ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Thursday, June 4, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Yadda Taron Marubuta Na Arewacin Nijeriya Ya Gudana A Jihar Katsina

by El-Zaharadeen Umar
4 years ago
Taron Marubuta

Kungiyar marubuta ta arewacin Najeriya ‘Nigeria Northern Writers Forum’ ta shirya taron marubutan arewa domin lalubo hanyoyin da za a magance matsalar tsaro a yankin arewa da ma ƙasa baki ɗaya.

Taron na bana, anyi masa take da Amfani da rubuce-rubucen adabi da harsuna a matsayin makamin yaki da matsalar tsaro a yankin arewa da Najeriya baki ɗaya.

Kazalika masana da masu sharhi akan tsaro sun gudanar da ƙasidoji daban-daban da suke da alaƙa da hanya mafi sauki wajan tunkarar matsalar tsaro.

ADVERTISEMENT

Tun da farko da yake jawabin maraba shugaban kungiyar marubuta Arewacin Najeriya, Dakta Bishir Abusabe ya yi ƙarin haske akan taron na bana wanda ya ce an taɓo batun matsalar da ta addabi yankin arewa.

Ya ce taron zai kasance wani ɗan ba na ƙarfafa gwiwar marubuta saboda irin gudunmawar da suke badawa wajan haɓaka harsuna da adabi.

LABARAI MASU NASABA

2027: Kasancewa Ɗan Arewa Kaɗai Ba Zai Tabbatar Da Samun Ƙuri’u Ba – Baba-Ahmed

Gwamnatin Tarayya Ta Mayar Da Ofishin NAGGW Zuwa Kano Domin Yaƙi Da Hamada

“Mu anan jihar Katsina muna alfahari da manyan kuma sananun marubuta irin su Abubakar Imam da sauran su, saboda ƙoƙarin da suka yi wajan samar adabi da zai amfani wannan al’umma shekaru da dama masu zuwa.” Inji shi

Dakta Bishir Abusabe ya yaba da ƙoƙarin gwamnatin jihar Katsina ƙarƙashin jagorancin gwamna Aminu Bello Masari musamman irin tallafin da take ba marubuta da harkar rubutu a jihar Katsina.

Shima a nasa jawabin Ferfesa Saleh Abdu wanda ya gabatar da ƙasida  akan hanyoyin da ya kamata a bi ta hanyar amfani da adabin gargajiya wajan magance matsalar tsaro a arewacin Najeriya da ma ƙasa baki ɗaya.

Ya ƙara da cewa adabi hanya ce mafi sauki wajan isar da sako musamman a yanayi da kuma tsari irin na Hausa Fulani da kuma Malam Bahaushe.

Da yake jawabi a wajan taron gwamnan jihar Katsina Aminu Bello Masari ya yaba da ƙoƙarin marubuta wajan bunƙasa al’ada acikin al’umma domin isar da muhimmin sako akan wani al’amari kuma kwalliya ta biya kuɗin sabulu.

 

  • Nijeriya Ba Za Ta Bunkasa Ba Sai Da Ingantacciyar Wuta – Tambuwal 
  • IAEA: Za A Tattauna Batun Hadin Gwiwa Tsakanin Amurka Da Birtaniya Da Australiya

 

Taron Marubuta
Wasu daga cikin mahalarta taron

Gwamnan wanda ya samu wakilcin kwamishinan yaɗa labarai, al’adu da harkokin cikin gida, Alhaji Abdulkarim Yahaya Sirika ya  jadadda aniyar gwamnati wajan haɗa hannu da kungiyar marubuta ta arewacin Najeriya wajan ciyar da ilimi gaba.

Haka kuma ya bayyana cewa daman gwamna Aminu Bello Masari ya ɗauki harkar ilimi a matsayin lamba ɗaya tun zuwan gwamnatin sa, ya ƙara da cewa kungiyar marubuta suna da rawar da za su taka wajan cimma nasarori a tsare-tsaren gwamnati.

” Gwamnatin mu zata cigaba da haɗa hannu da kungiyar marubuta wajan ƙara inganta hanyoyin samar da ilimi a jihar Katsina sannan ya yaba da ƙoƙarin marubuta akan samar da litattafan nazari da bincike ga ɗaliban ilmin.”

Taron Marubuta
Yadda taron ya gudana a Jihar Katsina

Daga ƙarshe ya jaddada goyon bayan gwamnatin jihar Katsina na cigaba da taimakawa marubuta da rubutu a matsayin wani kaso na gudunmawar gwamnatin jihar Katsina.

Wasu daga cikin waɗanda suka gabatar da ƙasida a wannan taron sun haɗa da Ferfesa Saleh Abdu na jami’ar Gwamnatin Tarayyar da ke jihar Gombe da Ferfesa Idris Amale da tsohon shugaban kungiyar Malam Muhammad Kabir Sani da fitaccen mawaki Aminu Abubakar Ladan (Alan Waƙa)

Sannan an gabatar da bada kyaututukan girmamawa ga wasu fitattun mutane da suka haɗa da gwamnan jihar Katsina Aminu Bello Masari da sauran jama’a.

