ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Saturday, July 25, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Yadda Taron Marubuta Na Arewacin Nijeriya Ya Gudana A Jihar Katsina

by El-Zaharadeen Umar
4 years ago
Taron Marubuta

Kungiyar marubuta ta arewacin Najeriya ‘Nigeria Northern Writers Forum’ ta shirya taron marubutan arewa domin lalubo hanyoyin da za a magance matsalar tsaro a yankin arewa da ma ƙasa baki ɗaya.

Taron na bana, anyi masa take da Amfani da rubuce-rubucen adabi da harsuna a matsayin makamin yaki da matsalar tsaro a yankin arewa da Najeriya baki ɗaya.

Kazalika masana da masu sharhi akan tsaro sun gudanar da ƙasidoji daban-daban da suke da alaƙa da hanya mafi sauki wajan tunkarar matsalar tsaro.

ADVERTISEMENT

Tun da farko da yake jawabin maraba shugaban kungiyar marubuta Arewacin Najeriya, Dakta Bishir Abusabe ya yi ƙarin haske akan taron na bana wanda ya ce an taɓo batun matsalar da ta addabi yankin arewa.

Ya ce taron zai kasance wani ɗan ba na ƙarfafa gwiwar marubuta saboda irin gudunmawar da suke badawa wajan haɓaka harsuna da adabi.

LABARAI MASU NASABA

Kyamar Baki: Shettima Ya Ja Kunnen Gwamnatin Afirka Ta Kudu

Yadda Kasar Sin Ta Samar Da Ci Gaba Na Bai Daya

“Mu anan jihar Katsina muna alfahari da manyan kuma sananun marubuta irin su Abubakar Imam da sauran su, saboda ƙoƙarin da suka yi wajan samar adabi da zai amfani wannan al’umma shekaru da dama masu zuwa.” Inji shi

Dakta Bishir Abusabe ya yaba da ƙoƙarin gwamnatin jihar Katsina ƙarƙashin jagorancin gwamna Aminu Bello Masari musamman irin tallafin da take ba marubuta da harkar rubutu a jihar Katsina.

Shima a nasa jawabin Ferfesa Saleh Abdu wanda ya gabatar da ƙasida  akan hanyoyin da ya kamata a bi ta hanyar amfani da adabin gargajiya wajan magance matsalar tsaro a arewacin Najeriya da ma ƙasa baki ɗaya.

Ya ƙara da cewa adabi hanya ce mafi sauki wajan isar da sako musamman a yanayi da kuma tsari irin na Hausa Fulani da kuma Malam Bahaushe.

Da yake jawabi a wajan taron gwamnan jihar Katsina Aminu Bello Masari ya yaba da ƙoƙarin marubuta wajan bunƙasa al’ada acikin al’umma domin isar da muhimmin sako akan wani al’amari kuma kwalliya ta biya kuɗin sabulu.

 

  • Nijeriya Ba Za Ta Bunkasa Ba Sai Da Ingantacciyar Wuta – Tambuwal 
  • IAEA: Za A Tattauna Batun Hadin Gwiwa Tsakanin Amurka Da Birtaniya Da Australiya

 

Taron Marubuta
Wasu daga cikin mahalarta taron

Gwamnan wanda ya samu wakilcin kwamishinan yaɗa labarai, al’adu da harkokin cikin gida, Alhaji Abdulkarim Yahaya Sirika ya  jadadda aniyar gwamnati wajan haɗa hannu da kungiyar marubuta ta arewacin Najeriya wajan ciyar da ilimi gaba.

Haka kuma ya bayyana cewa daman gwamna Aminu Bello Masari ya ɗauki harkar ilimi a matsayin lamba ɗaya tun zuwan gwamnatin sa, ya ƙara da cewa kungiyar marubuta suna da rawar da za su taka wajan cimma nasarori a tsare-tsaren gwamnati.

” Gwamnatin mu zata cigaba da haɗa hannu da kungiyar marubuta wajan ƙara inganta hanyoyin samar da ilimi a jihar Katsina sannan ya yaba da ƙoƙarin marubuta akan samar da litattafan nazari da bincike ga ɗaliban ilmin.”

Taron Marubuta
Yadda taron ya gudana a Jihar Katsina

Daga ƙarshe ya jaddada goyon bayan gwamnatin jihar Katsina na cigaba da taimakawa marubuta da rubutu a matsayin wani kaso na gudunmawar gwamnatin jihar Katsina.

Wasu daga cikin waɗanda suka gabatar da ƙasida a wannan taron sun haɗa da Ferfesa Saleh Abdu na jami’ar Gwamnatin Tarayyar da ke jihar Gombe da Ferfesa Idris Amale da tsohon shugaban kungiyar Malam Muhammad Kabir Sani da fitaccen mawaki Aminu Abubakar Ladan (Alan Waƙa)

Sannan an gabatar da bada kyaututukan girmamawa ga wasu fitattun mutane da suka haɗa da gwamnan jihar Katsina Aminu Bello Masari da sauran jama’a.

