Fansa

‘Yansanda Sun Damke Mutum Shida Kan Kisan Da Aka Yi A Kasuwar Abuja

July 12, 2025
Sojoji Sun Cafke Wani Soja Kan Mutuwar Mai Gyaran Waya A Adamawa

Sojoji Sun Cafke Wani Soja Kan Mutuwar Mai Gyaran Waya A Adamawa

July 12, 2025
Kotu Ta Umarci Majalisar Dattijan Nijeriya Da Ta Gaggauta Janye Dakatarwar Da Ta Yi Wa Natasha

Lauyoyin Natasha Sun Buƙaci Ta Koma Majalisa Ranar Talata Bayan Miƙa Takardun Hukuncin Kotu

July 12, 2025
Wa’adin Da Tinubu Ya Bai Wa Manoman Da Suka Ci Bashin ‘Anchor Borrowers’ Ya Cika

Dalilin Ware Naira Biliyan 19.5 Da Asusun Bunkasa Aikin Noma Ya Yi

July 12, 2025
Nazari Kan Taraktoci 2,000 Da Tinubu Ya Kaddamar Don Bunkasa Noma

Nazari Kan Taraktoci 2,000 Da Tinubu Ya Kaddamar Don Bunkasa Noma

July 12, 2025
Kashim Shettima Ya Mayar Da Martani Kan Tsadar Rayuwa

Rashin Ganin Shugabannin APC Yayin Ziyarar Shettima A Kano Ya Haifar Da Zazzafar Muhawara

July 12, 2025
Sin Na Goyon Bayan G20 Ta Ci Gaba Da Ba Da Kyakkyawar Gudummawa

Sin Na Goyon Bayan G20 Ta Ci Gaba Da Ba Da Kyakkyawar Gudummawa

July 11, 2025
Hadakar Jam’iyyar ADC Ta Fara Dusashe Karfin PDP A Wasu Jihohin Nijeriya

Hadakar Jam’iyyar ADC Ta Fara Dusashe Karfin PDP A Wasu Jihohin Nijeriya

July 11, 2025
Kasar Sin Na Da Muradin Zurfafa Hadin Gwiwar BRI Da Masar 

Kasar Sin Na Da Muradin Zurfafa Hadin Gwiwar BRI Da Masar 

July 11, 2025
Nijeriya Na Fuskantar Siyasa Mara Tabbas —  Peter Obi

2027: Takarar Shugaban Kasa Zan Yi Ba Mataimaki Ba – Peter Obi

July 11, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.