• English
  • Business News
Sunday, June 8, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

NIS Ta Ƙaddamar Da Sabon Ingantaccen Fasfo A Ƙasar Kanada

CGI Isah Jere Ya Ce Za A Kawar Da Tsaikon Da Ake Samu Wajen Samun Fasfo

by yahuzajere
3 years ago
in Labarai
0
fasfo

Kwanturola Janar na NIS, CGI Isah Jere Idris (a dama) yayin da yake taya Ministan Cikin Gida, Rauf Aregbesola kaddamar da sabuwar cibiyar bayar da ingantaccen fasfo a ofishin jakadancin Nijeriya da ke Ottawa, kasar Kanada

Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Hukumar Kula da Shige da Fice ta Ƙasa (NIS) ta ƙaddamar da sabon ingantaccen fasfo da ake wa laƙabi da “enhanced e-passport” tare da buɗe ofishin da zai riƙa samarwa a Ottawa da ke yankin Ontario a ƙasar Kanada, domin bai wa ‘Yan Nijeriya mazauna ƙasar damar samun sabon fasfon mai matakai daban-daban.

Nijeriya dai tana daga cikin ƙasashe biyar na duniya kuma ta farko a Afirka da suka samar da sabon ingantaccen fasfon. Shi dai sabon fasfon, an tsara shi ne da fasahohin zamani tare da inganta tsaro a cikinsa da kuma ƙara yawan samfuransa ciki har da mai shafi 64 da ke aiki har na tsawon shekara 10 domin ƙara kyautata walwalar ‘Yan Nijeriya masu balaguro a ƙasashen duniya.

  • Kayan Angonci Sun Yi Batan Dabo, An Sace Sadakin Amarya A Taron Daurin Aure A Kano

Sakamakon tsaron da aka ƙara a sabon fasfon ta fuskoki 25 fiye da wanda ake amfani da shi a yanzu, maɓarnata da masu satar shaida ba za su iya amfani da shi ba wajen damfara.

Da yake jawabi a yayin ƙaddamarwar, Kwanturola Janar na NIS, CGI Isah Jere Idris, ya bayyana cewa duk da fara bayar da sabon ingantaccen fasfon a Kanada, za a ci gaba da bayar da tsohon da sabon a tare har zuwa lokacin da za a kammala aikin fasfunan da aka nema a baya.

“Za a ci gaba da bayar da sabon ingantaccen fasfon da kuma wanda ake bayarwa kafin zuwan sabon har sai lokacin da aka mayar da ɗaukacin cibiyoyin bayar da fasfo zuwa na sabon da aka samar”, ya bayyana.

Labarai Masu Nasaba

An Kama Magidanci A Bauchi Bisa Zargin Lalata Da Agolarsa

Hako Man Fetur: Jihar Neja Ta Nemi Hadin Gwiwar Kamfanin Dangote

Fasfo
CGI Isah Jere (na biyu a dama) yayin da Ministan Cikin Gida Aregbesola yake miqa wa Jakadan Nijeriya a Kanada, Mista Asekun sabon ingantaccen fasfon da aka kaddamar

Har ila yau, CGI Isah Jere ya ce za a magance tsaikon da ake samu wajen yi wa mutane fasfo matuƙar masu nema suna bin matakai da ƙa’idojin da aka shimfiɗa ta hanyar tabbatar da cewa sun gabatar da buƙatarsu ta fasfo ta shafin intanet tare da biyan kuɗi ta nan, da daidaita bayanan fasfonsu su yi daidai da bayanan da ke ƙunshe a katinsu na shaidar ɗan ƙasa (NIN).

Isah Jere ya ƙara jaddada cewa NIS za ta ci gaba da jajircewa wajen ganin ta sauke nauyin da tsarin mulkin ƙasa ya ɗora mata tare da kyautata mu’amala da abokan hulɗa a ko ina cikin faɗin duniya.

A nashi jawabin tun da farko, Ministan Cikin Gida, Rauf Ogbeni Aregbesola, ya bayyana cewa sakamakon ƙaddamar da ofishin sabon fasfon a Kanada, a halin yanzu ‘Yan Nijeriya mazauna can za su iya shiga shafin NIS na intanet su gabatar da buƙatunsu na fasfo kai-tsaye.

  • Daga Yanzu Wajibi Ne A Koyar Da Yara Da Harshen Gado A Firamare – Gwamnati

Ya ce, wa’adin da aka ɗiba ga mai neman sabon fasfo shi ne za a yi masa a cikin mako shida, yayin da wanda zai sabunta kuma za a yi masa a cikin mako uku. Waɗannan makonnin da aka ɗiba a cewar ministan, domin a bai wa NIS sarari ne ta yi bincike game da bayanan da mai neman fasfo ya gabatar da kuma tabbatar da ingancin aikin kamar yadda ake yi a duk ƙasashen duniya da suka ci gaba.

fasfo
Kwanturola Janar na NIS, CGI Isah Jere Idris (a hagu), Jakadan Nijeriya a Kanada, Mista Adeyinka Asekun da Ministan Cikin Gida, Rauf Aregbesola yayin kaddamarwar

Haka nan ya nanata muhimmancin daidaita bayanan fasfo da na katin ɗan ƙasa (NIN), domin a cewarsa, ana matuƙar samun matsala kan haka kuma da zarar an samu bambanci komai ƙanƙanta, za a samu tsaiko wajen aikin fasfon.

Wakazalika, da yake tofa albarkacin bakinsa, Jakadan Nijeriya a Kanada, Mista Adeyinka Asekun ya yaba wa Ministan da Kwanturola Janar na NIS bisa hoɓɓasar da suka yi wajen ƙaddamar da sabin ingantaccen fasfon a Kanada wanda ya ce ita ce ta uku da NIS ta samar da sabon fasfon baya ga Amurka da Ingila.

