• Leadership Hausa
Monday, February 6, 2023
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Sana’a Sa’a
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Sana’a Sa’a
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result
Home Labarai

Nijeriya Ba Za Ta Bunkasa Ba Sai Da Ingantacciyar Wutar Lantarki – Tambuwal 

by Sharfaddeen Sidi Umar, Sokoto
5 months ago
in Labarai
0
Nijeriya Ba Za Ta Bunkasa Ba Sai Da Ingantacciyar Wutar Lantarki – Tambuwal 

Gwamna Aminu Waziri Tambuwal na Jihar Sakkwato, ya bayyana cewar akwai kalubale sosai a fannin samar da wutar lantarki a kasar nan wanda ya zama wajibi idan a na son samun ci gaba mai ma’ana a dauki gabaran matakai domin shawo kan matsalolin.

Ya ce fannin wuta na bukatar kwararru kuma gogaggun hannaye wadanda suke jajirtattu ta hanyar yin aiki da gaske domin shawo kan tarin manyan kalubalen da fannin ya jima yana fuskanta.

  • Cristiano Ronaldo Ya Yi Watsi Da Karbar Albashi Mafi Tsoka A Duniya
  • ‘Yansanda A Ebonyi Sun Damke Wasu Masoya Da Suka Sayar Da Jaririnsu A Kan Kudi N500,000

Ya ce Nijeriya za ta iya samun ci-gaba ne kadai a matsayin Kasa idan ta na da ingantacciyar wutar lantarki.

Ya ce kashe tsohuwar NEPA bai samu cikakkiyar nasara ba, har yanzu akwai kalubale sosai amma kuma za a iya shawo kan su idan Gwamnati da gaske take yi.

Gwamnan ya yi wannan bayanin ne a yayin da ya karbi bakuncin sabon Shugaban Hukumar Gudanarwar Kamfanin Wutar Lantarki na KAEDCO, Alhaji Abbas Muhammad Jega a Fadar Gwamnatin Sakkwato.

Labarai Masu Nasaba

Dalilan Da Ke Hana Kwamfuta Da Wayoyin Hannu Sauri

Ko Mafarkin Samun Gwamna Mace Ta Farko A Nijeriya Zai Zama Gaskiya?

“Kasashe da dama sun yi, me zai hana mu ma mu yi? Ba za mu samu nasarar cika alkawulan mu ba, ba za mu gano damar da muke da ita ba idan ba mu gyara fannin wuta ba.” Ya bayyana.

Ya ce duk fannonin ci-gaba mafi yawa sun dogara ne ga samun wuta wanda a kan hakan ne ya ce Gwamnatinsa ta na goyon bayan bunkasa fannin wutar lantarki wanda a bisa ga wannan ne Gwamnatinsa ta kashe makuddan kudade wajen samar da na’urorin taransifoma da daga darajar layukan wuta a fadin Jihar.

Gwamnan ya bukaci Kamfanin da su rika amfani da tsarin lissafin kudin wutar da aka ci maimakon hasashe ba tare da lissafi ba.Ya ce ta hanyar sanya na’urar mita, hasashen kudin wuta da ake yi zai ragu sosai, wanda hakan zai sa a samu gagarumar nasara a kokarin da ake yi na bunkasa fannin samar da wuta.

Tambuwal wanda ya ce yin amfani da tsarin biyan wutar da aka sha, shine mafi dacewa kamar yadda kamfanonin sadarwa ke yi wanda jama’a ke jin dadin tsarin, don haka me zai hana a yi shi a fannin wuta?” gwamnan ya tambaya.

Ya ce yin hakan zai zama alfanu ga kamfanin domin za a gano kwastomomi na kwarai wadanda ke biyan wuta, haka ma wadanda ke biyan wuta za su gamsu kuma su ga alfanun biyan kudinsu kuma za rika cajinsu yadda ya kamata.

A jawabinsa Abbas Jega ya bayar da tabbacin cewar tattaunawar Kamfanin da Gwamnatin Jihar Sakkwato da jin bukatocin kwastomomin su ya karfafa fahimtar juna da samar da sakamako mai kyau a kakkarfan kamfani da samun wuta a kodayaushe a Jihar.

Ya kuma bayyana nauyin matsalolin da aka gabatar tare da bayar da tabbacin za su kara tashi tsaye wajen magance matsalolin tare da kara inganta bayar da hasken wuta da rage korafe- korafen jama’a.

