• English
  • Business News
Sunday, May 11, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

NIS Reshen Jihar Bayelsa Ta Yi Shirin Tunkarar Zaɓen 2023

by Yusuf Shuaibu
3 years ago
in Labarai
0
NIS Reshen Jihar Bayelsa Ta Yi Shirin Tunkarar Zaɓen 2023
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Hukumar shige da fice ta ƙasa (NIS) reshen Jihar Bayelsa ta gudanar da taron ganawa da masu ruwa da tsaki da shugabannin al’ummar Nijar, Benin, Togo, Ghana da kuma na Mali a Yenagoa.

Hukumar NIS reshen Jihar Bayelsa ta bayyana taron ganawar ne a cikin wata sanarwa da ta fitar a ranar 29 ga watan Satumbar 2022.

A zaman ganawarsa na musamman da kwanturololin hukumar na faɗin ƙasar nan a shalkwatan hukumar da ke Abuja, Shugaban hukumar NIS, CGI Isah Jere Idris ya ba su umurnin sa ido da duba waɗanda ba ‘yan Nijeriya ba domin shirin tunkarar zaɓen 2023, a cikin umurnin har da hana baƙin-haure yin zaɓe ko mallakar katin zaɓe ko kuma dukkan kayayyakin da ke da alaƙa da zane domin tsare iyakokin ƙasar nan.

  • Shirin Zaɓe: Mun Ƙwace Katin Zaɓe Da Shaidar Ɗan Ƙasa 526 Daga ‘Yan Ƙasar Waje – Shugaban NIS

Domin ƙarin haske a kan wannan umurni, hukumar NIS reshin Jihar Bayelsa ta yi gaban kanta wajen sake ilmantarwa da wayar da kan bakin-haure da ke zaune a Jihar Bayelsa domin cika wannan umurni wajen saka ido da kulawa da kwararowar baƙin-haure a cikin jihar, inda ake binciken maɓoyansu da ke saƙo da lungu a Yenagoa.

Sanarwar ta nuna cewa wasu daga cikin baƙin-hauren suna gudanar da sana’o’in da suka haɗa da gadi, wankin takalma, tala, sayar da fiyowata da yin acaɓa a ciki da wajen garin Yenagoa.

Labarai Masu Nasaba

Shugaban NPA Ya Sha Yabo Kan Yadda Ya Bunƙasa Tashar Jiragen Ruwa Ta Onne

Tarihin Sarkin Katsina Muhammadu Dikko (5)

Dukkan ɗaukacin rassan hukumar NIS an ba su umurnin sa ido da kulawa wajen bayyana wa hukumar rahoton sirri kan ayyukan da baƙin-haure suke gudanarwa a ƙananan hukumomi guda 8 da ke faɗin Jihar Bayelsa baya ga babban birnin jihar Yenago, wannan ƙoƙari ne na faɗaɗa umurnin da shugaban hukumar NIS ya bayar na ganin ya sauke nauyin da ya rataya a wuyansa, a matsayinsa na shugaban hukumar da ke kulawa da iyakokin Nijeriya.

Sanarwar ta ƙara da cewa wannan tsare-tsare zai ci gaba da gudana har zuwa zaɓen 2023 da ake fuskanta da kuma bayan zaɓen.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

ShareTweetSendShare
Previous Post

Sin Da Argentina Sun Sha Alwashin Yayata Manufar Samar Da Al’umma Mai Makomar Bai Daya

Next Post

Kasar Sin Ta Samu Babban Ci Gaba A Fannin Raya Karkara Cikin Shekaru 5 Da Suka Gabata

Related

Shugaban NPA Ya Sha Yabo Kan Yadda Ya Bunƙasa Tashar Jiragen Ruwa Ta Onne
Labarai

Shugaban NPA Ya Sha Yabo Kan Yadda Ya Bunƙasa Tashar Jiragen Ruwa Ta Onne

2 hours ago
Tarihin Sarkin Katsina Muhammadu Dikko (5)
Labarai

Tarihin Sarkin Katsina Muhammadu Dikko (5)

3 hours ago
Kaduna Ta Gano Ma’adanai 73, Yayin Da Take Neman Masu Zuba Jari
Labarai

Kaduna Ta Gano Ma’adanai 73, Yayin Da Take Neman Masu Zuba Jari

4 hours ago
Labarai

Kungiyar Malaman Jami’o’i Ta Ba Dalibai 164 Tallafin Karatu

16 hours ago
Dalilan Da Ke Nuna Malaman Makaranta Na Da Muhimmaci (5)
Labarai

Dalilan Da Ke Nuna Malaman Makaranta Na Da Muhimmaci (5)

17 hours ago
Ra’ayin Al’umma Game Da Iyaye Masu Furta Muggan Kalamai A Kan ‘Ya’yansu
Labarai

Ra’ayin Al’umma Game Da Iyaye Masu Furta Muggan Kalamai A Kan ‘Ya’yansu

19 hours ago
Next Post
Kasar Sin Ta Samu Babban Ci Gaba A Fannin Raya Karkara Cikin Shekaru 5 Da Suka Gabata

Kasar Sin Ta Samu Babban Ci Gaba A Fannin Raya Karkara Cikin Shekaru 5 Da Suka Gabata

LABARAI MASU NASABA

Rashin Hadin Kai Ke Dakile Ci Gaban Masana’antar Kannywood -Ayatullahi Tage

Rashin Hadin Kai Ke Dakile Ci Gaban Masana’antar Kannywood -Ayatullahi Tage

May 11, 2025
Barin Liverpool Ita Ce Shawara Mafi Wahala Da Na Taɓa Yankewa A Rayuwata -Alexander 

Barin Liverpool Ita Ce Shawara Mafi Wahala Da Na Taɓa Yankewa A Rayuwata -Alexander 

May 11, 2025
Shugaban NPA Ya Sha Yabo Kan Yadda Ya Bunƙasa Tashar Jiragen Ruwa Ta Onne

Shugaban NPA Ya Sha Yabo Kan Yadda Ya Bunƙasa Tashar Jiragen Ruwa Ta Onne

May 11, 2025
Tarihin Sarkin Katsina Muhammadu Dikko (5)

Tarihin Sarkin Katsina Muhammadu Dikko (5)

May 11, 2025
Kaduna Ta Gano Ma’adanai 73, Yayin Da Take Neman Masu Zuba Jari

Kaduna Ta Gano Ma’adanai 73, Yayin Da Take Neman Masu Zuba Jari

May 11, 2025
Tawagar Wanzar Da Zaman Lafiya Ta Farko Ta Sin Ta Dawo Daga Abyei Cikin Nasara

Tawagar Wanzar Da Zaman Lafiya Ta Farko Ta Sin Ta Dawo Daga Abyei Cikin Nasara

May 10, 2025
An Fara Taron Tattalin Arziki Da Cinikayya Na Matakin Koli Tsakanin Sin Da Amurka A Geneva

An Fara Taron Tattalin Arziki Da Cinikayya Na Matakin Koli Tsakanin Sin Da Amurka A Geneva

May 10, 2025
Sharhi: Sin Da Rasha Suna Sauke Nauyin Dake Wuyansu

Sharhi: Sin Da Rasha Suna Sauke Nauyin Dake Wuyansu

May 10, 2025

Kungiyar Malaman Jami’o’i Ta Ba Dalibai 164 Tallafin Karatu

May 10, 2025
Dalilan Da Ke Nuna Malaman Makaranta Na Da Muhimmaci (5)

Dalilan Da Ke Nuna Malaman Makaranta Na Da Muhimmaci (5)

May 10, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.