ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Monday, June 29, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

NIS Na Taka Muhimmiyar Rawa Wajen Bunkasa Zuba Jari A Nijeriya –CI James

by Khalid Idris Doya
3 years ago
NIS

Kwanturolan hukumar kula da shige da fice ta kasa (Immigration) a jihar Ribas, CI James Sunday, ya misalta ayyukan hukumar a matsayin wanda ke taka muhimmiyar rawa wajen bunkasa sashen zuba jari a Nijeriya.

Sunday wanda ke magana da ‘yan jarida kan rawar da hukumar ke takawa wajen kyautata tattalin arzikin kasa, ya ce, a matsayinsu na masu kula da shige da fice da iyakokin kasa, aikinsu na da alaka kai tsaye da tattalin arziki, siyasa, tsaro, ilimi, addini da kyautata kiwon lafiya a kasar nan.

  • Hukumar Raba Daidai Ta Nijeriya Ta Bukaci A Kara Wa Tinubu Da Gwamoni Albashi
  • Sauyin Gwamnati Zai Yi Sanadin Rasa Guraben Aiki 2,585 A Nijeriya

Sannan, da tsarin bin dokokin shigowa ko fita, kula da wadanda za su zo domin zuba jari da masu kawo ziyara cikin kasa.

ADVERTISEMENT

A kan hakan ne ya misalta jajircewa da kokarin da suke yi a matsayin hanyar da ke kyautata sashin zuba jari a cikin Nijeriya, yana mai cewa jami’ansu sun kware wajen gudanar da aikinsu da ake alfahari da su.

James ya bada misalin yadda suka taka rawa wajen kula da iyakokin kasa lokacin da annobar Korona ya barke a kwanakin baya, ta yadda suka kula da masu shigowa domin tabbatar da wadanda suke dauke da cutar ba su shigo sun yada wa al’ummar Nijeriya ba.

LABARAI MASU NASABA

Shigo Da Fetur Daga Waje Ya Sauka Zuwa N983.92, Ya Fi Na Matatar Dangote Arha

An Lakaɗawa Wata Malamar Makaranta Duka Har Lahira A Lokoja

Ya kuma kara da cewa, hukumarsu ta taimaka wa tawagar sojojin wajen yaki da ‘yan ta’adda a shiyyar Arewa Maso Gabas ta fuskacin kula da wadanda aka yi garkuwa da su, agajin gaggawa ga ‘yan Nijeriya, ceto da aikin tallafi ga wadanda lamarin ya shafa da taimaka wa ‘yan gudun hijira a jihohin da suke Arewa Maso Gabas.

Ta fannin zuba jari kuwa, ya ce, hukumarsu ce ke bada izinin shigowa kasa ga masu son zuba jari, da masu kawo ziyara da tabbatar da tsawon lokacin zamansu ko wa’adi wanda ta hakan ana samun bunkasar tattalin arziki sosai.

Baya ga masu zuba jari da masu kawo ziyarar, ya ce, hukumarsu kuma tana kula da masu zuwa Nijeriya a bangaren kwararru wadanda ake kira domin su yi gyara ko aikin kwaskwarima na wasu muhimman abubuwa a cikin kasar nan.

“Hukumar NIS a karkashin jagorancin Kwanturola Janar, Isa Jere Idris, ta narka jami’ai sosai da suke taimaka wa tawagar jami’an tsaro, wadanda suke iyakokin kasa da filayen jiragen kasa da suke kasar nan, wuraren kula da iyakoki, wuraren sintirin ababen hawa a kokarinmu na tabbatar da dakile masu shigowa ba bisa ka’ida ba da tabbatar da tsaron kasa.”

Ya kara da cewa, sannan, an ware kwararrun jami’ai wadanda suke kula da jihohi a matsayin kwanturololin jihohi domin tabbatar ingancin aiki da tsaron kasa da kula da masu shige da fice da tabbatar da jama’a na bin cikakken ka’idar samun izinin zama ko shigowa Nijeriya a kowani lokaci.

A cewar James, suna kokarin tabbatar da jama’a na samun sauki da ingancin samun iznin shigowa ko zama cikin Nijeriya a kan lokaci, don haka ne ya tabbatar da cewa akwai kyakkawar tsari da suke da shi wajen inganta aiki a kowane lokaci.

