ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Monday, August 3, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Nazari Kan Taraktoci 2,000 Da Tinubu Ya Kaddamar Don Bunkasa Noma

by Abubakar Abba
1 year ago
Noma

A kokarin Nijeriya na samar da sauyi, domin inganta fannin aikin noma, a ranar 23 ga watan Yunin 2025 ne, gwamnatin shugaba Bola Tinubu, ta kaddamar da Taraktocin noma 2,000.

Ta kaddamar da Taraktocin ne, karkashin shirin nan na gwamnatinsa ‘Renewed Hope’, don aiwatar da noma zamani.

  • Rashin Ganin Shugabannin APC Yayin Ziyarar Shettima A Kano Ya Haifar Da Zazzafar Muhawara
  • 2027: Takarar Shugaban Kasa Zan Yi Ba Mataimaki Ba – Peter Obi

Gwamatin ta yi hakan ne, domin kara bunkasa aikin noma da samar da wadataccen abinci a fannin aikin noma, domin samun riba.

ADVERTISEMENT

Kaddamar da Taraktocin, ya nuna irin kudurin gwamnatin; na komawa aikin noma tare kuma da amfani da kayan noman na zamani.

A cewar fadar shugaban kasa, gwamnatin ta samar da wannan dauki ne, domin cike gibin da kasar ke da shi na karancin kayan aikin noma na zamani tare kuma da kara habaka fannin aikin noma.

LABARAI MASU NASABA

Kha’amuna Khadi Ta Karɓi Jagorancin Gudanarwa Ta Bankin Noma

Dalilin Da Ya Sa Aka Horar Da Manoman Tumatir 100 A Garin Zariya

Har ila yau, manufar ita ce; don rage yawan asarar da manoma ke tabkawa, bayan sun yi girbin farko da kuma jawo hankalin matasan kasar, domin su rungumi aikin na noma; musamman wanda za su yi, su samu riba.

Kaddamar da Taraktocin na zuwa ne, daidai da lokacin da kasar ke ci gaba da fuskantar hauhawar farashin kayan abinci, wanda ya kai sama da kashi 30 cikin 100, duba da cewa; noman da ake yi a karkara na ci gaba yin karanci.

Idan har an rabar da wadannan Taraktoci yadda ya dace tare da horar da manoman da za su amfana, an kuma tabbatar da ana bai wa Taraktocin kulawar da ta kamata da sayar da su cikin rahusa, hakan zai taimaka wajen samun kyakkyawan sauyi a fannin noman kasar, musamman a bangaren samun riba.

Sai dai, har yanzu; tambayar da ake ci gaba da yi ita ce, shin ko wannan shiri zai samar da kyakkyawan sauyi a fannin na aikin noman kasar?

Hakikanin Fannin Aikin Noma Don Samun Riba A Nijeriya:

Fannin aikin noman kasar, na samar da ayyukan yi sama da kashi 70 cikin 100, inda kuma fannin ya kasance kimanin kashi 34 cikin 100 na aikin da ake yi a kasar.

Amma duk da haka, har yanzu fannin kashi 26 kacal yake bayarwa a matsayin gudunmawa, don bunkasa tattalin arzikin kasar, wanda akasari hakan na faruwa ne, sakamakon yadda ake yin noma da kayan aiki na gargajiya.

Nijeriya da ke Afirka ta Kudu da Hamada, aikin nomanta ya yi kasa sakamakon rashin yin aiki da kayan noma na zamani. Ta kuma kasance, tana da kasa da karamin ma’auni na hekta da ya kimanin 0.3, wanda hakan ya saba da shawarar da Hukumar Kula da Abinci da Ayyukan Noma ta Majalisar Dinkin Duniya (FAO) ta bayar na bukatar samar da hekta 1.5 na yin noma.

