ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Wednesday, September 9, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Yadda Taron Marubuta Na Arewacin Nijeriya Ya Gudana A Jihar Katsina

by El-Zaharadeen Umar
4 years ago
Taron Marubuta

Kungiyar marubuta ta arewacin Najeriya ‘Nigeria Northern Writers Forum’ ta shirya taron marubutan arewa domin lalubo hanyoyin da za a magance matsalar tsaro a yankin arewa da ma ƙasa baki ɗaya.

Taron na bana, anyi masa take da Amfani da rubuce-rubucen adabi da harsuna a matsayin makamin yaki da matsalar tsaro a yankin arewa da Najeriya baki ɗaya.

Kazalika masana da masu sharhi akan tsaro sun gudanar da ƙasidoji daban-daban da suke da alaƙa da hanya mafi sauki wajan tunkarar matsalar tsaro.

ADVERTISEMENT

Tun da farko da yake jawabin maraba shugaban kungiyar marubuta Arewacin Najeriya, Dakta Bishir Abusabe ya yi ƙarin haske akan taron na bana wanda ya ce an taɓo batun matsalar da ta addabi yankin arewa.

Ya ce taron zai kasance wani ɗan ba na ƙarfafa gwiwar marubuta saboda irin gudunmawar da suke badawa wajan haɓaka harsuna da adabi.

LABARAI MASU NASABA

‘Yan Bindiga Sun Kashe 2, Sun Yi Garkuwa Da 26 A Kaduna

Gwamna Radda Ya Gabatar Da Kasafin N828.6bn Na 2027

“Mu anan jihar Katsina muna alfahari da manyan kuma sananun marubuta irin su Abubakar Imam da sauran su, saboda ƙoƙarin da suka yi wajan samar adabi da zai amfani wannan al’umma shekaru da dama masu zuwa.” Inji shi

Dakta Bishir Abusabe ya yaba da ƙoƙarin gwamnatin jihar Katsina ƙarƙashin jagorancin gwamna Aminu Bello Masari musamman irin tallafin da take ba marubuta da harkar rubutu a jihar Katsina.

Shima a nasa jawabin Ferfesa Saleh Abdu wanda ya gabatar da ƙasida  akan hanyoyin da ya kamata a bi ta hanyar amfani da adabin gargajiya wajan magance matsalar tsaro a arewacin Najeriya da ma ƙasa baki ɗaya.

Ya ƙara da cewa adabi hanya ce mafi sauki wajan isar da sako musamman a yanayi da kuma tsari irin na Hausa Fulani da kuma Malam Bahaushe.

Da yake jawabi a wajan taron gwamnan jihar Katsina Aminu Bello Masari ya yaba da ƙoƙarin marubuta wajan bunƙasa al’ada acikin al’umma domin isar da muhimmin sako akan wani al’amari kuma kwalliya ta biya kuɗin sabulu.

 

  • Nijeriya Ba Za Ta Bunkasa Ba Sai Da Ingantacciyar Wuta – Tambuwal 
  • IAEA: Za A Tattauna Batun Hadin Gwiwa Tsakanin Amurka Da Birtaniya Da Australiya

 

Taron Marubuta
Wasu daga cikin mahalarta taron

Gwamnan wanda ya samu wakilcin kwamishinan yaɗa labarai, al’adu da harkokin cikin gida, Alhaji Abdulkarim Yahaya Sirika ya  jadadda aniyar gwamnati wajan haɗa hannu da kungiyar marubuta ta arewacin Najeriya wajan ciyar da ilimi gaba.

Haka kuma ya bayyana cewa daman gwamna Aminu Bello Masari ya ɗauki harkar ilimi a matsayin lamba ɗaya tun zuwan gwamnatin sa, ya ƙara da cewa kungiyar marubuta suna da rawar da za su taka wajan cimma nasarori a tsare-tsaren gwamnati.

” Gwamnatin mu zata cigaba da haɗa hannu da kungiyar marubuta wajan ƙara inganta hanyoyin samar da ilimi a jihar Katsina sannan ya yaba da ƙoƙarin marubuta akan samar da litattafan nazari da bincike ga ɗaliban ilmin.”

Taron Marubuta
Yadda taron ya gudana a Jihar Katsina

Daga ƙarshe ya jaddada goyon bayan gwamnatin jihar Katsina na cigaba da taimakawa marubuta da rubutu a matsayin wani kaso na gudunmawar gwamnatin jihar Katsina.

Wasu daga cikin waɗanda suka gabatar da ƙasida a wannan taron sun haɗa da Ferfesa Saleh Abdu na jami’ar Gwamnatin Tarayyar da ke jihar Gombe da Ferfesa Idris Amale da tsohon shugaban kungiyar Malam Muhammad Kabir Sani da fitaccen mawaki Aminu Abubakar Ladan (Alan Waƙa)

Sannan an gabatar da bada kyaututukan girmamawa ga wasu fitattun mutane da suka haɗa da gwamnan jihar Katsina Aminu Bello Masari da sauran jama’a.

