• English
  • Business News
Saturday, October 11, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

NIS Ta Bi Ƙa’ida Sau Da Ƙafa Wajen Bai Wa David Nwamina Fasfo – CGI Isah Jere

by yahuzajere
3 years ago
David Nwamina

Hukumar Kula da Shige da Fice ta Nijeriya (NIS), ta tabbatar da cewa ta bi ƙa’ida sau da ƙafa wajen bayar da Fasfon Nijeriya ga ɗan samarin nan, Mista David Ukpo Nwamina da ake ƙiƙi-ƙaƙa a kansa game da batun cire wata gava a jikinsa domin dasa wa wata yarinya mara lafiya, ‘yar gidan tsohon mataimakin shugaban Majalisar Dattawa, Sanata Ike Ekweremadu.

Wata sanarwar manema labarai da Shugaban NIS, CGI Isah Idris Jere ya fitar tare da rattaba hannu da kansa, ta yi bayanin cewa yamaɗiɗin da wasu ke yaɗawa, “cewa hukumar ba ta tantance takardun wanda aka bai wa fasfon yadda ya kamata ba, ba gaskiya ba ne illa ƙazafi da wasu suka kitsa don kawai su shafa wa hukumar kashin kaji a vata mata suna.

  • Yajin Aikin ASUU: Dalibai Sun Yi Barazanar Rufe Tituna, Tashoshin Jirgin Sama Da Na Kasa
  • Da Aka Gama Rarraba Wa Deliget Kudi, Sai Kuma Me? (Ra’ayinmu)

“Don haka gaskiyar abin da ya faru game da lamarin shi ne, shi wanda ake magana a kansa, Mista David Ukpo Nwamina ya gabatar da buƙatarsa ta sabon fasfo da aka inganta kuma ya biya kuɗin fasfon ta manhajar intanet wanda bayan haka ne ya tafi Ofishin Fasfo na Abuja da ke Gwagwalada a ranar 2 ga Nuwambar 2021 domin amsa tambayoyi. Domin ƙarfafa samun fasfon nasa, Mista David Nwamina ya gabatar da dukkan takardun ƙa’ida da suka wajaba, da suka haɗa da takardar haihuwarsa wadda Hukumar ƙidaya ta ƙasa (NPC) ta ba shi, da ta nuna an haife shi a ranar 12 ga Oktobar 2000, sannan bayanan shaidar haihuwarsa ta lambar ɗan ƙasa wadda Hukumar NIMC ta ba shi, sun yi daidai da na takardar haihuwarsa sai kuma takardar shaidar asalinsa wadda Ofishin Gwamnatin Jihar Ebonyi na Abuja ya ba shi da kuma takardar shaidar mutumin da ya tsaya masa da aka rattaba wa hannu kamar yadda ya kamata.”

Saboda haka bisa waɗannan hujjoji, NIS tace tana sanar da jama’a cewa ba ta wallafa ranar haihuwa ko wasu bayanai a duk wani fasfon Nijeriya har sai an tantance su yadda ya kamata tare da tantance shi kansa mai neman fasfo. “Don haka batun Mista Nwamina ba zai zama daban ko na ɗanmowa ba.”

Har ila yau, Hukumar ta NIS ta tabbatar wa da al’umma irin duƙufar da ta yi wajen kare mutuncin fasfon Nijeriya, kana ta yi amfani da wannan damar wajen yin kira ga jama’a su guji furta irin waɗannan ƙarairayi domin za su iya zubar da kimar hukumar a idon duniya.

LABARAI MASU NASABA

Masana Sun Bayyana Yadda Za A Magance Ficewar Kamfanoni Da Masana’antu Daga Nijeriya

Shugaba Tinubu Ya Yi Wa Maryam Sanda Afuwa Bayan Shafe Shekaru 6 A Gidan Yari

  • https://portal.immigration.gov.ng/

Mista David Ukpo Nwamina dai na can Ingila ana ci gaba da bincike a kansa da wanda abin ya shafa Sanata Ike Ekweremadu.