Taron Marubuta
El-Zaharadeen Umar
+ postsBio
  • El-Zaharadeen Umar
    https://hausa.leadership.ng/author/el-zaharadeen-umar/
    Sana’ar Kilishi:Yadda Ta Bunkasa Daga Jihar Katsina Zuwa Wasu Sassan Nijeriya
  • El-Zaharadeen Umar
    https://hausa.leadership.ng/author/el-zaharadeen-umar/
    Yadda Gidauniyar Ɗahiru Mangal Ta Tallafa Wa Marasa Lafiya 30,000 A Katsina
  • El-Zaharadeen Umar
    https://hausa.leadership.ng/author/el-zaharadeen-umar/
    Ko Shirin Da Gwamnatin Jihar Katsina Ke Yi Wa Manoma Zai  Amfane Su A wannan Daminar?
  • El-Zaharadeen Umar
    https://hausa.leadership.ng/author/el-zaharadeen-umar/
    Mutum 1,000 Daga Jam’iyyar ADC Sun Koma PDP A Jihar Katsina

MASU ALAKA

Kashim Shettima Ya Mayar Da Martani Kan Tsadar Rayuwa
Labarai

Kyamar Baki: Shettima Ya Ja Kunnen Gwamnatin Afirka Ta Kudu

July 24, 2026
Yadda Kasar Sin Ta Samar Da Ci Gaba Na Bai Daya
Ra'ayi Riga

Yadda Kasar Sin Ta Samar Da Ci Gaba Na Bai Daya

July 24, 2026
NLC Ta Yi Barazanar Daukar Matakin Yajin Aiki Kan Albashi Mafi Karanci
Rahotonni

NLC Ta Yi Barazanar Daukar Matakin Yajin Aiki Kan Albashi Mafi Karanci

July 24, 2026
Next Post
Nijeriya Ba Za Ta Bunkasa Ba Sai Da Ingantacciyar Wutar Lantarki – Tambuwal 

Nijeriya Ba Za Ta Bunkasa Ba Sai Da Ingantacciyar Wutar Lantarki - Tambuwal 

LABARAI MASU NASABA

An Karrama Masana Ilimin Lissafi Na Kasar Sin Da Lambobin Yabo Na Fields Medal

An Karrama Masana Ilimin Lissafi Na Kasar Sin Da Lambobin Yabo Na Fields Medal

July 24, 2026
Ta Da Zaune Tsaye Da Philippines Ta Yi A Teku Ba Zai Lalata Dangantakar Hadin Gwiwar Sin Da ASEAN Ba

Ta Da Zaune Tsaye Da Philippines Ta Yi A Teku Ba Zai Lalata Dangantakar Hadin Gwiwar Sin Da ASEAN Ba

July 24, 2026
Jadawalin INEC:Kotun Daukaka Kara Ta Kassara Fatan Jam’iyyu Da ‘Yan Siyasa

Jadawalin INEC:Kotun Daukaka Kara Ta Kassara Fatan Jam’iyyu Da ‘Yan Siyasa

July 24, 2026
An Zartas Da Sanarwar Chengdu A Taron Ministocin Kungiyar APEC Kan Harkar Raya Fasahohin Dijital Da AI

An Zartas Da Sanarwar Chengdu A Taron Ministocin Kungiyar APEC Kan Harkar Raya Fasahohin Dijital Da AI

July 24, 2026
NNPP Za Ta Kwace Mulki A Jihar Imo – Kwankwaso

Jam’iyyar NDC Ta Shirya Tsaf Domin Kafa Gwamnati A 2027 —Kwankwaso

July 24, 2026
Sin Ta Kara Kamfanoni 14 Na Tarayyar Turai Cikin Jerin Wadanda Aka Hana Fitar Masu Da Kaya

Sin Ta Kara Kamfanoni 14 Na Tarayyar Turai Cikin Jerin Wadanda Aka Hana Fitar Masu Da Kaya

July 24, 2026
Kashim Shettima Ya Mayar Da Martani Kan Tsadar Rayuwa

Kyamar Baki: Shettima Ya Ja Kunnen Gwamnatin Afirka Ta Kudu

July 24, 2026
Yadda Kasar Sin Ta Samar Da Ci Gaba Na Bai Daya

Yadda Kasar Sin Ta Samar Da Ci Gaba Na Bai Daya

July 24, 2026
Hatsin Da Kasar Sin Ta Girbe Da Lokacin Zafin Bana Ya Zarce Tan Miliyan 150

Hatsin Da Kasar Sin Ta Girbe Da Lokacin Zafin Bana Ya Zarce Tan Miliyan 150

July 24, 2026
Wani Dalilin Da Ya Sa Al’Ummar Afirka Ke Kaunar Kasar Sin Shi Ne Yadda Take Kokarin Zuba Musu Jari

Wani Dalilin Da Ya Sa Al’Ummar Afirka Ke Kaunar Kasar Sin Shi Ne Yadda Take Kokarin Zuba Musu Jari

July 24, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.