ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Thursday, June 25, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Tattalin Arziki: Gwamna Lawal Ya Nemi Hadin Gwiwar Masu Zuba Jari Na Kasashen Afirka A Taron AFREXIM A Kenya 

by Sulaiman
2 years ago
Lawal

Gwamnan Jihar Zamfara, Dauda Lawal ya jaddada ƙudirin gwamnatinsa na mayar da hankali wajen lalubo hanyoyin haɗin gwiwar ci gaba na gaskiya da adalci da za su amfani zamantakewa da tattalin arzikin jihar.

 

Gwamnan ya wakilci Ƙungiyar Gwamnonin Nijeriya, kuma ya kasance babban baƙo a taron ƙara wa juna sani na Haɗin Gwiwa na Ƙasashen Afirka karo na huɗu, wanda aka gudanar ranar Litinin a otel ɗin Swiss Grand Royal da ke garin Kisumu ta ƙasar Kenya.

ADVERTISEMENT
  • An Kama Dillalin Safarar Makamai Dan Aljeria A Zamfara 
  • Xi Ya Bukaci A Aiwatar Da Kudurin Kwamitin Sulhun MDD Kan Batun Palastinu

Wata sanarwa da mai magana da yawun gwamnan, Sulaiman Bala Idris, ya fitar ta bayyana cewa, taron da aka fara daga ranar 25 zuwa 27 ga watan Nuwamba, Shugaban Ƙasar Kenya, Dr. Williams Ruto ne ya buɗe taron.

 

LABARAI MASU NASABA

Zargin Ɓata Suna: Kwankwaso Ya Yi Barazanar Neman Diyyar Naira Biliyan 10 Kan Wani Malamin Coci

Atiku Ya Soki Tsare El-Rufai, Ya Ce Sharuɗan Belinsa Sun Yi Tsauri

Sanarwar ta ƙara da cewa, taken taron na AfsNET shi ne “Yin amfani da AfCFTA don Samun Ɗorewar Cinikayya da Zuba Jari: Hanyar Ci Gaba ga Ƙasashen Afirka.”

 

Gwamna Lawal, wanda ke gabatar da saƙon fatan alheri a madadin Ƙungiyar Gwamnonin Nijeriya, ya ce taken taron na AfsNET na bana ya yi daidai da muradun ci gaban gwamnatocin ƙasashen Afirka. “Taron na ƙalubalantar mu da mu daidaita dabarunmu da albarkatunmu don buɗe damar kawo sauyi a harkar Cinikiyyar Ta Gaskiya d Adalci A Afirka (AfCFTA).

 

“A Nijeriya, mun fahimci muhimmiyar rawar da ƙananan gwamnatocin ƙasashe ke takawa wajen tafiyar da harkokin kasuwanci, zuba jari, da ci gaban tattalin arziki. Jihohinmu 36 cibiyoyi ne na tattalin arziki daban-daban, kowannensu yana da rawar da yake takawa ta musamman da ke ba da gudunmawa ga tattalin arzikin ƙasa.

 

“Ana iya ganin babban misalin hakan a shirin Agro-Allied Industrial Zone ta Jihar Kaduna, shirin haɗin gwiwar gwamnati da ɗaiɗaikun jama’a da aka tsara don inganta noma tare da sarrafa anganin gona don fitarwa zuwa waje.

 

“Wannan aikin yana nuna yadda masu mulki za su iya amfani da albarkatun cikin gida da kuma tsarin AfCFTA don haɓaka ƙimar kasuwanci da faɗaɗa damar kasuwanci a duk faɗin Afirka. Hakazalika, yankin AfCFTA na Lekki ya zama abin koyi na samar da masana’antu da kuma jawo hannun jari kai tsaye daga ƙetare a jihar Legas. ”

 

A wajen taron tattaunawa kan samar da mafita mai ɗorewa ga ci gaban yankin Afirka, Gwamna Lawal ya bayyana cewa, haɗin gwiwa ne zai kawo daidaito a bangaren ci gaban tattalin arziki.

 

“A matsayina na gwamna a yankin Arewa maso Yamma na Nijeriya, tare da haɗin gwiwar wasu gwamnoni shida, mun ƙirƙiro Ƙungiyar Gwamnonin Arewa maso Yamma don bayyanawa tare da daidaita manufofin da za su samar da haɗin kan yankin don samun ci gaba mai ɗorewa. Wannan ya riga ya fara samar da sakamakon mai kyau a yankin.

 

Dangane da batun tsaro, Gwamna Lawal ya jaddada cewa, in ba tare da ingantaccen tsarin muhalli ba, gwamnatoci ba za su iya samar da ayyukan jin daɗin jama’a yadda ya kamata ba kamar ilimi, kiwon lafiya, daidaiton jinsi, kawar da rashin daidaito, da samar da ayyukan dogaro da kai ga maau ƙaramin ƙarfi, waɗanda su ne muhimman abubuwan da ake buƙata don ci gaba mai ɗorewa.

 

“Tsarin mulki ya taƙaita ƙarfin Gwamna ta fuskar samar da tsaro ga al’ummar da yake mulka; duk da haka, mun yi namijin ƙoƙari wajen ganin mun tabbatar da cewa muhallinmu ya kasance cikin kwanciyar hankali ta hanyar kafa Rundunar Kare Al’umma (CPG), wadda ta daƙile matsalar rashin tsaro da ake fuskanta kafin zuwan gwamnatina.”