Bugu da kari, an rawaito Mataimakin Shugaban Kasa, Sanata Kashim Shettima ya bayyana cewa; Nijeriya mai yawan al’umma sama da miliyan 210, amma abin takaici, kasar na da Taraktocin noma masu aiki daga tsakanin 7,000 zuwa 12,000 ne kacal.

A cewarsa, hakan ya sanya a shekaru da dama da suka gabata, aka gaza samun bukatar da ake da ita ta samar da yawan abincin da ya kai mililiyan 2.4, domin bukatar ‘yan kasar.

Sai dai, ana ganin bisa wannan sabon yunkuri na gwamnatin ta hanyar hadaka da kamfanin kera kayan aikin noma da ke Belarus, wanda aka kaddamar da aikin tare da AfTrade DMCC, hakan ya sa an samar da ingantattun Taraktocin noma 2,000 tare da samar da kayan haro 190 da sauran makamantansu.

A karkashin aikin, ana sa ran za a noma hektar noma sama da 550,000, wadanda za su samar da tan miliyan 2 na hatsi tare da samar da ayyukan yi, wadanda ba na kai tsaye ba kimanin 16,000 da kuma na kai tsaye kimanin sama da 550,000.

Kaddamar da Taraktocin da sauran kayan aiki, hakan zai taimaka wajen habaka aikin noma don samun riba da kara bunkasa samar da wadataccen abinci da rage shigo da kayan abinci cikin Nijeriya, wanda yanzu haka, wadanda ake shigo da su a duk shekara, kudinsu ya kai sama da dala biliyan 2.5

Samar Da Wadataccen Abinci Da Matsalar Samun Hauhawar Farashin Kayan Abinci A Nijeriya:

Duk da samar da albarkar hektocin noma da Nijeriya ke da su, wadanda suka kai miliyan 70.8 kuma ake noma amfanin gona kamar irin su; Masara, Rogo, Shinkafa da saurasu, amma kasar na ci gaba da fuskantar hauhawar farashin kayan abinci.

Fannin shi ne kusan kashin bayan bunkasa tattalin arzikin kasar, amma sama da ‘yan kasar miliyan 100 ne a yanzu ke fuskantar karancin abinci, kuma suna ci gaba da fuskantar hauhawar farashin kayan na abinci da kuma rashin wadatattun kudaden sayen kayan abincin.

Wannan adadin, ya nuna yadda yanayin hauhawar farashin ya yi kamari, musamman a Arewa ta Tsakiyar kasar, wanda ya kai kashi 29.43 a Arewa ta Gabas, ya kai kashi 29.72.

Bugu da kari, kididdiga ta nuna cewa; ‘yan Nijeriya miliyan 18.6 ke ci gaba da jure wa yunwa, inda kuma mutane miliyan 43.7, suka dauki matakin rage cin abincin da suke ciyar da iyalansu.

‘Yan Nijeriya miliyan 133 ke ci gaba da fuskantar karancin ababen more rayuwa tare da ci gaba da fuskantar hauhawar farashin kayan abinci, wanda a watan Mayun 2025 ya kai kashi 21.14 tare da kuma fuskantar matsananciyar yunwa.

Noma
Abubakar Abba
+ postsBio
  • Abubakar Abba
    https://hausa.leadership.ng/author/abubakar-abba/
    Kha’amuna Khadi Ta Karɓi Jagorancin Gudanarwa Ta Bankin Noma
  • Abubakar Abba
    https://hausa.leadership.ng/author/abubakar-abba/
    Matatar Man Ɗangote Ta Samu Ƙarin Ribar Dala Biliyan 2.5 A Ɓangaren Zuba Jari
  • Abubakar Abba
    https://hausa.leadership.ng/author/abubakar-abba/
    Sabon Rahoton Bankin Duniya Ya Yaba Da Yadda Tattalin Arzkin Nijeriya Ke Bunkasa
  • Abubakar Abba
    https://hausa.leadership.ng/author/abubakar-abba/
    Nijeriya Ta Tabka Asarar Naira Biliyan 2.61 A Samar Da Wuta A Zangon Farko Na 2026 —NERC

