• English
  • Business News
Friday, July 11, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

NIS Na Taka Muhimmiyar Rawa Wajen Bunkasa Zuba Jari A Nijeriya –CI James

by Khalid Idris Doya
2 years ago
in Labarai
0
NIS Na Taka Muhimmiyar Rawa Wajen Bunkasa Zuba Jari A Nijeriya –CI James
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Kwanturolan hukumar kula da shige da fice ta kasa (Immigration) a jihar Ribas, CI James Sunday, ya misalta ayyukan hukumar a matsayin wanda ke taka muhimmiyar rawa wajen bunkasa sashen zuba jari a Nijeriya.

Sunday wanda ke magana da ‘yan jarida kan rawar da hukumar ke takawa wajen kyautata tattalin arzikin kasa, ya ce, a matsayinsu na masu kula da shige da fice da iyakokin kasa, aikinsu na da alaka kai tsaye da tattalin arziki, siyasa, tsaro, ilimi, addini da kyautata kiwon lafiya a kasar nan.

  • Hukumar Raba Daidai Ta Nijeriya Ta Bukaci A Kara Wa Tinubu Da Gwamoni Albashi
  • Sauyin Gwamnati Zai Yi Sanadin Rasa Guraben Aiki 2,585 A Nijeriya

Sannan, da tsarin bin dokokin shigowa ko fita, kula da wadanda za su zo domin zuba jari da masu kawo ziyara cikin kasa.

A kan hakan ne ya misalta jajircewa da kokarin da suke yi a matsayin hanyar da ke kyautata sashin zuba jari a cikin Nijeriya, yana mai cewa jami’ansu sun kware wajen gudanar da aikinsu da ake alfahari da su.

James ya bada misalin yadda suka taka rawa wajen kula da iyakokin kasa lokacin da annobar Korona ya barke a kwanakin baya, ta yadda suka kula da masu shigowa domin tabbatar da wadanda suke dauke da cutar ba su shigo sun yada wa al’ummar Nijeriya ba.

Labarai Masu Nasaba

Akwai Bukatar Hada Kai Da Aiki Tare Tsakanin Hukumomin Tsaro

Ƴan Bindiga Sun Yi Wa Jami’an NSCDC Ƙwantan Ɓauna A Binuwe

Ya kuma kara da cewa, hukumarsu ta taimaka wa tawagar sojojin wajen yaki da ‘yan ta’adda a shiyyar Arewa Maso Gabas ta fuskacin kula da wadanda aka yi garkuwa da su, agajin gaggawa ga ‘yan Nijeriya, ceto da aikin tallafi ga wadanda lamarin ya shafa da taimaka wa ‘yan gudun hijira a jihohin da suke Arewa Maso Gabas.

Ta fannin zuba jari kuwa, ya ce, hukumarsu ce ke bada izinin shigowa kasa ga masu son zuba jari, da masu kawo ziyara da tabbatar da tsawon lokacin zamansu ko wa’adi wanda ta hakan ana samun bunkasar tattalin arziki sosai.

Baya ga masu zuba jari da masu kawo ziyarar, ya ce, hukumarsu kuma tana kula da masu zuwa Nijeriya a bangaren kwararru wadanda ake kira domin su yi gyara ko aikin kwaskwarima na wasu muhimman abubuwa a cikin kasar nan.

“Hukumar NIS a karkashin jagorancin Kwanturola Janar, Isa Jere Idris, ta narka jami’ai sosai da suke taimaka wa tawagar jami’an tsaro, wadanda suke iyakokin kasa da filayen jiragen kasa da suke kasar nan, wuraren kula da iyakoki, wuraren sintirin ababen hawa a kokarinmu na tabbatar da dakile masu shigowa ba bisa ka’ida ba da tabbatar da tsaron kasa.”

Ya kara da cewa, sannan, an ware kwararrun jami’ai wadanda suke kula da jihohi a matsayin kwanturololin jihohi domin tabbatar ingancin aiki da tsaron kasa da kula da masu shige da fice da tabbatar da jama’a na bin cikakken ka’idar samun izinin zama ko shigowa Nijeriya a kowani lokaci.

