• English
  • Business News
Friday, November 7, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

NIS Reshen Jihar Bayelsa Ta Yi Shirin Tunkarar Zaɓen 2023

by Yusuf Shuaibu
3 years ago
NIS

Hukumar shige da fice ta ƙasa (NIS) reshen Jihar Bayelsa ta gudanar da taron ganawa da masu ruwa da tsaki da shugabannin al’ummar Nijar, Benin, Togo, Ghana da kuma na Mali a Yenagoa.

Hukumar NIS reshen Jihar Bayelsa ta bayyana taron ganawar ne a cikin wata sanarwa da ta fitar a ranar 29 ga watan Satumbar 2022.

A zaman ganawarsa na musamman da kwanturololin hukumar na faɗin ƙasar nan a shalkwatan hukumar da ke Abuja, Shugaban hukumar NIS, CGI Isah Jere Idris ya ba su umurnin sa ido da duba waɗanda ba ‘yan Nijeriya ba domin shirin tunkarar zaɓen 2023, a cikin umurnin har da hana baƙin-haure yin zaɓe ko mallakar katin zaɓe ko kuma dukkan kayayyakin da ke da alaƙa da zane domin tsare iyakokin ƙasar nan.

  • Shirin Zaɓe: Mun Ƙwace Katin Zaɓe Da Shaidar Ɗan Ƙasa 526 Daga ‘Yan Ƙasar Waje – Shugaban NIS

Domin ƙarin haske a kan wannan umurni, hukumar NIS reshin Jihar Bayelsa ta yi gaban kanta wajen sake ilmantarwa da wayar da kan bakin-haure da ke zaune a Jihar Bayelsa domin cika wannan umurni wajen saka ido da kulawa da kwararowar baƙin-haure a cikin jihar, inda ake binciken maɓoyansu da ke saƙo da lungu a Yenagoa.

Sanarwar ta nuna cewa wasu daga cikin baƙin-hauren suna gudanar da sana’o’in da suka haɗa da gadi, wankin takalma, tala, sayar da fiyowata da yin acaɓa a ciki da wajen garin Yenagoa.

LABARAI MASU NASABA

Hajjin 2026: NAHCON Ta Kammala Tantance Masaukai Da Ɗakunan Dafa Abincin Alhazai A Madinah

An Gano Gawar Wata Tsohuwa Mai Shekaru 96 Bayan Faɗawa Shadda A Kano

Dukkan ɗaukacin rassan hukumar NIS an ba su umurnin sa ido da kulawa wajen bayyana wa hukumar rahoton sirri kan ayyukan da baƙin-haure suke gudanarwa a ƙananan hukumomi guda 8 da ke faɗin Jihar Bayelsa baya ga babban birnin jihar Yenago, wannan ƙoƙari ne na faɗaɗa umurnin da shugaban hukumar NIS ya bayar na ganin ya sauke nauyin da ya rataya a wuyansa, a matsayinsa na shugaban hukumar da ke kulawa da iyakokin Nijeriya.

Sanarwar ta ƙara da cewa wannan tsare-tsare zai ci gaba da gudana har zuwa zaɓen 2023 da ake fuskanta da kuma bayan zaɓen.

ShareTweetSendShare

MASU ALAKA

Hajjin 2026: NAHCON Ta Kammala Tantance Masaukai Da Ɗakunan Dafa Abincin Alhazai A Madinah
Manyan Labarai

Hajjin 2026: NAHCON Ta Kammala Tantance Masaukai Da Ɗakunan Dafa Abincin Alhazai A Madinah

November 7, 2025
An Gano Gawar Wata Tsohuwa Mai Shekaru 96 Bayan Faɗawa Shadda A Kano
Labarai

An Gano Gawar Wata Tsohuwa Mai Shekaru 96 Bayan Faɗawa Shadda A Kano

November 7, 2025
Batun Kawo Harin Soja: ‘Yan Nijeriya Sun Yi Watsi Da Barazanar Trump
Manyan Labarai

Batun Kawo Harin Soja: ‘Yan Nijeriya Sun Yi Watsi Da Barazanar Trump

November 7, 2025
Next Post
Kasar Sin Ta Samu Babban Ci Gaba A Fannin Raya Karkara Cikin Shekaru 5 Da Suka Gabata

Kasar Sin Ta Samu Babban Ci Gaba A Fannin Raya Karkara Cikin Shekaru 5 Da Suka Gabata

LABARAI MASU NASABA

Rashin Daukar Tsauraran Matakai Na Iya Durkusar Da Bangaren Noma – Shehu Galadima

Hanyoyin Noma Na Gargajiya Ba Za Su Iya Wadata Abinci A Nijeriya Ba -Masanin Kimiyya

November 7, 2025
An Kaddamar Da Taron Kolin Wuzhen Na Ayyuka Masu Nasaba Da Yanar Gizo

An Kaddamar Da Taron Kolin Wuzhen Na Ayyuka Masu Nasaba Da Yanar Gizo

November 7, 2025
Hajjin 2026: NAHCON Ta Kammala Tantance Masaukai Da Ɗakunan Dafa Abincin Alhazai A Madinah

Hajjin 2026: NAHCON Ta Kammala Tantance Masaukai Da Ɗakunan Dafa Abincin Alhazai A Madinah

November 7, 2025
Sin Ta Kadammar Da Babban Jirgin Ruwan Dakon Jiragen Yaki Na CNS Fujian a Rundunar Sojan Ruwanta

Sin Ta Kadammar Da Babban Jirgin Ruwan Dakon Jiragen Yaki Na CNS Fujian a Rundunar Sojan Ruwanta

November 7, 2025
Xi Jinping Ya Taya Paul Biya Murnar Tazarce a Kamaru

Xi Jinping Ya Taya Paul Biya Murnar Tazarce a Kamaru

November 7, 2025
Dantsoho Ya Matsar Da Aikin Tashoshin Apapa Da Tin Can Zuwa Zango Na 1 Na 2026

Dantsoho Ya Matsar Da Aikin Tashoshin Apapa Da Tin Can Zuwa Zango Na 1 Na 2026

November 7, 2025
An Gano Gawar Wata Tsohuwa Mai Shekaru 96 Bayan Faɗawa Shadda A Kano

An Gano Gawar Wata Tsohuwa Mai Shekaru 96 Bayan Faɗawa Shadda A Kano

November 7, 2025

Ma’aikatan NPA Wasu Ginshikai Ne Na Ciyar Da NPA Gaba —Dantsoho

November 7, 2025
Batun Kawo Harin Soja: ‘Yan Nijeriya Sun Yi Watsi Da Barazanar Trump

Batun Kawo Harin Soja: ‘Yan Nijeriya Sun Yi Watsi Da Barazanar Trump

November 7, 2025
Barazanar Amurka Na Kawo Wa Nijeriya Hari 

Barazanar Amurka Na Kawo Wa Nijeriya Hari 

November 7, 2025

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.