• Leadership Hausa
Friday, December 8, 2023
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Sana’a Sa’a
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Sana’a Sa’a
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

NIS Na Taka Muhimmiyar Rawa Wajen Bunkasa Zuba Jari A Nijeriya –CI James

by Khalid Idris Doya
7 months ago
in Labarai
0
NIS Na Taka Muhimmiyar Rawa Wajen Bunkasa Zuba Jari A Nijeriya –CI James
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Kwanturolan hukumar kula da shige da fice ta kasa (Immigration) a jihar Ribas, CI James Sunday, ya misalta ayyukan hukumar a matsayin wanda ke taka muhimmiyar rawa wajen bunkasa sashen zuba jari a Nijeriya.

Sunday wanda ke magana da ‘yan jarida kan rawar da hukumar ke takawa wajen kyautata tattalin arzikin kasa, ya ce, a matsayinsu na masu kula da shige da fice da iyakokin kasa, aikinsu na da alaka kai tsaye da tattalin arziki, siyasa, tsaro, ilimi, addini da kyautata kiwon lafiya a kasar nan.

  • Hukumar Raba Daidai Ta Nijeriya Ta Bukaci A Kara Wa Tinubu Da Gwamoni Albashi
  • Sauyin Gwamnati Zai Yi Sanadin Rasa Guraben Aiki 2,585 A Nijeriya

Sannan, da tsarin bin dokokin shigowa ko fita, kula da wadanda za su zo domin zuba jari da masu kawo ziyara cikin kasa.

A kan hakan ne ya misalta jajircewa da kokarin da suke yi a matsayin hanyar da ke kyautata sashin zuba jari a cikin Nijeriya, yana mai cewa jami’ansu sun kware wajen gudanar da aikinsu da ake alfahari da su.

James ya bada misalin yadda suka taka rawa wajen kula da iyakokin kasa lokacin da annobar Korona ya barke a kwanakin baya, ta yadda suka kula da masu shigowa domin tabbatar da wadanda suke dauke da cutar ba su shigo sun yada wa al’ummar Nijeriya ba.

Labarai Masu Nasaba

Hukumar Kwastam A Kano Ta Samu Kudin Shiga Naira Biliyan 6.9 A Nuwamba

Kyautata Rayuwar Matasa Ne Fatanmu – Kwamoti La’ori 

Ya kuma kara da cewa, hukumarsu ta taimaka wa tawagar sojojin wajen yaki da ‘yan ta’adda a shiyyar Arewa Maso Gabas ta fuskacin kula da wadanda aka yi garkuwa da su, agajin gaggawa ga ‘yan Nijeriya, ceto da aikin tallafi ga wadanda lamarin ya shafa da taimaka wa ‘yan gudun hijira a jihohin da suke Arewa Maso Gabas.

Ta fannin zuba jari kuwa, ya ce, hukumarsu ce ke bada izinin shigowa kasa ga masu son zuba jari, da masu kawo ziyara da tabbatar da tsawon lokacin zamansu ko wa’adi wanda ta hakan ana samun bunkasar tattalin arziki sosai.

Baya ga masu zuba jari da masu kawo ziyarar, ya ce, hukumarsu kuma tana kula da masu zuwa Nijeriya a bangaren kwararru wadanda ake kira domin su yi gyara ko aikin kwaskwarima na wasu muhimman abubuwa a cikin kasar nan.

“Hukumar NIS a karkashin jagorancin Kwanturola Janar, Isa Jere Idris, ta narka jami’ai sosai da suke taimaka wa tawagar jami’an tsaro, wadanda suke iyakokin kasa da filayen jiragen kasa da suke kasar nan, wuraren kula da iyakoki, wuraren sintirin ababen hawa a kokarinmu na tabbatar da dakile masu shigowa ba bisa ka’ida ba da tabbatar da tsaron kasa.”

