• English
  • Business News
Saturday, September 6, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

NIS Ta Bi Ƙa’ida Sau Da Ƙafa Wajen Bai Wa David Nwamina Fasfo – CGI Isah Jere

by yahuzajere
3 years ago
in Labarai
0
NIS Ta Bi Ƙa’ida Sau Da Ƙafa Wajen Bai Wa David Nwamina Fasfo – CGI Isah Jere
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Hukumar Kula da Shige da Fice ta Nijeriya (NIS), ta tabbatar da cewa ta bi ƙa’ida sau da ƙafa wajen bayar da Fasfon Nijeriya ga ɗan samarin nan, Mista David Ukpo Nwamina da ake ƙiƙi-ƙaƙa a kansa game da batun cire wata gava a jikinsa domin dasa wa wata yarinya mara lafiya, ‘yar gidan tsohon mataimakin shugaban Majalisar Dattawa, Sanata Ike Ekweremadu.

Wata sanarwar manema labarai da Shugaban NIS, CGI Isah Idris Jere ya fitar tare da rattaba hannu da kansa, ta yi bayanin cewa yamaɗiɗin da wasu ke yaɗawa, “cewa hukumar ba ta tantance takardun wanda aka bai wa fasfon yadda ya kamata ba, ba gaskiya ba ne illa ƙazafi da wasu suka kitsa don kawai su shafa wa hukumar kashin kaji a vata mata suna.

  • Yajin Aikin ASUU: Dalibai Sun Yi Barazanar Rufe Tituna, Tashoshin Jirgin Sama Da Na Kasa
  • Da Aka Gama Rarraba Wa Deliget Kudi, Sai Kuma Me? (Ra’ayinmu)

“Don haka gaskiyar abin da ya faru game da lamarin shi ne, shi wanda ake magana a kansa, Mista David Ukpo Nwamina ya gabatar da buƙatarsa ta sabon fasfo da aka inganta kuma ya biya kuɗin fasfon ta manhajar intanet wanda bayan haka ne ya tafi Ofishin Fasfo na Abuja da ke Gwagwalada a ranar 2 ga Nuwambar 2021 domin amsa tambayoyi. Domin ƙarfafa samun fasfon nasa, Mista David Nwamina ya gabatar da dukkan takardun ƙa’ida da suka wajaba, da suka haɗa da takardar haihuwarsa wadda Hukumar ƙidaya ta ƙasa (NPC) ta ba shi, da ta nuna an haife shi a ranar 12 ga Oktobar 2000, sannan bayanan shaidar haihuwarsa ta lambar ɗan ƙasa wadda Hukumar NIMC ta ba shi, sun yi daidai da na takardar haihuwarsa sai kuma takardar shaidar asalinsa wadda Ofishin Gwamnatin Jihar Ebonyi na Abuja ya ba shi da kuma takardar shaidar mutumin da ya tsaya masa da aka rattaba wa hannu kamar yadda ya kamata.”

Saboda haka bisa waɗannan hujjoji, NIS tace tana sanar da jama’a cewa ba ta wallafa ranar haihuwa ko wasu bayanai a duk wani fasfon Nijeriya har sai an tantance su yadda ya kamata tare da tantance shi kansa mai neman fasfo. “Don haka batun Mista Nwamina ba zai zama daban ko na ɗanmowa ba.”

Har ila yau, Hukumar ta NIS ta tabbatar wa da al’umma irin duƙufar da ta yi wajen kare mutuncin fasfon Nijeriya, kana ta yi amfani da wannan damar wajen yin kira ga jama’a su guji furta irin waɗannan ƙarairayi domin za su iya zubar da kimar hukumar a idon duniya.

Labarai Masu Nasaba

‘Yansanda Sun Fara Binciken Yadda Matasa Suka Kone Wata Mata Har Lahira A Neja

Mutanen Gari Sun Kashe ‘Yan Bindiga, Sun Ceto Wasu A Sakkwato

  • https://portal.immigration.gov.ng/

Mista David Ukpo Nwamina dai na can Ingila ana ci gaba da bincike a kansa da wanda abin ya shafa Sanata Ike Ekweremadu.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

ShareTweetSendShare
Previous Post

Har Yanzu Ina Neman Abokin Takara — Tinubu

Next Post

Na Dakatar Da Ayyukan Banga Har Gwamnati Ta Binciki Dalilin Kamani – Manta

Related

‘Yansanda Sun Fara Binciken Yadda Matasa Suka Kone Wata Mata Har Lahira A Neja
Tsaro