A cewar James, suna kokarin tabbatar da jama’a na samun sauki da ingancin samun iznin shigowa ko zama cikin Nijeriya a kan lokaci, don haka ne ya tabbatar da cewa akwai kyakkawar tsari da suke da shi wajen inganta aiki a kowane lokaci.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: 'Yan NijeriyaArewa Maso GabasJereNISZuba Jari
ShareTweetSendShare
Previous Post

Hukumar Raba Daidai Ta Nijeriya Ta Bukaci A Kara Wa Tinubu Da Gwamoni Albashi

Next Post

GORON JUMA’A

Related

Yunkurin Magance Matsalar Tsaro Da Rigingimu A Arewa…
Manyan Labarai

Akwai Bukatar Hada Kai Da Aiki Tare Tsakanin Hukumomin Tsaro

41 minutes ago
Ƴan Bindiga Sun Yi Wa Jami’an NSCDC Ƙwantan Ɓauna A Binuwe
Manyan Labarai

Ƴan Bindiga Sun Yi Wa Jami’an NSCDC Ƙwantan Ɓauna A Binuwe

11 hours ago
An Kama Magungunan Jabu Na Fiye Da Naira Biliyan Ɗaya A Kano
Labarai

An Kama Magungunan Jabu Na Fiye Da Naira Biliyan Ɗaya A Kano

12 hours ago
Majalisar Ta Kwace Shugabacin Kwamitin Da Natasha Ke Jagoranta
Labarai

Majalisar Ta Kwace Shugabacin Kwamitin Da Natasha Ke Jagoranta

14 hours ago
Shiri Na Shekaru Biyar Biyar: Sirrin Tabbatar Da Ci Gaban Kasar Sin
Ra'ayi Riga

Shiri Na Shekaru Biyar Biyar: Sirrin Tabbatar Da Ci Gaban Kasar Sin

14 hours ago
EFCC Ta Gargaɗi Ƴan Nijeriya Kan Ɓullar Sabbin Hanyoyin Damfarar Kuɗi
Labarai

EFCC Ta Gargaɗi Ƴan Nijeriya Kan Ɓullar Sabbin Hanyoyin Damfarar Kuɗi

15 hours ago
Next Post
GORON JUMA’A

GORON JUMA’A

LABARAI MASU NASABA

Yunkurin Magance Matsalar Tsaro Da Rigingimu A Arewa…

Akwai Bukatar Hada Kai Da Aiki Tare Tsakanin Hukumomin Tsaro

July 11, 2025
Ƙwallon Mata: Nijeriya Ta Kai Matakin Kwata Fainal Bayan Doke Botswana

Ƙwallon Mata: Nijeriya Ta Kai Matakin Kwata Fainal Bayan Doke Botswana

July 10, 2025
Mataimakin Babban Magatakardan MDD: Sin Aminiya Ce Da Afirka Za Ta Iya Dogaro Da Ita

Mataimakin Babban Magatakardan MDD: Sin Aminiya Ce Da Afirka Za Ta Iya Dogaro Da Ita

July 10, 2025
Li Qiang Ya Gana Da Manyan Jami’an Masar Da ALLi Qiang Ya Gana Da Manyan Jami’an Masar Da AL

Li Qiang Ya Gana Da Manyan Jami’an Masar Da ALLi Qiang Ya Gana Da Manyan Jami’an Masar Da AL

July 10, 2025
Ƴan Bindiga Sun Yi Wa Jami’an NSCDC Ƙwantan Ɓauna A Binuwe

Ƴan Bindiga Sun Yi Wa Jami’an NSCDC Ƙwantan Ɓauna A Binuwe

July 10, 2025
Yadda JKS Ta Jure Tsawon Tarihin Gwagwarmaya Da Cimma Nasarori

Yadda JKS Ta Jure Tsawon Tarihin Gwagwarmaya Da Cimma Nasarori

July 10, 2025
An Kama Magungunan Jabu Na Fiye Da Naira Biliyan Ɗaya A Kano

An Kama Magungunan Jabu Na Fiye Da Naira Biliyan Ɗaya A Kano

July 10, 2025
Xi Jinping Ya Aike Da Sakon Taya Murnar Bude Taron Ministocin Kasa Da Kasa Na Tattaunawa Kan Wayewar Kan Bil Adam

Xi Jinping Ya Aike Da Sakon Taya Murnar Bude Taron Ministocin Kasa Da Kasa Na Tattaunawa Kan Wayewar Kan Bil Adam

July 10, 2025
Majalisar Ta Kwace Shugabacin Kwamitin Da Natasha Ke Jagoranta

Majalisar Ta Kwace Shugabacin Kwamitin Da Natasha Ke Jagoranta

July 10, 2025
An Bude Taron Ministoci Kan Wayewar Kai A Birnin Beijing

An Bude Taron Ministoci Kan Wayewar Kai A Birnin Beijing

July 10, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.