• English
  • Business News
Tuesday, June 10, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

NEDC Ta Raba Wa Mutanen Da Ambaliyar Ruwa Ta Shafa Kayan Abinci A Jihar Bauchi

by Khalid Idris Doya
3 years ago
in Rahotonni
0
NEDC Ta Raba Wa Mutanen Da Ambaliyar Ruwa Ta Shafa Kayan Abinci A Jihar Bauchi
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Babban daraktan gudanarwa na hukumar bunkasa shiyyar Arewa Maso Gabas (NEDC), Mohammed G. Alkali, ya nuna aniyar hukumar na yin hadin guiwar Gwamnatin jihar Bauchi domin labibo hanyoyin magance ambaliyar ruwa domin kiyaye barnar da hakan ka iya yi a nan gaba a fadin jihar.

Alhaji Mohammed G. Alkali ya yi bayanin cewa sun zo jihar Bauchi a ranar Laraba ne domin mika kyautar kayan abinci da wasu kayan bukatun yau da gobe ga wadanda ambaliyar ruwa ta shafa domin rage musu radadin halin da suke ciki a jihar ta Bauchi.

  • Gwamnatin Tarayya Ta Raba Buhunan Abinci 4,200 Ga Marasa Karfi A Bauchi

Goni, ya kuma kara da jajanta wa gwamnati da al’ummar jihar bisa wannan ambaliyar ruwa da ta shafi jihar a bana da ya shafi wasu sassan jihar.

Ya yi bayanin kayan abinci da na sanyawa da suka bai wa jihar da cewa sun hada da buhunan shinkafa dubu 10 (10,000), bargunan rufuwa guda 5,000, atamfa na mata guda 5,000, shadda na maza guda 3,000, tabarma guda dubu biyar (5,000), galan din Mangeda guda 3,000, rigunan yara guda 3,000 da kuma dukka an mika su ga Gwamnatin jihar Bauchi da nufin rabawa ga wadanda lamarin ya shafa.

NEDC

Labarai Masu Nasaba

2027: An Yi Kira Ga Masu Mulki Da Su Rungumi Tafarkin Inganta Rayuwar Al’umma

Tsadar Rayuwa: Yadda Al’umma Suka Yi Sallah Cikin Kunci

MD, ya jinjina wa gwamnan Jihar Bauchi bisa kokarinsa na taimakawa ga wadanda ambaliyar ta shafa, ya yi fatan kayan abinci da wadanda ba na abincin da suka kawo jihar za su rage radadin tare da tallafawa ga wadanda ambaliyar ta shafa a jihar.

Alhaji Goni daga bisani ya yi magana kan ayyukan da hukumar ke gudanarwa a jihar Bauchi da suka hada da aikin hanyar Kirfi zuwa Gombe Abba, da ayyuka a sashin Ilimi, lafiya da sauran fannoni gami da saura da dama.

“Sannan, muna da aikin gina gidaje da ake ciki gaba da yi, sannan da aiki a daya daga cikin manyan cibiyoyin ilimi da na lafiya na jiha ko na tarayya, da kuma ayyukan su na cigaba da gudana.”

A nasa fannin, gwamna Bala Muhammad na Jihar, ya nuna matukar farin cikinsa bisa wannan tallafin da hukumar ta bai wa jihar, yana mai cewa samar da hukumar NEDC na daga cikin muhimman tarihi da nasarorin da shugaban kasa Muhammadu Buhari ya kafa a zamansa Shugaban kasa.

Ya ce, hukumar na daga cikin rassan da ke gudanar da ayyukansu da ke zuwa ga talakawa da al’umma kai tsaye, kuma sa a jima ana amfanuwa da ayyukan da suke gudanarwa.

Ya kuma jinjina kan yadda hukumar ke gudanar da ayyukanta na farfado da shiyyar Arewa Maso Gabas da hare-haren Boko Haram ya daidaiya a shekarun baya.

Gwamna Bala ya sanar da bakin nasa cewa tabbas ambaliyar ruwa ta yi barna sosai a jihar, ya nuna cewa hatta shi kansa da Gwamnatinsa sun yi kokarin samar da tallafin gaggawa ga wadanda lamarin ya shafa, ya nuna cewa lamarin ne ya yi yawa sosai amma sun yi kokari sosai wajen samar da nasu tallafin a matakin jihar.

NEDC

Kan hakan ne ya nuna cewa kayan tallafin abinci da na wadanda ba abinci ba da suka samu daga hukumar za su taimaka sosai ga wadanda ambaliyar ta shafa.

Kana, ya jinjina da ayyukan da hukumar ke gudanarwa a jihar da cewa tabbas hakan na taimaka wa rayuwar al’ummar jihar.