NIS
Khalid Idris Doya
+ postsBio
  • Khalid Idris Doya
    https://hausa.leadership.ng/author/khalid-idris-doya/
    Ɗan Majalisar Dokokin Bauchi, Hon. Wanzam, Ya Rasu
  • Khalid Idris Doya
    https://hausa.leadership.ng/author/khalid-idris-doya/
    Tsohon Mataimakin Gwamnan Bauchi, Audu Sule Katagum Ya Rasu
  • Khalid Idris Doya
    https://hausa.leadership.ng/author/khalid-idris-doya/
    Kotu Ta Umarci DSS Ta Mutunta Umarninta Kan Shari’ar Filin Firo Na Bauchi
  • Khalid Idris Doya
    https://hausa.leadership.ng/author/khalid-idris-doya/
    Ana Zargin Jami’in Kwastam Da Kashe Kansa A Bauchi Saboda Damuwa

MASU ALAKA

Shigo Da Fetur Daga Waje Ya Sauka Zuwa N983.92, Ya Fi Na Matatar Dangote Arha
Manyan Labarai

Shigo Da Fetur Daga Waje Ya Sauka Zuwa N983.92, Ya Fi Na Matatar Dangote Arha

June 28, 2026
An Lakaɗawa Wata Malamar Makaranta Duka Har Lahira A Lokoja
Manyan Labarai

An Lakaɗawa Wata Malamar Makaranta Duka Har Lahira A Lokoja

June 28, 2026
Ƴan Bindiga Sun Harbe Limami Da Wasu Mutane 3 A Sokoto
Labarai

Ƴan Bindiga Sun Harbe Limami Da Wasu Mutane 3 A Sokoto

June 28, 2026
Next Post
GORON JUMA’A

GORON JUMA’A

LABARAI MASU NASABA

Ana Taron Ministocin Kula Da Yawon Bude Ido Na Kasashen APEC A Macao

Ana Taron Ministocin Kula Da Yawon Bude Ido Na Kasashen APEC A Macao

June 28, 2026
Shigo Da Fetur Daga Waje Ya Sauka Zuwa N983.92, Ya Fi Na Matatar Dangote Arha

Shigo Da Fetur Daga Waje Ya Sauka Zuwa N983.92, Ya Fi Na Matatar Dangote Arha

June 28, 2026
An Lakaɗawa Wata Malamar Makaranta Duka Har Lahira A Lokoja

An Lakaɗawa Wata Malamar Makaranta Duka Har Lahira A Lokoja

June 28, 2026
Mataimakin Firaministan Sin Ya Yi Kira Da A Gaggauta Zamanantar Da Tsarin Ayyukan Masana’antu

Mataimakin Firaministan Sin Ya Yi Kira Da A Gaggauta Zamanantar Da Tsarin Ayyukan Masana’antu

June 28, 2026
Kotu Ta Fara Sauraron Shari’ar Da Ke Ƙalubalantar Takarar Pantami A PDP

Kotu Ta Fara Sauraron Shari’ar Da Ke Ƙalubalantar Takarar Pantami A PDP

June 28, 2026
Ƴan Bindiga Sun Harbe Limami Da Wasu Mutane 3 A Sokoto

Ƴan Bindiga Sun Harbe Limami Da Wasu Mutane 3 A Sokoto

June 28, 2026
Ƴansanda Sun Kama Mutum 10 Kan Kisan Shugaban MACBAN Na Jihar Binuwe

Ƴansanda Sun Kama Mutum 10 Kan Kisan Shugaban MACBAN Na Jihar Binuwe

June 28, 2026
Mun Kaɗu Matuƙa Kan Labarin Mutuwar ‘Yan Mauludi A Hanyar Saminaka – Gwamnan Kaduna

Gwamna Uba Sani Ya Ziyarci Iyalan Malamar Addini Da Aka Kashe A Kaduna Saboda Zargin Satar Yara

June 28, 2026
Abubuwan Da Ba A Faɗa Ba Game Da Yadda Aka Hallaka Malamar Islamiyya A Kaduna

Abubuwan Da Ba A Faɗa Ba Game Da Yadda Aka Hallaka Malamar Islamiyya A Kaduna

June 28, 2026
Abubuwan Da Ke Tattare Da Jami’in Soja Sambo Dasuki

Abubuwan Da Ke Tattare Da Jami’in Soja Sambo Dasuki

June 28, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.