‘Yansanda Sun Fara Binciken Yadda Matasa Suka Kone Wata Mata Har Lahira A Neja

41 minutes ago
Mutanen Gari Sun Kashe ‘Yan Bindiga, Sun Ceto Wasu A Sakkwato
Manyan Labarai

Mutanen Gari Sun Kashe ‘Yan Bindiga, Sun Ceto Wasu A Sakkwato

1 hour ago
Gwamnatin Kogi Ta Jaddada Aniyar Magance Ambaliya Da Zaizayar Ƙasa
Labarai

Gwamnatin Kogi Ta Jaddada Aniyar Magance Ambaliya Da Zaizayar Ƙasa

3 hours ago
Zulum Ya Ba Da Tallafin ₦300,000 Ga Iyaye, Da Ciyar Da Ɗalibai 90 Kyauta A Borno
Labarai

Zulum Ya Ba Da Tallafin ₦300,000 Ga Iyaye, Da Ciyar Da Ɗalibai 90 Kyauta A Borno

4 hours ago
Labarai

Ilimi Shi Ne Matakin Nasarar Rayuwar Duniya Da Lahira – Yerima Shettima

7 hours ago
NUPENG Za Ta Fara Yajin Aiki, Dangote Na Shirin Shiga Harkar Sufurin Mai
Manyan Labarai

NUPENG Za Ta Fara Yajin Aiki, Dangote Na Shirin Shiga Harkar Sufurin Mai

8 hours ago
Next Post
Na Dakatar Da Ayyukan Banga Har Gwamnati Ta Binciki Dalilin Kamani – Manta

Na Dakatar Da Ayyukan Banga Har Gwamnati Ta Binciki Dalilin Kamani - Manta

LABARAI MASU NASABA

‘Yansanda Sun Fara Binciken Yadda Matasa Suka Kone Wata Mata Har Lahira A Neja

‘Yansanda Sun Fara Binciken Yadda Matasa Suka Kone Wata Mata Har Lahira A Neja

September 6, 2025
Mutanen Gari Sun Kashe ‘Yan Bindiga, Sun Ceto Wasu A Sakkwato

Mutanen Gari Sun Kashe ‘Yan Bindiga, Sun Ceto Wasu A Sakkwato

September 6, 2025
Nazari Kan Bukatar Manoma Su Rika Yi Wa Mangwaro Ban-ruwa

Nazari Kan Bukatar Manoma Su Rika Yi Wa Mangwaro Ban-ruwa

September 6, 2025
Muna Bukatar Karin Hekta 500,000 Domin Noman Kwakwar Manja – POFON

Muna Bukatar Karin Hekta 500,000 Domin Noman Kwakwar Manja – POFON

September 6, 2025
Gwamnatin Kogi Ta Jaddada Aniyar Magance Ambaliya Da Zaizayar Ƙasa

Gwamnatin Kogi Ta Jaddada Aniyar Magance Ambaliya Da Zaizayar Ƙasa

September 6, 2025
Zulum Ya Ba Da Tallafin ₦300,000 Ga Iyaye, Da Ciyar Da Ɗalibai 90 Kyauta A Borno

Zulum Ya Ba Da Tallafin ₦300,000 Ga Iyaye, Da Ciyar Da Ɗalibai 90 Kyauta A Borno

September 6, 2025
A Zango Mai Zuwa Za A Fara Aikin Dala Miliyan Daya A Tashar Jirgin Ruwa Ta Legas – Dantsoho

Kungiyoyi Da Abokan Arziki Na Ci Gaba Da Taya Dantsoho Murna

September 6, 2025
Fursunoni Ba Za Su Samu Damar Kada Kuri’a Ba A Zaben 2023 – INEC

Rudani Ya Kunno Kai Yayin Da INEC Ta Ki Amincewa Da Shugabancin ADC

September 6, 2025
Tsohon Mataimakin Gwamnan Gombe Da Wasu jigogin PDP Sun Koma APC

Tsohon Mataimakin Gwamnan Gombe Da Wasu jigogin PDP Sun Koma APC

September 6, 2025

Ilimi Shi Ne Matakin Nasarar Rayuwar Duniya Da Lahira – Yerima Shettima

September 6, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.