• English
  • Business News
Wednesday, October 8, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Nijeriya Da Amurka Sun Jaddada Kudurin Karfafa Kasuwanci A Tsakaninsu

byBello Hamza
1 year ago
Amurka

A halin yanzu Nijeriya da kasar Amurka sun jaddada shirin kara karfafa harkokin kasuwanci da zuba jari a tsakaninsu.

 

Wannann ya biyo bayan taron koli nena kasashen da ya gudana a tsakanin Ministar Masa’anatu, Kasuwanci da Zuba Jari na Nijeriya, Dakta Doris Uzoka-Anite, da tawagar kasar Amurka a karkashin jagorancin mataimakin sakatare mai kula da harkokin ciniki da kasuwanci tsakanin kasashen waje, Mista Arun Benkataraman, a Abuja ranar Laraba.

  • Zanga-zangar Tsadar Rayuwa Na Shirin Shiriricewa
  • Tinubu Ya Gana Da Gwamnonin APC Kan Zanga-zangar Matsin Rayuwa

Taron ya mayar da hankali ne wajen karfafawa tare da tabbatar da yarjejeniyar da ke tsakanin kasashen biyu da suka hada da shirin nan na (TIFA) da (AGOA) da (BNC) da kuma (CID) wadanda ke karfafa kasuwanci a tsakanin kasashen Afrika da duniya baki daya ba a manta da su ba.

 

LABARAI MASU NASABA

Bayan Shekara 20 Nijeriya Ta Sake Dawo Da Tsarin Bayar Da Hayar Kananan Jiragen Sama

Tashoshin Jiragen Ruwa Sun Samar Da Kashi 19.6 Na Fitar Da Kayan Da Ba Su Shafi Mai Ba—Dantsoho

Duka bangarorin sun karfafa bukatar fadada harkokin kasuwanci a tsakaninsu tare da kuma kirkiro da sabbin hanyoyin cimma bukatun kasashen nasu domin bunkasa tattalin arzikin juna.

 

Dakta Uzoka-Anite ta bayyana abubuwan da Amurka za ta amfana dasu a Nijeriya wadanda suka hada da kasancewar ta babbar kasuwar da babu irinta a nan kusa da kuma ma’adanai da Allah ya hore mana a sassan kasa, haka kuma muna da kwararru masu ilimi daban-daban da za a iya fitar dasu zuwa kasashen waje su amfanar da kasashe daban-daban,” in ji ta.

 

Ta kuma jinjina wa dangantakar da ke tsakanin Nijeriya da Amurka. “Nijeriya da Amurka sun dade suna hulda da juna na tsawon shekaru, suna mutunta juna tare da amfanar juna a bangarorin tattalin arziki da dama,” in ji ta.

 

A nasa jawabin, Benkataraman ya sanar da goyon bayan Amurka ga shirin farfado da tattalin arzikn kasa da kuma irin kalubalen da kamfanonin Amurka da ke harkoki a Nijeriya ke fuskanta.

 

“Za mu yi aiki domin karfafa dangantakar da ke tsakanin mu domin samun ci gaba da bunkasar tattalin arziki ta yadda al’ummar kasashen biyu za su amfana,” in ji shi.

 

Tawagar ta kasa Amurka ta nuna sha’awarta ga sauye-sauyen tattalin arziki da gwamnatin Tinubu take yi, sun kuma yi alkawarin bayar da gudummawarsu wajen karfafa kasuwanci da zuba jari a Nijeriya a daidai wannan lokacin.

 

Duka bangarorin sun amince da ci gaba da tattaunawa akai akai tsakaninsu don tabbatar da dorewar yarjejeniyar da aka kulla. An kammala taron tare da alkawarin kara karfafa kasuwanci da zuba jari a tsakanin kasashen biyu.

