• English
  • Business News
Monday, July 7, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Tattalin Arziki: Gwamna Lawal Ya Nemi Hadin Gwiwar Masu Zuba Jari Na Kasashen Afirka A Taron AFREXIM A Kenya 

by Sulaiman
7 months ago
in Manyan Labarai
0
Tattalin Arziki: Gwamna Lawal Ya Nemi Hadin Gwiwar Masu Zuba Jari Na Kasashen Afirka A Taron AFREXIM A Kenya 
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Gwamnan Jihar Zamfara, Dauda Lawal ya jaddada ƙudirin gwamnatinsa na mayar da hankali wajen lalubo hanyoyin haɗin gwiwar ci gaba na gaskiya da adalci da za su amfani zamantakewa da tattalin arzikin jihar.

 

Gwamnan ya wakilci Ƙungiyar Gwamnonin Nijeriya, kuma ya kasance babban baƙo a taron ƙara wa juna sani na Haɗin Gwiwa na Ƙasashen Afirka karo na huɗu, wanda aka gudanar ranar Litinin a otel ɗin Swiss Grand Royal da ke garin Kisumu ta ƙasar Kenya.

  • An Kama Dillalin Safarar Makamai Dan Aljeria A Zamfara 
  • Xi Ya Bukaci A Aiwatar Da Kudurin Kwamitin Sulhun MDD Kan Batun Palastinu

Wata sanarwa da mai magana da yawun gwamnan, Sulaiman Bala Idris, ya fitar ta bayyana cewa, taron da aka fara daga ranar 25 zuwa 27 ga watan Nuwamba, Shugaban Ƙasar Kenya, Dr. Williams Ruto ne ya buɗe taron.

 

Labarai Masu Nasaba

Ranar Talata Mai Zuwa Zan Koma Zauren Majalisar Dattawa – Sanata Natasha

Ku Manta Da 2027, Tinubu Zai Ci Gaba Da Mulki Har 2031 — Fadar Shugaban Ƙasa Ga ADC

Sanarwar ta ƙara da cewa, taken taron na AfsNET shi ne “Yin amfani da AfCFTA don Samun Ɗorewar Cinikayya da Zuba Jari: Hanyar Ci Gaba ga Ƙasashen Afirka.”

 

Gwamna Lawal, wanda ke gabatar da saƙon fatan alheri a madadin Ƙungiyar Gwamnonin Nijeriya, ya ce taken taron na AfsNET na bana ya yi daidai da muradun ci gaban gwamnatocin ƙasashen Afirka. “Taron na ƙalubalantar mu da mu daidaita dabarunmu da albarkatunmu don buɗe damar kawo sauyi a harkar Cinikiyyar Ta Gaskiya d Adalci A Afirka (AfCFTA).

 

“A Nijeriya, mun fahimci muhimmiyar rawar da ƙananan gwamnatocin ƙasashe ke takawa wajen tafiyar da harkokin kasuwanci, zuba jari, da ci gaban tattalin arziki. Jihohinmu 36 cibiyoyi ne na tattalin arziki daban-daban, kowannensu yana da rawar da yake takawa ta musamman da ke ba da gudunmawa ga tattalin arzikin ƙasa.

 

“Ana iya ganin babban misalin hakan a shirin Agro-Allied Industrial Zone ta Jihar Kaduna, shirin haɗin gwiwar gwamnati da ɗaiɗaikun jama’a da aka tsara don inganta noma tare da sarrafa anganin gona don fitarwa zuwa waje.

 

“Wannan aikin yana nuna yadda masu mulki za su iya amfani da albarkatun cikin gida da kuma tsarin AfCFTA don haɓaka ƙimar kasuwanci da faɗaɗa damar kasuwanci a duk faɗin Afirka. Hakazalika, yankin AfCFTA na Lekki ya zama abin koyi na samar da masana’antu da kuma jawo hannun jari kai tsaye daga ƙetare a jihar Legas. ”

 

A wajen taron tattaunawa kan samar da mafita mai ɗorewa ga ci gaban yankin Afirka, Gwamna Lawal ya bayyana cewa, haɗin gwiwa ne zai kawo daidaito a bangaren ci gaban tattalin arziki.

 

“A matsayina na gwamna a yankin Arewa maso Yamma na Nijeriya, tare da haɗin gwiwar wasu gwamnoni shida, mun ƙirƙiro Ƙungiyar Gwamnonin Arewa maso Yamma don bayyanawa tare da daidaita manufofin da za su samar da haɗin kan yankin don samun ci gaba mai ɗorewa. Wannan ya riga ya fara samar da sakamakon mai kyau a yankin.

 

Dangane da batun tsaro, Gwamna Lawal ya jaddada cewa, in ba tare da ingantaccen tsarin muhalli ba, gwamnatoci ba za su iya samar da ayyukan jin daɗin jama’a yadda ya kamata ba kamar ilimi, kiwon lafiya, daidaiton jinsi, kawar da rashin daidaito, da samar da ayyukan dogaro da kai ga maau ƙaramin ƙarfi, waɗanda su ne muhimman abubuwan da ake buƙata don ci gaba mai ɗorewa.

 

“Tsarin mulki ya taƙaita ƙarfin Gwamna ta fuskar samar da tsaro ga al’ummar da yake mulka; duk da haka, mun yi namijin ƙoƙari wajen ganin mun tabbatar da cewa muhallinmu ya kasance cikin kwanciyar hankali ta hanyar kafa Rundunar Kare Al’umma (CPG), wadda ta daƙile matsalar rashin tsaro da ake fuskanta kafin zuwan gwamnatina.”