Ya shawarci ‘Yan Nijeriya da ke ƙasar su yi ƙoƙari su ci gajiyar wannan damar da NIS ta samar musu musamman wajen neman fasfo mai shafi 64 da ke aiki na tsawon shekara 10 wanda ake iya neman sabuntawa tun ana saura shekara ɗaya wa’adin aikinsa ya ƙare.

 

 


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

ShareTweetSendShare
Previous Post

Gwamnatin Tarayya Ta Nuna Takaicin Yadda Gwamnoni Ke Mayar Da Kauyuka Saniyar Ware

Next Post

Kotu Ta Bayar Da Umarnin A Cafko Mata Shugaban Sojojin Nijeriya, Faruk Yahaya

Related

‘Yansanda Sun Kashe Masu Garkuwa Da Mutane 8, Sun Kubutar Da Mutane 3 A Jihar Bauchi
Labarai

An Kama Magidanci A Bauchi Bisa Zargin Lalata Da Agolarsa

3 hours ago
Hako Man Fetur: Jihar Neja Ta Nemi Hadin Gwiwar Kamfanin Dangote
Labarai

Hako Man Fetur: Jihar Neja Ta Nemi Hadin Gwiwar Kamfanin Dangote

5 hours ago
Aikin Ba Da Ilmi Ba Makamin Takarar Jam’iyyu Ba Ne
Ra'ayi Riga

Aikin Ba Da Ilmi Ba Makamin Takarar Jam’iyyu Ba Ne

6 hours ago
Sojojin Sama Sun Tarwatsa Maɓoyar Ƴan Ta’adda, Ya Daƙile Hari Ranar Idi A Borno
Labarai

Sojojin Sama Sun Tarwatsa Maɓoyar Ƴan Ta’adda, Ya Daƙile Hari Ranar Idi A Borno

10 hours ago
fasfo
Rahotonni

2027: An Yi Kira Ga Masu Mulki Da Su Rungumi Tafarkin Inganta Rayuwar Al’umma

11 hours ago
Tufka Da Warwarar INEC Kan Yiwuwar Zaben 2023
Labarai

Ana Ci Gaba Da Samun Rudani Yayin Da INEC Ta Jinkirta Rajistar Sabbin Jam’iyyu

12 hours ago
Next Post
Kotu Ta Bayar Da Umarnin A Cafko Mata Shugaban Sojojin Nijeriya, Faruk Yahaya

Kotu Ta Bayar Da Umarnin A Cafko Mata Shugaban Sojojin Nijeriya, Faruk Yahaya

LABARAI MASU NASABA

Tattaunawar Da Shugabannin Sin Da Amurka Suka Yi Ta Wayar Tarho Ta Ba Da Jagoranci Ga Dangantakar Dake Tsakanin Kasashen Biyu

Tattaunawar Da Shugabannin Sin Da Amurka Suka Yi Ta Wayar Tarho Ta Ba Da Jagoranci Ga Dangantakar Dake Tsakanin Kasashen Biyu

June 7, 2025
‘Yansanda Sun Kashe Masu Garkuwa Da Mutane 8, Sun Kubutar Da Mutane 3 A Jihar Bauchi

An Kama Magidanci A Bauchi Bisa Zargin Lalata Da Agolarsa

June 7, 2025
Dabarar Yaudara Ta Kasar Philippines Kan Batun Tekun Kudancin Sin Ta Fito Fili

Dabarar Yaudara Ta Kasar Philippines Kan Batun Tekun Kudancin Sin Ta Fito Fili

June 7, 2025
Wang Yi Ya Nanata Matsayin Taiwan Yayin Tattaunawa Da Takwaransa Na Faransa

Wang Yi Ya Nanata Matsayin Taiwan Yayin Tattaunawa Da Takwaransa Na Faransa

June 7, 2025
Hako Man Fetur: Jihar Neja Ta Nemi Hadin Gwiwar Kamfanin Dangote

Hako Man Fetur: Jihar Neja Ta Nemi Hadin Gwiwar Kamfanin Dangote

June 7, 2025
Aikin Ba Da Ilmi Ba Makamin Takarar Jam’iyyu Ba Ne

Aikin Ba Da Ilmi Ba Makamin Takarar Jam’iyyu Ba Ne

June 7, 2025
Hukumar NPA Ta Bayar Da Kwangilar Aikin Ruwa Na Tashar Lekki

Hukumar NPA Ta Bayar Da Kwangilar Aikin Ruwa Na Tashar Lekki

June 7, 2025
Roland Busch: Kasar Sin Tana Daya Daga Cikin Kasuwanni Mafi Kuzari A Bangaren Kirkire-kirkire A Duniya

Roland Busch: Kasar Sin Tana Daya Daga Cikin Kasuwanni Mafi Kuzari A Bangaren Kirkire-kirkire A Duniya

June 7, 2025
Gwamnatin Tarayya Da Hadin Gwiwar IFAD Za Su Yi Wa Manoma Rijista Domin Tantance Su

Gwamnatin Tarayya Da Hadin Gwiwar IFAD Za Su Yi Wa Manoma Rijista Domin Tantance Su

June 7, 2025
Dalibai Sama Da Miliyan 13 Ne Za Su Rubuta Jarrabawar Shiga Jami’a Ta Kasar Sin

Dalibai Sama Da Miliyan 13 Ne Za Su Rubuta Jarrabawar Shiga Jami’a Ta Kasar Sin

June 7, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.