Tags: Bunkasa Tattalin ArzikiCi GabaSakkwatoTambuwalWutar Lantarki
Previous Post

Yadda Taron Marubuta Na Arewacin Nijeriya Ya Gudana A Jihar Katsina

Next Post

‘Yansanda Sun Kashe ‘Yan Bindiga 2, Sun Ceto Uwa Da Danta A Kwara

Related

Dalilan Da Ke Hana Kwamfuta Da Wayoyin Hannu Sauri
Rahotonni

Dalilan Da Ke Hana Kwamfuta Da Wayoyin Hannu Sauri

4 hours ago
Ko Mafarkin Samun Gwamna Mace Ta Farko A Nijeriya Zai Zama Gaskiya?
Labarai

Ko Mafarkin Samun Gwamna Mace Ta Farko A Nijeriya Zai Zama Gaskiya?

5 hours ago
NAHCON Ta Rarraba Kujerun Aikin Hajjin Bana Ga Jihohi 36 Da Abuja
Labarai

NAHCON Ta Rarraba Kujerun Aikin Hajjin Bana Ga Jihohi 36 Da Abuja

7 hours ago
Matar Sufeto Ta Gurfanar Da Kurtun Dan Sanda A Kotu Kan Kashe Mijinta
Kotu Da Ɗansanda

Ya Kashe Makocinsa Don Ya Haske Idon Mahaifiyarsa Da Cocila

10 hours ago
Majalisar Dinkin Duniya Ta Yi Tir Da Kisan Fulani 40 A Jihar Nasarawa
Labarai

Majalisar Dinkin Duniya Ta Yi Tir Da Kisan Fulani 40 A Jihar Nasarawa

12 hours ago
Sojoji Sun Kama Mutum 116 Da Ke Yin Laifuka Daban-daban A Legas
Kotu Da Ɗansanda

Sojoji Sun Kama Mutum 116 Da Ke Yin Laifuka Daban-daban A Legas

13 hours ago
Next Post
Ango Da Wasu Mutum Shida Sun Mutu A Inugu

'Yansanda Sun Kashe 'Yan Bindiga 2, Sun Ceto Uwa Da Danta A Kwara

LABARAI MASU NASABA

Afirka Ba Ta Bukatar Lakca

Afirka Ba Ta Bukatar Lakca

February 5, 2023
Manoman Kwakwa 50 Sun Samu Horo Kan Noman Zamani

Manoman Kwakwa 50 Sun Samu Horo Kan Noman Zamani

February 5, 2023
Sin Na Matukar Adawa Da Matakin Amurka Na Harbo Babban Balan-balan Din Kasar Sin

Sin Na Matukar Adawa Da Matakin Amurka Na Harbo Babban Balan-balan Din Kasar Sin

February 5, 2023
Dalilan Da Ke Hana Kwamfuta Da Wayoyin Hannu Sauri

Dalilan Da Ke Hana Kwamfuta Da Wayoyin Hannu Sauri

February 5, 2023
Ko Mafarkin Samun Gwamna Mace Ta Farko A Nijeriya Zai Zama Gaskiya?

Ko Mafarkin Samun Gwamna Mace Ta Farko A Nijeriya Zai Zama Gaskiya?

February 5, 2023
Shirin Fim Na Tallata Shagalin Murnar Bikin Kunna Fitilu Da CMG Ya Tsara Ya Jawo Hankulan Al’ummar Afirka

Shirin Fim Na Tallata Shagalin Murnar Bikin Kunna Fitilu Da CMG Ya Tsara Ya Jawo Hankulan Al’ummar Afirka

February 5, 2023
An Gudanar Da Jerin Ayyuka Don Murnar Cika Shekara 1 Da Samun Nasarar Gudanar Da Wasannin Olympics Na Lokacin Sanyi Na Beijing

An Gudanar Da Jerin Ayyuka Don Murnar Cika Shekara 1 Da Samun Nasarar Gudanar Da Wasannin Olympics Na Lokacin Sanyi Na Beijing

February 5, 2023
NAHCON Ta Rarraba Kujerun Aikin Hajjin Bana Ga Jihohi 36 Da Abuja

NAHCON Ta Rarraba Kujerun Aikin Hajjin Bana Ga Jihohi 36 Da Abuja

February 5, 2023
Matar Sufeto Ta Gurfanar Da Kurtun Dan Sanda A Kotu Kan Kashe Mijinta

Ya Kashe Makocinsa Don Ya Haske Idon Mahaifiyarsa Da Cocila

February 5, 2023
Gwamnan Jigawa Ya Nada Hameem Nuhu Sanusi Matsayin Sabon Sarkin Dutse

Gwamnan Jigawa Ya Nada Hameem Nuhu Sanusi Matsayin Sabon Sarkin Dutse

February 5, 2023
ADVERTISEMENT
Advertise with us

© 2022 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2022 Leadership Media Group - All Right Reserved.