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

ShareTweetSendShare
Previous Post

Kasar Sin Za Ta Samar Da Ababen Hawa 100,000 Don Aikin Taksi Da Na Amfanin Kai Nan Da Shekarar 2030

Next Post

Yadda Amfani Da Karen Mutum-mutumi Da Jiragen Ruwa Da Motoci Masu Sarrafa Kansu Ya Kara Fito Da Ci Gaban Fasahar Kasar Sin

Related

Kotu Ta Umarci Majalisar Dattijan Nijeriya Da Ta Gaggauta Janye Dakatarwar Da Ta Yi Wa Natasha
Manyan Labarai

Ranar Talata Mai Zuwa Zan Koma Zauren Majalisar Dattawa – Sanata Natasha

10 hours ago
Ku Manta Da 2027, Tinubu Zai Ci Gaba Da Mulki Har 2031 — Fadar Shugaban Ƙasa Ga ADC
Manyan Labarai

Ku Manta Da 2027, Tinubu Zai Ci Gaba Da Mulki Har 2031 — Fadar Shugaban Ƙasa Ga ADC

1 day ago
Kwankwaso Ba Zai Sake Yi Mana Takarar Shugabancin Ƙasa Ba A Zaɓen 2027 Ba – NNPP
Manyan Labarai

Kwankwaso Ba Zai Sake Yi Mana Takarar Shugabancin Ƙasa Ba A Zaɓen 2027 Ba – NNPP

1 day ago
Gwamna Ademola Adeleke Ya Ƙaryata Jita-Jitar Sauya Sheƙa Daga PDP Zuwa APC
Manyan Labarai

Gwamna Ademola Adeleke Ya Ƙaryata Jita-Jitar Sauya Sheƙa Daga PDP Zuwa APC

2 days ago
‘Yansanda Sun Kama Barayi 15, Sun Kwato Motocin Sata 20 A Kano
Manyan Labarai

’Yansanda Sun Kama ’Yan Bindiga 17 Tare Da Kashe 3 A Abuja

2 days ago
Kotu Ta Umarci Majalisar Dattijan Nijeriya Da Ta Gaggauta Janye Dakatarwar Da Ta Yi Wa Natasha
Manyan Labarai

Kotu Ta Umarci Majalisar Dattijan Nijeriya Da Ta Gaggauta Janye Dakatarwar Da Ta Yi Wa Natasha

2 days ago
Next Post
Yadda Amfani Da Karen Mutum-mutumi Da Jiragen Ruwa Da Motoci Masu Sarrafa Kansu Ya Kara Fito Da Ci Gaban Fasahar Kasar Sin

Yadda Amfani Da Karen Mutum-mutumi Da Jiragen Ruwa Da Motoci Masu Sarrafa Kansu Ya Kara Fito Da Ci Gaban Fasahar Kasar Sin

LABARAI MASU NASABA

Ƙwallon Mata: Nijeriya Ta Lallasa Tunisiya Da Ci 3-0 A Moroko

Ƙwallon Mata: Nijeriya Ta Lallasa Tunisiya Da Ci 3-0 A Moroko

July 6, 2025
Sojoji Sun Kashe ‘Yan Bindiga Tare Da Kwato Makamai A Jihar Filato

‘Yan Boko Haram Sun Kashe Mutane 9, Tare Da Jikkata Wasu Mutum 4 A Borno

July 6, 2025
Mataimakin Firaministan Sin Ya Jaddada Muhimmancin Sabbin Fasahohin Kimiyya A Fannin Aikin Gona Da Kiwon Lafiya

Mataimakin Firaministan Sin Ya Jaddada Muhimmancin Sabbin Fasahohin Kimiyya A Fannin Aikin Gona Da Kiwon Lafiya

July 6, 2025
Sanata Dickson Ya Buƙaci ‘Yan Nijeriya Da Su Yi Yaƙi Da Matsalar Sayen Ƙuri’a

Sanata Dickson Ya Buƙaci ‘Yan Nijeriya Da Su Yi Yaƙi Da Matsalar Sayen Ƙuri’a

July 6, 2025
Xi Ya Ba Da Amsar Wasikar Matasan Amurka ’Yan Wasan Kwallon Pickle Bisa Ziyartar Sin

Xi Ya Ba Da Amsar Wasikar Matasan Amurka ’Yan Wasan Kwallon Pickle Bisa Ziyartar Sin

July 6, 2025
Yankin Kudu-Maso-Kudu Zai Cimma Matsaya Ɗaya Kan Gyaran Kundin Tsarin Mulki – Sanata Dickson

Yankin Kudu-Maso-Kudu Zai Cimma Matsaya Ɗaya Kan Gyaran Kundin Tsarin Mulki – Sanata Dickson

July 6, 2025
Sin Za Ta Fadada Hadin Gwiwa Da Brazil A Fannin Tattalin Arzikin Fasahar Zamani Da Sha’anin Jiragen Sama

Sin Za Ta Fadada Hadin Gwiwa Da Brazil A Fannin Tattalin Arzikin Fasahar Zamani Da Sha’anin Jiragen Sama

July 6, 2025
Hadimin Gwamnan Yobe Ya Fice Daga APC Ya Koma Jam’iyyar ADC

Hadimin Gwamnan Yobe Ya Fice Daga APC Ya Koma Jam’iyyar ADC

July 6, 2025
Masanin Kenya: Kasashe Masu Tasowa Suna Bukatar Kasar Sin

Masanin Kenya: Kasashe Masu Tasowa Suna Bukatar Kasar Sin

July 6, 2025
Ba Ni Da Niyyar Barin APC Zuwa Wata Jam’iyyar — Gwamna Zulum

Ba Ni Da Niyyar Barin APC Zuwa Wata Jam’iyyar — Gwamna Zulum

July 6, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.