ShareTweetSendShare

MASU ALAKA

Masana Sun Bayyana Yadda Za A Magance Ficewar Kamfanoni Da Masana’antu Daga Nijeriya
Rahotonni

Masana Sun Bayyana Yadda Za A Magance Ficewar Kamfanoni Da Masana’antu Daga Nijeriya

October 11, 2025
Shugaba Tinubu Ya Yi Wa Maryam Sanda Afuwa Bayan Shafe Shekaru 6 A Gidan Yari
Manyan Labarai

Shugaba Tinubu Ya Yi Wa Maryam Sanda Afuwa Bayan Shafe Shekaru 6 A Gidan Yari

October 11, 2025
Ranar Malamai Ta Duniya: Rashin Kulawa Ke Sa Malamai Barin Aiki
Rahotonni

Ranar Malamai Ta Duniya: Rashin Kulawa Ke Sa Malamai Barin Aiki

October 11, 2025
Next Post
Na Dakatar Da Ayyukan Banga Har Gwamnati Ta Binciki Dalilin Kamani – Manta

Na Dakatar Da Ayyukan Banga Har Gwamnati Ta Binciki Dalilin Kamani - Manta

LABARAI MASU NASABA

Wang Yi: Sin Na Maraba Da Dukkanin Matakai Na Dawo Da Zaman Lafiya A Gaza

Wang Yi: Sin Na Maraba Da Dukkanin Matakai Na Dawo Da Zaman Lafiya A Gaza

October 11, 2025
Ayyukan Da Suka Sauya Fuskar Zamfara A Ƙarƙashin Gwamna Dauda Lawal

Ayyukan Da Suka Sauya Fuskar Zamfara A Ƙarƙashin Gwamna Dauda Lawal

October 11, 2025
Masanin Kenya: Taron Kolin Mata Ya Shaida Alkawarin Sin Na Inganta Hakkin Mata

Masanin Kenya: Taron Kolin Mata Ya Shaida Alkawarin Sin Na Inganta Hakkin Mata

October 11, 2025
Neman Kudi Ne Ya Kawo Ni Masana’antar Kannywood Ba Fadakarwa Ba – Khadija Muhammad 

Neman Kudi Ne Ya Kawo Ni Masana’antar Kannywood Ba Fadakarwa Ba – Khadija Muhammad 

October 11, 2025
Sin Ta Mayar Da Martani Game Da Takunkumin Da Amurka Ta Sanyawa Masana’antunta 

Sin Ta Mayar Da Martani Game Da Takunkumin Da Amurka Ta Sanyawa Masana’antunta 

October 11, 2025
Me Ya Sa Jaruman Masana’antar Kannywood Ke Auren Sirri?

Me Ya Sa Jaruman Masana’antar Kannywood Ke Auren Sirri?

October 11, 2025
Yanayin Sashen Samar Da Gidaje Na Sin Ya Kara Inganta Tsakanin 2021 Zuwa 2025

Yanayin Sashen Samar Da Gidaje Na Sin Ya Kara Inganta Tsakanin 2021 Zuwa 2025

October 11, 2025
Tarihin Hassan Usman Katsina (1)

Tarihin Hassan Usman Katsina (1)

October 11, 2025
An Gudanar Da Taron Hadin Kai Na Raya Albarkatun Kasa Tsakanin Sin Da Mozambique

An Gudanar Da Taron Hadin Kai Na Raya Albarkatun Kasa Tsakanin Sin Da Mozambique

October 11, 2025
Masana Sun Bayyana Yadda Za A Magance Ficewar Kamfanoni Da Masana’antu Daga Nijeriya

Masana Sun Bayyana Yadda Za A Magance Ficewar Kamfanoni Da Masana’antu Daga Nijeriya

October 11, 2025

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.