Ya kara da cewa, sannan, an ware kwararrun jami’ai wadanda suke kula da jihohi a matsayin kwanturololin jihohi domin tabbatar ingancin aiki da tsaron kasa da kula da masu shige da fice da tabbatar da jama’a na bin cikakken ka’idar samun izinin zama ko shigowa Nijeriya a kowani lokaci.

A cewar James, suna kokarin tabbatar da jama’a na samun sauki da ingancin samun iznin shigowa ko zama cikin Nijeriya a kan lokaci, don haka ne ya tabbatar da cewa akwai kyakkawar tsari da suke da shi wajen inganta aiki a kowane lokaci.

Tags: 'Yan NijeriyaArewa Maso GabasJereNISZuba Jari
ShareTweetSendShare
Previous Post

Hukumar Raba Daidai Ta Nijeriya Ta Bukaci A Kara Wa Tinubu Da Gwamoni Albashi

Next Post

GORON JUMA’A

Related

kwastam
Labarai

Hukumar Kwastam A Kano Ta Samu Kudin Shiga Naira Biliyan 6.9 A Nuwamba

2 hours ago
Kyautata Rayuwar Matasa Ne Fatanmu – Kwamoti La’ori 
Labarai

Kyautata Rayuwar Matasa Ne Fatanmu – Kwamoti La’ori 

5 hours ago
NAHCON
Labarai

Hajjin 2024: NAHCON Za Ta Sabunta Ka’idojin Ciyar Da Alhazai Da Masaukansu

6 hours ago
kaduna
Manyan Labarai

Matsalar Da Ta Haddasa Harin Bom Na Kaduna

7 hours ago
Ministan Yaɗa Labarai Ya Kafa Kwamitin Tsara Cusa Ɗa’a Da Kishin Ƙasa
Labarai

Ministan Yaɗa Labarai Ya Kafa Kwamitin Tsara Cusa Ɗa’a Da Kishin Ƙasa

15 hours ago
Shettima Ya Ziyarci Wadanda Sojoji Suka Jefawa Bam A Kaduna
Manyan Labarai

Shettima Ya Ziyarci Wadanda Sojoji Suka Jefawa Bam A Kaduna

16 hours ago
Next Post
GORON JUMA’A

GORON JUMA’A

LABARAI MASU NASABA

Fu Qiaomei

Fu Qiaomei: Matashiyar Masaniyar Kimiyyar Kasar Sin Da Ta Sake Rubuta Tarihin Dan Adam Na Da

December 8, 2023
kwastam

Hukumar Kwastam A Kano Ta Samu Kudin Shiga Naira Biliyan 6.9 A Nuwamba

December 8, 2023
Al’ajabi: Saurayi Ya Yi Wa Zakara Fyade A Adamawa

Al’ajabi: Saurayi Ya Yi Wa Zakara Fyade A Adamawa

December 8, 2023
tallafi

Gwamnatin Tarayya Za Ta Fara Raba Tallafi Ga Masu Kananan Masana’antu

December 8, 2023
Akpabio

‘Yan Nijeriya Ba Sa Amanna Da Jam’iyyun Siyasa – Akpabio

December 8, 2023
Manzon Allah

Daga Cikin Mutane Aka Aiko Manzon Allah Amma Ba Mutum Ne Kamar Kowa Ba (SAW)

December 8, 2023
Kyautata Rayuwar Matasa Ne Fatanmu – Kwamoti La’ori 

Kyautata Rayuwar Matasa Ne Fatanmu – Kwamoti La’ori 

December 8, 2023
Ba Za A Cimma Wannan Yarjejeniya Ba Tare Da Taimakon Sin Ba

Ba Za A Cimma Wannan Yarjejeniya Ba Tare Da Taimakon Sin Ba

December 8, 2023
NAHCON

Hajjin 2024: NAHCON Za Ta Sabunta Ka’idojin Ciyar Da Alhazai Da Masaukansu

December 8, 2023
kaduna

Matsalar Da Ta Haddasa Harin Bom Na Kaduna

December 8, 2023
Advertise with us

© 2022 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2022 Leadership Media Group - All Right Reserved.