ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Friday, November 14, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Nijeriya Ta Koma Matsayi Na 44 A Iya Taka Leda A Duniya 

by Rabilu Sanusi Bena and Sulaiman
12 months ago
Nijeriya

Babbar tawagar kwallon kafar Nijeriya ta Super Eagles ta gamu da ragowar matsayi a fagen iya taka leda a Duniya kamar yadda alkaluman da hukumar kwallon kafa ta FIFA ta fitar a baya bayan nan wanda ta wallafa a shafinta na yanar gizo a ranar Alhamis.

 

Tawagar da Augustine Eguavoen ke jagoranta ta fadi zuwa matsayi na 44 daga matsayi na 36 da ta ke a baya,kuma sun koma matsayi na biyar a iya taka leda a Afirika daga matsayi na hudu da suke a kwanakin baya.

ADVERTISEMENT
  • Hukumar FIFA Ta Dage Gasar Cin Kofin Afirka AFCON Zuwa Shekarar 2026
  • Tattalin Arziki: Gwamna Lawal Ya Nemi Hadin Gwiwar Masu Zuba Jari Na Kasashen Afirka A Taron AFREXIM A Kenya 

Ana hasashen faduwar ba zata rasa nasaba da yadda kungiyar ta nuna rashin katabus a wasanninta na karshe na neman gurbin shiga gasar cin kofin Afrika ta 2025,inda kasar dake yammacin Afirka ta tashi kunnen doki 1-1 da Jamhuriyar Benin a Cote d’Ivoire, sannan suka sha kashi a hannun Rwanda da ci 1-2 a Uyo.

 

LABARAI MASU NASABA

Kofin Duniya: Nijeriya Za Ta Fafata Da DR Congo A Wasan Ƙarshe

Ronaldo Na Fuskantar Dakatarwar Wasanni Biyu Bayan Samun Jan Kati

Kasar Morocco ta ci gaba da zama ta daya a Afirka, inda Senegal da Aljeriya da Masar ke matsayi na biyu da na uku da na hudu,a ranar 14 ga watan Disamba ne za a fitar da jadawalin FIFA na shekarar 2024 na karshe,amma kuma babu wani fatan da Nijeriya ke da shi na hawa sama saboda babu wata wasa da zasu buga kafin wannan lokacin.

 

Kasashen Argentina da Faransa da kuma Spain ne suka ci gaba da zama a matsayi na daya zuwa na uku, inda Ingila da Brazil suka cigaba da zama a cikin kasashe biyar na farko.

ShareTweetSendShare

MASU ALAKA

Kofin Duniya: Nijeriya Za Ta Fafata Da DR Congo A Wasan Ƙarshe
Wasanni

Kofin Duniya: Nijeriya Za Ta Fafata Da DR Congo A Wasan Ƙarshe

November 14, 2025
Ronaldo Na Fuskantar Dakatarwar Wasanni Biyu Bayan Samun Jan Kati
Wasanni

Ronaldo Na Fuskantar Dakatarwar Wasanni Biyu Bayan Samun Jan Kati

November 14, 2025
Neman Gurbin Kofin Duniya: Nijeriya Ta Lallasa Gabon Da Ci 4
Manyan Labarai

Neman Gurbin Kofin Duniya: Nijeriya Ta Lallasa Gabon Da Ci 4

November 13, 2025
Next Post
Sin Za Ta Soke Ka’idar Yin Rijistar Hajojin Da Ake Fitarwa Zuwa Dakunan Adana Kayayyaki Da Kamfanoni Masu Sayar Da Kaya Ta Intanet Suka Kafa A Ketare

Sin Za Ta Soke Ka’idar Yin Rijistar Hajojin Da Ake Fitarwa Zuwa Dakunan Adana Kayayyaki Da Kamfanoni Masu Sayar Da Kaya Ta Intanet Suka Kafa A Ketare

LABARAI MASU NASABA

Sin Ta Yi Tsokaci Kan Kalaman Da Firaministar Japan Takaichi Sanae Ta Yi A Kanta

Sin Ta Yi Tsokaci Kan Kalaman Da Firaministar Japan Takaichi Sanae Ta Yi A Kanta

November 14, 2025
Tsohon Gwamnan Anambra, Willie Obiano, Ya Rasu Yana Da Shekaru 70

Tsohon Gwamnan Anambra, Willie Obiano, Ya Rasu Yana Da Shekaru 70

November 14, 2025
ADC Ta Tsara Ka’idojin Da Shugabanninta Za Su Bi Don Tunkarar Zaben 2027

ADC Ta Tsara Ka’idojin Da Shugabanninta Za Su Bi Don Tunkarar Zaben 2027

November 14, 2025

Rikicin PDP: Fiye Da Wakilai 3,000 Ne Za Su Raba Gardama A Babban Taron Jam’iyyar

November 14, 2025
Kasar Sin Ta Kara Azamar Kirkiro Da Fasahar Sadarwar 6G

Kasar Sin Ta Kara Azamar Kirkiro Da Fasahar Sadarwar 6G

November 14, 2025
GORON JUMA’A

GORON JUMA’A

November 14, 2025
Kalubalantar Ka’idar “Kasar Sin Daya Tak A Duniya” Tamkar Wasa Da Wuta Ne

Kalubalantar Ka’idar “Kasar Sin Daya Tak A Duniya” Tamkar Wasa Da Wuta Ne

November 14, 2025
Musulmin da Aka Kashe  A Zamfara, Katsina Da Sokoto Sun Ninka Na Kiristoci A Tsakiyar Najeriya: MACBAN

Musulmin da Aka Kashe  A Zamfara, Katsina Da Sokoto Sun Ninka Na Kiristoci A Tsakiyar Najeriya: MACBAN

November 14, 2025
Manzon Allah (SAW) A Matsayin Dan Gatan Allah 

Manzon Allah (SAW) A Matsayin Dan Gatan Allah 

November 14, 2025
Fansho Da Garatuti A Kano: Yau Fari Gobe Tsumma: Martani

Fansho Da Garatuti A Kano: Yau Fari Gobe Tsumma: Martani

November 14, 2025

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.