ShareTweetSendShare

MASU ALAKA

Bayan Shekara 20 Nijeriya Ta Sake Dawo Da Tsarin Bayar Da Hayar Kananan Jiragen Sama
Tattalin Arziki

Bayan Shekara 20 Nijeriya Ta Sake Dawo Da Tsarin Bayar Da Hayar Kananan Jiragen Sama

October 3, 2025
Tashoshin Jiragen Ruwa Sun Samar Da Kashi 19.6 Na Fitar Da Kayan Da Ba Su Shafi Mai Ba—Dantsoho
Tattalin Arziki

Tashoshin Jiragen Ruwa Sun Samar Da Kashi 19.6 Na Fitar Da Kayan Da Ba Su Shafi Mai Ba—Dantsoho

October 3, 2025
Majalisar Wakilai Za Ta Sasanta Dangote Da NUPENG
Tattalin Arziki

Majalisar Wakilai Za Ta Sasanta Dangote Da NUPENG

September 27, 2025
Next Post
BUK

Jami’ar Bayero Ta Fito Da Kurakuran Da Ake Tafkawa A Rediyo Da Talabijin

LABARAI MASU NASABA

Tawagar Likitocin Sin Dake Saliyo Ta Gudanar Da Tiyatar Dashen Yatsa Irinta Ta Farko

Tawagar Likitocin Sin Dake Saliyo Ta Gudanar Da Tiyatar Dashen Yatsa Irinta Ta Farko

October 8, 2025
Babban Yankin Sin Ya Soki Lamirin Kalaman Aware Na Jagoran Yankin Taiwan

Babban Yankin Sin Ya Soki Lamirin Kalaman Aware Na Jagoran Yankin Taiwan

October 8, 2025
Yawan Zirga-Zirgar Jiragen Kasa Tsakanin Sin Da Turai Kan Layin Dogo Na Tsakiya Ya Zarce 3,000 A Bana

Yawan Zirga-Zirgar Jiragen Kasa Tsakanin Sin Da Turai Kan Layin Dogo Na Tsakiya Ya Zarce 3,000 A Bana

October 8, 2025
Majalisa Ta Nemi Jami’an Tsaro Su Ceto Daliban Jami’ar Gusau 30 Da Aka Sace

Kafa ‘Yansandan Jihohi Na Da Matuƙar Muhimmanci Wajen Magance Matsalar Rashin Tsaro

October 8, 2025
Adadin Kudaden Da Gidajen Sinima Na Sin Suka Tara Yayin Hutun Bikin Ranar Kasa Ya Haura Yuan Biliyan 1.7

Adadin Kudaden Da Gidajen Sinima Na Sin Suka Tara Yayin Hutun Bikin Ranar Kasa Ya Haura Yuan Biliyan 1.7

October 8, 2025
Tinubu

Tinubu Na Son A Saka Hannun Jari Da Kuɗaɗen Fansho A Ɓangaren Mai Da Iskar Gas

October 8, 2025
Gwamnatin Nasarawa Za Ta Hukunta Duk Masu Amfani Da Sinadiran Kamun Kifi Acikin Ruwa

Gwamnatin Nasarawa Za Ta Hukunta Duk Masu Amfani Da Sinadiran Kamun Kifi Acikin Ruwa

October 8, 2025
Sin: Ana Sa Ran Jigilar Fasinjoji Fiye Da Miliyan 21 A Yau Ta Jiragen Kasa

Sin: Ana Sa Ran Jigilar Fasinjoji Fiye Da Miliyan 21 A Yau Ta Jiragen Kasa

October 8, 2025
Kwastam Ta Kama Lita 35,000 Na Man Fetur, Tabar Wiwi Da Sauran Kayayyaki A Kebbi

Kwastam Ta Kama Lita 35,000 Na Man Fetur, Tabar Wiwi Da Sauran Kayayyaki A Kebbi

October 8, 2025
Sin Ta Yi Kira Ga Mambobin WTO Da Su Tinkari Yanayin Tangal-Tangal Tare

Sin Ta Yi Kira Ga Mambobin WTO Da Su Tinkari Yanayin Tangal-Tangal Tare

October 8, 2025

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Go to mobile version