Daga bisani ne kuma MD, Alkali ya mika kayan tallafin da suka kawo jihar ta hannun mataimakin gwamnan Jihar Bauchi Sanata Baba Tela da nufin rabawa ga wadanda lamarin ya shafa.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

ShareTweetSendShare
Previous Post

Dan Chinan Da Ake Zargi Da Kisan Budurwarsa ‘Ummita’ A Kano Ya Musanta Aikata Kisan

Next Post

Xi Ya Jagoranci Shugabannin JKS Zuwa Tsohuwar Hedkwatar Jam’iyyar  

Related

NEDC
Rahotonni

2027: An Yi Kira Ga Masu Mulki Da Su Rungumi Tafarkin Inganta Rayuwar Al’umma

3 days ago
Tsadar Rayuwa: Yadda Al’umma Suka Yi Sallah Cikin Kunci
Rahotonni

Tsadar Rayuwa: Yadda Al’umma Suka Yi Sallah Cikin Kunci

4 days ago
Ana Fargabar Boko Haram Ta Kara Mamaye Wasu Kananan Hukumomi A Borno
Rahotonni

Ana Fargabar Boko Haram Ta Kara Mamaye Wasu Kananan Hukumomi A Borno

1 week ago
Kokarin Minista Tuggar Na Mayar Da Hijirar Masana Daga Nijeriya Zuwa Kasashen Waje Alhairi
Rahotonni

Kokarin Minista Tuggar Na Mayar Da Hijirar Masana Daga Nijeriya Zuwa Kasashen Waje Alhairi

1 week ago
Faduwar Jarrabawar JAMB Ta Tayar Da Bukatar Neman Sake Fasalin Hukumar
Rahotonni

Faduwar Jarrabawar JAMB Ta Tayar Da Bukatar Neman Sake Fasalin Hukumar

2 weeks ago
Gwamna Umar Namadi Ya Dauki Matakan Kai Jihar Jigawa Babban Matsayi
Rahotonni

Gwamna Umar Namadi Ya Dauki Matakan Kai Jihar Jigawa Babban Matsayi

2 months ago
Next Post
Xi Ya Jagoranci Shugabannin JKS Zuwa Tsohuwar Hedkwatar Jam’iyyar  

Xi Ya Jagoranci Shugabannin JKS Zuwa Tsohuwar Hedkwatar Jam’iyyar  

LABARAI MASU NASABA

Gwamnatin Borno Ta Nemi A Gaggauta Yashe Alo Dam Don Guje Wa Sabuwar Ambaliya

Gwamnatin Borno Ta Nemi A Gaggauta Yashe Alo Dam Don Guje Wa Sabuwar Ambaliya

June 10, 2025
Bam Ya Hallaka Masu Yawon Sallah A Sakkwato

Bam Ya Hallaka Masu Yawon Sallah A Sakkwato

June 10, 2025
Mataimakin Firaministan Sin Ya Gana Da Ministar Kudin Birtaniya

Mataimakin Firaministan Sin Ya Gana Da Ministar Kudin Birtaniya

June 9, 2025
An Kaddamar Da Taron Farko Na Tattauna Batutuwan Tattalin Arziki Da Cinikayya Na Sin Da Amurka A London

An Kaddamar Da Taron Farko Na Tattauna Batutuwan Tattalin Arziki Da Cinikayya Na Sin Da Amurka A London

June 9, 2025
Shin Rashin Nasara Ya Rage Damar Yamal Na Ballon d’Or?

Shin Rashin Nasara Ya Rage Damar Yamal Na Ballon d’Or?

June 9, 2025
Kididiga Ta Nuna Yadda Kasar Sin Ke Samun Bunkasar Tattalin Arzikin Teku

Kididiga Ta Nuna Yadda Kasar Sin Ke Samun Bunkasar Tattalin Arzikin Teku

June 9, 2025
Kasashen Da Sin Ta Bai Wa Jama’arsu Izinin Shiga Kasar Ba Tare Da Biza Ba Ya Karu Zuwa 47

Kasashen Da Sin Ta Bai Wa Jama’arsu Izinin Shiga Kasar Ba Tare Da Biza Ba Ya Karu Zuwa 47

June 9, 2025
Gwamnatin Bauchi Ta Buɗe Sabon Tsarin Neman Ƙirƙirar Sabbin Masarautu

Gwamnatin Bauchi Ta Buɗe Sabon Tsarin Neman Ƙirƙirar Sabbin Masarautu

June 9, 2025
Ma’aunin Farashin Kayan Masarufi Na Watan Mayu A Kasar Sin Ya Ragu Da Kaso 0.1 Bisa Dari

Ma’aunin Farashin Kayan Masarufi Na Watan Mayu A Kasar Sin Ya Ragu Da Kaso 0.1 Bisa Dari

June 9, 2025
Ma’aikatar Tsaron Kasar Sin Ta Gargadi Mahukuntan Taiwan Game Da Sayen Makamai Daga Amurka

Ma’aikatar Tsaron Kasar Sin Ta Gargadi Mahukuntan Taiwan Game Da Sayen Makamai Daga Amurka

June 9, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.