Taron Marubuta
El-Zaharadeen Umar
+ postsBio
  • El-Zaharadeen Umar
    https://hausa.leadership.ng/author/el-zaharadeen-umar/
    Cutar Mashako:Yadda Yara Ke Mutuwar Bazata A Jihohin Katsina Da Kano
  • El-Zaharadeen Umar
    https://hausa.leadership.ng/author/el-zaharadeen-umar/
    Mauludin Annabi (SAW): Shugaba Tinubu Ya Nemi A Yi Addu’o’in Nasara Kan Matsalar Tsaro
  • El-Zaharadeen Umar
    https://hausa.leadership.ng/author/el-zaharadeen-umar/
    Shekaru 8 Cikin Raɗaɗi: Wani Bawan Allah Ya Samu Tiyata Kyauta Daga Gidauniyar Mangal
  • El-Zaharadeen Umar
    https://hausa.leadership.ng/author/el-zaharadeen-umar/
    Tinubu Ya Nemi Malamai Su Taimaka Wajen Yaƙi Da Ƴan Ta’adda

MASU ALAKA

'Yan Bindiga
Labarai

‘Yan Bindiga Sun Kashe 2, Sun Yi Garkuwa Da 26 A Kaduna

September 8, 2026
Yadda Taron Tattalin Arziki Da Zuba Jari Na Kwana Biyu Ya Gudana A Katsina
Labarai

Gwamna Radda Ya Gabatar Da Kasafin N828.6bn Na 2027

September 8, 2026
Gwamnan Kebbi Ya Bayyana Shirin Sake Duba Albashin Malaman Firamare
Labarai

Gwamna Idris Ya Rushe Majalisar Shugabannin Hukumar Zaɓe Ta Kebbi

September 8, 2026
Next Post
Nijeriya Ba Za Ta Bunkasa Ba Sai Da Ingantacciyar Wutar Lantarki – Tambuwal 

Nijeriya Ba Za Ta Bunkasa Ba Sai Da Ingantacciyar Wutar Lantarki - Tambuwal 

LABARAI MASU NASABA

Batun AI Zai Fi Daukar Hankali A Bikin Baje Kolin Fasahar Zamani Ta Duniya Karo Na 5

Batun AI Zai Fi Daukar Hankali A Bikin Baje Kolin Fasahar Zamani Ta Duniya Karo Na 5

September 8, 2026
Gwamna Radda Ya Samu Goyon Bayan APC A Katsina Gabanin Zaɓen 2027

Gwamna Radda Ya Samu Goyon Bayan APC A Katsina Gabanin Zaɓen 2027

September 8, 2026
Cinikin Wajen Sin Ya Ci Gaba Da Samun Bunkasa Cikin Sauri A Watanni Takwas Na Farkon Bana

Cinikin Wajen Sin Ya Ci Gaba Da Samun Bunkasa Cikin Sauri A Watanni Takwas Na Farkon Bana

September 8, 2026
'Yan Bindiga

‘Yan Bindiga Sun Kashe 2, Sun Yi Garkuwa Da 26 A Kaduna

September 8, 2026
Binciken CGTN Ya Nuna Gamsuwa Da Yadda Baje Kolin CIFTIS Ke Shaida Karfin Gwiwar Sin A Fannin Kara Fadada Bude Kofa Bisa Babban Matsayi

Binciken CGTN Ya Nuna Gamsuwa Da Yadda Baje Kolin CIFTIS Ke Shaida Karfin Gwiwar Sin A Fannin Kara Fadada Bude Kofa Bisa Babban Matsayi

September 8, 2026
Yadda Taron Tattalin Arziki Da Zuba Jari Na Kwana Biyu Ya Gudana A Katsina

Gwamna Radda Ya Gabatar Da Kasafin N828.6bn Na 2027

September 8, 2026
Sin Za Ta Yi Aiki Tare Da Sassa Daban Daban Domin Mayar Da Fasahar AI Wata Dama Ta Cin Gajiya Mai Dorewa

Sin Za Ta Yi Aiki Tare Da Sassa Daban Daban Domin Mayar Da Fasahar AI Wata Dama Ta Cin Gajiya Mai Dorewa

September 8, 2026
Gwamnan Kebbi Ya Bayyana Shirin Sake Duba Albashin Malaman Firamare

Gwamna Idris Ya Rushe Majalisar Shugabannin Hukumar Zaɓe Ta Kebbi

September 8, 2026
Han Zheng Ya Halarci Baje Kolin CIFIT Karo Na 26 Tare Da Gabatar Da Jawabi

Han Zheng Ya Halarci Baje Kolin CIFIT Karo Na 26 Tare Da Gabatar Da Jawabi

September 8, 2026
Wani Soja Ya Kashe Kansa Bayan Kashe Matarsa A Jihar Neja

Kano Za Ta Kafa Sansanonin Sojoji A Ƙananan Hukumomin Da Ke Fuskantar Barazanar Tsaro

September 8, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.