MASU ALAKA

Abin Da Ya Sa Gidauniyar NADF Da Bankin Manoma Suka Yi Haḍaka
Noma Da Kiwo

Kha’amuna Khadi Ta Karɓi Jagorancin Gudanarwa Ta Bankin Noma

August 1, 2026
Dalilin Da Ya Sa Aka Horar Da Manoman Tumatir 100 A Garin Zariya
Noma Da Kiwo

Dalilin Da Ya Sa Aka Horar Da Manoman Tumatir 100 A Garin Zariya

July 18, 2026
Labarin Farfesoshi Tagwaye Da Suka Yi Karatun Digiri Tare Suna Aiki Tare A Wuri Ɗaya
Noma Da Kiwo

Sharhi A Kan Dabarun Zamani Na Yin Auren Ƴaƴan Itatuwa

July 11, 2026
Next Post
Wa’adin Da Tinubu Ya Bai Wa Manoman Da Suka Ci Bashin ‘Anchor Borrowers’ Ya Cika

Dalilin Ware Naira Biliyan 19.5 Da Asusun Bunkasa Aikin Noma Ya Yi

LABARAI MASU NASABA

DSS

DSS Da ‘Yan Sa-kai Sun Kashe Fitaccen Jagoran ‘Yan Bindiga Da Mayaƙansa Sama Da 60 A Katsina

August 3, 2026
Sin Ta Yi Maraba Da Yarjejeniyar Fahimtar Juna Da Aka Cimma Tsakanin Amurka Da Iran

Iran Ta Musanta Iƙirarin Trump Kan Sabbin Tattaunawa da Amurka

August 3, 2026
Zamfara

‘Yan Ta’adda Sun Kashe Sojoji Shida, Sun Sace Mutane 75 A Zamfara

August 3, 2026
Alkalin Babbar Kotun Kebbi Ya Shaƙi Iskar ‘Yanci, Bayan Shafe Mako Guda A Hannun ‘Yan Bindiga

Alkalin Babbar Kotun Kebbi Ya Shaƙi Iskar ‘Yanci, Bayan Shafe Mako Guda A Hannun ‘Yan Bindiga

August 3, 2026
Kamfanin Abinci Na ‘BUA Foods’ Ya Samu Ribar ₦292.27bn A Rabin Farkon 2026

Kamfanin Abinci Na ‘BUA Foods’ Ya Samu Ribar ₦292.27bn A Rabin Farkon 2026

August 3, 2026
Noma

WAFCON 2026: Ƴan Wasan Nijeriya 2 Ba Zasu Buga Wasan Ƙarshe Na Rukunin C Ba

August 2, 2026
Babban Bankin Sin: Za A Ci Gaba Da Gudanar Da Matakan Saukaka Harkokin Kudade

Babban Bankin Sin: Za A Ci Gaba Da Gudanar Da Matakan Saukaka Harkokin Kudade

August 2, 2026
Yawan Tikitin Kallon Fina Finan Sin Da Aka Sayar A 2026 Ya Zarce Yuan Biliyan 23

Yawan Tikitin Kallon Fina Finan Sin Da Aka Sayar A 2026 Ya Zarce Yuan Biliyan 23

August 2, 2026
Noma

Sojoji Sun Daƙile Harin Ƴan Ta’adda, Sun Ceto Mutane 9 A Zamfara

August 2, 2026
Sin Ta Fitar Da Shirin Shekaru 5 Na Daukaka Tsarin Tallata Da Samar Da Kayayyaki Domin Kyautata Hidimomi A Kauyuka

Sin Ta Fitar Da Shirin Shekaru 5 Na Daukaka Tsarin Tallata Da Samar Da Kayayyaki Domin Kyautata Hidimomi A Kauyuka

August 2, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.