Lawal
Sulaiman
+ postsBio
  • Sulaiman
    Dokar Sin Ta Gurfanar Da Masu Rajin Ballewar Kabilun Kasar Da Ke Kasashen Waje Ta Dace
  • Sulaiman
    ’Yan Kasuwa Na Kasashen Waje Sun Yaba Wa Yanayin Kasuwanci Na Sin
  • Sulaiman
    Yadda Uba Sani Ya Farfaɗo Da Asibitin Da Aka Yi Watsi Da Shi Tsawon Shekaru 40 – Hakimin Makarfi
  • Sulaiman
    Dandalin DAVOS Na Bana: Fage Ne Da “Kirkire-Kirkiren Sin” Ya Sadu Da “Kyakkyawan Fatan Afirka”

MASU ALAKA

Yadda Na Sayar Da Kadarori Na Don Ɗaukar Nauyin Ɗalibai A Ƙasashen Waje – Kwankwaso
Manyan Labarai

Zargin Ɓata Suna: Kwankwaso Ya Yi Barazanar Neman Diyyar Naira Biliyan 10 Kan Wani Malamin Coci

June 24, 2026
Tinubu Ya Gaza Wajen Magance Matsalar Tsaro A Nijeriya — Atiku
Manyan Labarai

Atiku Ya Soki Tsare El-Rufai, Ya Ce Sharuɗan Belinsa Sun Yi Tsauri

June 24, 2026
‘Yansanda Sun Kama Ɗan Bindiga Da Kuɗin Fansa Naira Miliyan 5 A Delta
Manyan Labarai

’Yansanda Sun Kama Wani Mutum da Harsasai 174 A Nasarawa

June 24, 2026
Next Post
Yadda Amfani Da Karen Mutum-mutumi Da Jiragen Ruwa Da Motoci Masu Sarrafa Kansu Ya Kara Fito Da Ci Gaban Fasahar Kasar Sin

Yadda Amfani Da Karen Mutum-mutumi Da Jiragen Ruwa Da Motoci Masu Sarrafa Kansu Ya Kara Fito Da Ci Gaban Fasahar Kasar Sin

LABARAI MASU NASABA

Dokar Sin Ta Gurfanar Da Masu Rajin Ballewar Kabilun Kasar Da Ke Kasashen Waje Ta Dace

Dokar Sin Ta Gurfanar Da Masu Rajin Ballewar Kabilun Kasar Da Ke Kasashen Waje Ta Dace

June 24, 2026
’Yan Kasuwa Na Kasashen Waje Sun Yaba Wa Yanayin Kasuwanci Na Sin

’Yan Kasuwa Na Kasashen Waje Sun Yaba Wa Yanayin Kasuwanci Na Sin

June 24, 2026
Yadda Uba Sani Ya Farfaɗo Da Asibitin Da Aka Yi Watsi Da Shi Tsawon Shekaru 40 – Hakimin Makarfi

Yadda Uba Sani Ya Farfaɗo Da Asibitin Da Aka Yi Watsi Da Shi Tsawon Shekaru 40 – Hakimin Makarfi

June 24, 2026
Dandalin DAVOS Na Bana: Fage Ne Da “Kirkire-Kirkiren Sin” Ya Sadu Da “Kyakkyawan Fatan Afirka”

Dandalin DAVOS Na Bana: Fage Ne Da “Kirkire-Kirkiren Sin” Ya Sadu Da “Kyakkyawan Fatan Afirka”

June 24, 2026
Binciken CGTN: Amfanarwa A Aikace Shi Ne Nagartaccen Ma’aunin Tantance Ainihin Kimar Sabbin Fasahohi

Binciken CGTN: Amfanarwa A Aikace Shi Ne Nagartaccen Ma’aunin Tantance Ainihin Kimar Sabbin Fasahohi

June 24, 2026
Kasar Sin Na Kara Zama Babban Ginshikin Ci Gaban Tattalin Arzikin Duniya Na Gaba

Kasar Sin Na Kara Zama Babban Ginshikin Ci Gaban Tattalin Arzikin Duniya Na Gaba

June 24, 2026
Tsaro: Dasuki Ya Bukaci Tinubu Ya Gyara Alaka Da Nijar Domin Kare Iyakokin Arewa-Maso-Yamma

Tsaro: Dasuki Ya Bukaci Tinubu Ya Gyara Alaka Da Nijar Domin Kare Iyakokin Arewa-Maso-Yamma

June 24, 2026
Sabbin Ministoci

Kafa ‘Yansandan Jihohi: Majalisa Ta Amince Da Tsarin ‘Yar Tinƙe Wajen Kaɗa Ƙuri’a 

June 24, 2026
Sin Ta Gabatar Da Tsarin Karfafa Kwarin Gwiwar Kamfanoni Masu Jarin Waje

Sin Ta Gabatar Da Tsarin Karfafa Kwarin Gwiwar Kamfanoni Masu Jarin Waje

June 24, 2026
Shugaban Kasar Burundi: Dangantakar Afirka Da Sin Misali Ce Ta Hadin Gwiwar Kasashe Masu Tasowa

Shugaban Kasar Burundi: Dangantakar Afirka Da Sin Misali Ce Ta Hadin Gwiwar Kasashe Masu Tasowa

June 24, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.