Leadership Hausa Newspapers
No Result
View All Result
  • LABARAI
  • WASANNI
  • RAHOTANNI
  • SIYASA
  • KASUWANCI
  • ADABI
  • RA’AYINMU
  • TATTAUNAWA
  • BIDIYO
  • MAKALAR YAU
  • LABARAI
  • WASANNI
  • RAHOTANNI
  • SIYASA
  • KASUWANCI
  • ADABI
  • RA’AYINMU
  • TATTAUNAWA
  • BIDIYO
  • MAKALAR YAU
No Result
View All Result
Leadership Hausa Newspapers
No Result
View All Result
Home LABARAI

Nijeriya A Shekaru 57: Fadar Shugaban Ƙasa Ta Ayyana Nasarorin Gwamnatin Shugaba Buhari

by Tayo Adelaja
October 2, 2017
in LABARAI
4 min read
WhatsAppShare on FacebookShare on TwitterShare on Telegram

Daga Abubakar Abba

Fadar Shugaban ƙasa ta fitar da takarda akan cikar Nijeriya shekaru 57 da samun ’yancin kai, inda ta zayyana ɗimbin nasarorin da aka samar a ƙarƙashin  mulkin Shugaba Muhammadu Buhari.

Takardar wadda ta fito daga Ofishin Mataimakin Shugaban Ƙasa, Farfesa Yemi Osinbajo ta zayyana nasarorin akan fannoni daban-daban, waɗanda suka haɗa da; harkar tsaro da tattalin arzikin ƙasa, yaƙi da cin hanci da rashawa da sauransu.

Takardar ta ce, harkar  tsaro ita ce kan gaba a cikin jerin nasarorin da gwamnatin Buhari ta samar tun ɗarewarsa karagar mulki, cikin shekaru biyu da suka gabata.

Sauran nasarorin ƙarƙashin harkar tsaro sun haɗa da; magance rashin tsaro da daƙile ayyukan ‘yan Boko Haram a yankin Yamma Maso Kudu a ƙananan hukumomi 14 da suka mamaye da kuma sake gina rayuwar ‘yan yankin kimanin miliyan ɗaya waɗanda yaƙin ya ɗaiɗaita, waɗanda kuma tuni wasu sun koma yankunan su.

Fadar ta kuma zayyana nasarar da ta samu wajen magance masu yin garkuwa da mutane a ɗaukacin faɗin ƙasar nan, haɗe da cafko gaggan iyayen gidan masu aikata garkuwa da mutane da fasa inda suke ɓoye mutane in sun yi garkuwa da su a ɗaukacin faɗin ƙasar.

Gwamnatin ta kuma dawo da martabar Sojoji, inda aka wadata su da makamai, ta hanyar sawo masu jiragen yaƙi guda 12 masu suna ‘Super-Tucano’ akan kuɗi Dalar Amurka miliyan 600 don taimaka wa aikin su a Yamma Maso Kudu da kuma ci gaba da tabbatar da zaman lafiya

a yankin Neja Delta da kuma ci gaba da tura kuɗaɗe a shirin gwamnatin tarayya na afuwa ga tsagerun ‘yankin.

Gwamnatin ta kuma ce ta samu nasara wajen ƙirƙirar; bayar da tallafi na kaitsaye ga ‘yan gudun hijira da yaƙin Yamma Maso Gabas da yaƙin Boko Haram ya ɗaiɗaita, ƙarƙashin shirinta na musamman.

A kan harkar tattalin arzikin ƙasa kuwa, takardar ta zayyana nasarorin da ta samu waɗanda suka haɗa da; ƙaddamar da maido da tattalin arzikin ƙasa  da kuma tsamo taɓarwarewar  tattalin arzikin ƙasa data tsinci kanta a shekaru 29 duk da arzkin da aka samu ta hanyar Man fetur.

Ta bayyana cewar, an kashe Naira tiriliyan 1.2 wajen samar da ababen more rayuwa akan ayyukan da aka gudanar a ɗaukacin faɗin ƙasar nan, inda ta bayyana cewar, wannan ɗimbin nasara ce a bisa tarihin ƙasar nan.

Gwamnatin ta buga misali da ƙaddamar da tsarin lambar Banki ta BƁN, wanda ta ce, ta yi ne da nufin daƙile cin hanci da rashawa da rufe hanyar karkatar da kuɗin gwamnati ta hanyar ƙirƙirar Asusun bogi a Bankuna.

Don samar da sauƙi wajen gudanar da harkar kasuwanci kuwa, gwamnatin ta rattaba hannu akan dokar ƙudirin Majalisar ƙasar don bada damar gudanar da cinikayya ta shekarar 2017, ta bada damar samar da bashi ga ‘yan ƙasa cikin sauƙi, musamman wajen inganta kayan da ake

sarrafawa a cikin ƙasa.