Taron Marubuta
El-Zaharadeen Umar
+ postsBio
  • El-Zaharadeen Umar
    https://hausa.leadership.ng/author/el-zaharadeen-umar/
    Batun Kammala Aikin Gina Gidaje 250 Na “Renewed Hope” Ya Bar Baya Da Kura A Jihar Katsina
  • El-Zaharadeen Umar
    https://hausa.leadership.ng/author/el-zaharadeen-umar/
    Yusuf Buhari Ya Halarci Zaɓen Fidda Gwani Na Sanatan Shiyyar Daura
  • El-Zaharadeen Umar
    https://hausa.leadership.ng/author/el-zaharadeen-umar/
    Mace Ta Doke Namiji A Zaɓen Fidda Gwani Na Majalisar Tarayya A Katsina
  • El-Zaharadeen Umar
    https://hausa.leadership.ng/author/el-zaharadeen-umar/
    Gayyato Jakadun Kasashen Waje 17 Ya Kara Wa Bukukuwan Sallah Armashi A Katsina

MASU ALAKA

Atiku Ne Ya Fi Dacewa Da Tikitin Takara A ADC Amma Ya Kamata Ya Janye — Baba-Ahmed
Labarai

2027: Kasancewa Ɗan Arewa Kaɗai Ba Zai Tabbatar Da Samun Ƙuri’u Ba – Baba-Ahmed

June 4, 2026
Gwamnatin Tarayya Ta Mayar Da Ofishin NAGGW Zuwa Kano Domin Yaƙi Da Hamada
Labarai

Gwamnatin Tarayya Ta Mayar Da Ofishin NAGGW Zuwa Kano Domin Yaƙi Da Hamada

June 4, 2026
Mambobin NYSC 4, Soja da Mutum 1 Sun Rasu A Hatsarin Mota A Adamawa
Labarai

Mambobin NYSC 4, Soja da Mutum 1 Sun Rasu A Hatsarin Mota A Adamawa

June 4, 2026
Next Post
Nijeriya Ba Za Ta Bunkasa Ba Sai Da Ingantacciyar Wutar Lantarki – Tambuwal 

Nijeriya Ba Za Ta Bunkasa Ba Sai Da Ingantacciyar Wutar Lantarki - Tambuwal 

LABARAI MASU NASABA

Atiku Ne Ya Fi Dacewa Da Tikitin Takara A ADC Amma Ya Kamata Ya Janye — Baba-Ahmed

2027: Kasancewa Ɗan Arewa Kaɗai Ba Zai Tabbatar Da Samun Ƙuri’u Ba – Baba-Ahmed

June 4, 2026
Gwamnatin Tarayya Ta Mayar Da Ofishin NAGGW Zuwa Kano Domin Yaƙi Da Hamada

Gwamnatin Tarayya Ta Mayar Da Ofishin NAGGW Zuwa Kano Domin Yaƙi Da Hamada

June 4, 2026
Mambobin NYSC 4, Soja da Mutum 1 Sun Rasu A Hatsarin Mota A Adamawa

Mambobin NYSC 4, Soja da Mutum 1 Sun Rasu A Hatsarin Mota A Adamawa

June 4, 2026
Sarki Sanusi II Ya Tuɓe Rawanin Mai Unguwar Rikadawa Kan Badaƙalar Fili

Sarki Sanusi II Ya Tuɓe Rawanin Mai Unguwar Rikadawa Kan Badaƙalar Fili

June 4, 2026
Tawagar Masanan Dakile Yaduwar Cututtuka Ta Sin Ta Isa DR Congo

Tawagar Masanan Dakile Yaduwar Cututtuka Ta Sin Ta Isa DR Congo

June 3, 2026
Uba Sani Ya Sanya Hannu Kan Sabbin Dokoki A Bangaren Sauya Fannin Wuta, Noma, Da Muhalli

Uba Sani Ya Sanya Hannu Kan Sabbin Dokoki A Bangaren Sauya Fannin Wuta, Noma, Da Muhalli

June 3, 2026
Han Zheng Zai Halarci Taron SPIEF Karo Na 29 A Rasha Tare Da Gudanar Da Ziyarar Aiki A Belarus

Han Zheng Zai Halarci Taron SPIEF Karo Na 29 A Rasha Tare Da Gudanar Da Ziyarar Aiki A Belarus

June 3, 2026
Majalisa Ta Nemi Tinubu Ya Canza Dabarun Yaƙi Da Ta’addanci Don Kawo Ƙarshen Kashe-kashe

’Yan Majalisar Tarayya 3 Sun Fice Daga APC Zuwa ADC da PRP

June 3, 2026
An Fara Watsa Shirye-Shirye Masu Taken “Sha’awar Xi Jinping Ga Al’adu” Da Sauran Fina-Finan Bayyana Labaran Sin A Kasar Laos

An Fara Watsa Shirye-Shirye Masu Taken “Sha’awar Xi Jinping Ga Al’adu” Da Sauran Fina-Finan Bayyana Labaran Sin A Kasar Laos

June 3, 2026
Tambuwal Ya Jajanta Wa Waɗanda Harin ’Yan Bindiga Ya Shafa A Sokoto, Ya Nemi A Ƙara Tsaro

Tambuwal Ya Jajanta Wa Waɗanda Harin ’Yan Bindiga Ya Shafa A Sokoto, Ya Nemi A Ƙara Tsaro

June 3, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.