Kafa zauren tuntuɓa da ke ƙarkashin fadar Gwamnatin Tarayya na gudanar da harkar kasuwanci a duk tsakiyar shekara, wanda ake tattaunawa da kamfanoni masu zaman kansu don bunƙasa tattalin arzikin ƙasa da kuma mayar da cibiyoyin gwamnatin kan tsarin gudanar da aikin gwamnati ta hanyar ‘E-goɓernance’ da kuma ƙirƙiro da gidauniyar yin amfani da na’urar zamani don ciyar da tattalin arzikin ƙasa gaba.

Akan yaƙi da cin hanci da rashawan dai, gwamnatin ta bayyana cewar, an samu nasarar hukunta jami’an gwamnati da ake zargi da hannu dumu-dumu wajen cin hanci da rashawa kuma an samu  nasarori wajen ƙwato ɗimbin biliyoyin nairori na gwamnati da aka sace.

Gwamnatin ta ce, ta samu nasara wajen kafa tsarinta na busa Wusir da kuma sanya hannu akan Dokar gwamnati ta ‘004’ ta faɗar abin da jami’an gwamanti suke samu da kayan da suka mallaka, wanda an ƙirƙiro da dokar ce don wayar da kai da amince wa ƙara samar da kuɗin haraji da magance masu kaucewa biyan haraji.

An kuma samu nasara wajen rattaba hannu tsakanin Nijeriya da wasu ƙasashen duniya, don samar da hanyar samar da bayanai a zamanance da kuma rattaba hannu tsakanin daulolin ƙasashen larabawa  maido da kuɗaɗen da wasu suka sace na gwamnati zuwa gida Nijeriya, inda an yi hakan ne, don ƙara inganta gangamin yaƙi da cin hanci da rashawa a Nijeriya.

Gwamnatin ta ce, ta kuma ƙirƙiri ‘PACAC’ don samarwa da shugabancin ƙasar nan alƙibla mai ɗore wa da kuma ƙarfafa jami’an gwamnati wajen yaƙi da cin hanci da rashawa.

Bugu da ƙari, gwamnatin ta bayyana cewar ta samu nasara wajen yaƙar cutar Foliyo da kuma ƙirƙiro da cibiyoyin matakan lafiya na farko a kowacce mazaɓa da ke ƙasar nan.

 

SendShareTweetShare
Previous Post

Bikin ’Yancin Kai: Har Yanzu Nijeriya ƙasa Ɗaya Ce!

Next Post

Gwamnatin Jihar Katsina Zata Gina Wasu Hanyoyi A Shiyyoyi Uku –Kwamishina

RelatedPosts

Garkuwa

An Kama Sojan Da Ke Kai Wa ‘Yan Ta’adda Kayan Sojoji A Zamfara

by Sulaiman Ibrahim
7 hours ago
0

Daga Sulaiman Ibrahim "An kama wani jami’in soja da budurwarsa...

Aikin Wutar Mambilla  A Takardu Kawai Yake, Inji Gwamnonin Arewa Maso Gabas

Aikin Wutar Mambilla A Takardu Kawai Yake, Inji Gwamnonin Arewa Maso Gabas

by Sulaiman Ibrahim
10 hours ago
0

Kungiyar gwamnonin arewa maso gabas sun nuna rashin jin dadin...

Bindiga

Gwamna Ortom Ya Yabawa Umarnin Buhari Na Hana Mallakar  AK47 Ba Bisa Ka’ida Ba

by Muhammad
11 hours ago
0

Daga Rabiu Ali Indabawa, Gwamnan Jihar Benue Samuel Ortom a ranar...

Next Post

Gwamnatin Jihar Katsina Zata Gina Wasu Hanyoyi A Shiyyoyi Uku –Kwamishina

Leave a Reply Cancel reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

Domin sanya talla ko karin bayani a tuntube wannan numbar +2348126152609.

ADVERTISEMENT
  • LABARAI
  • WASANNI
  • RAHOTANNI
  • SIYASA
  • KASUWANCI
  • ADABI
  • RA’AYINMU
  • TATTAUNAWA
  • BIDIYO
  • MAKALAR YAU
Advertise with us

© 2020 Leadership Group .

No Result
View All Result
  • LABARAI
  • WASANNI
  • RAHOTANNI
  • SIYASA
  • KASUWANCI
  • ADABI
  • RA’AYINMU
  • TATTAUNAWA
  • BIDIYO
  • MAKALAR YAU

© 2020 Leadership Group .

Go to mobile version