Abdulrazaq Yahuza Jere">
Leadership Hausa Newspapers
No Result
View All Result
  • LABARAI
  • WASANNI
  • RAHOTANNI
  • SIYASA
  • KASUWANCI
  • ADABI
  • RA’AYINMU
  • TATTAUNAWA
  • BIDIYO
  • MAKALAR YAU
  • LABARAI
  • WASANNI
  • RAHOTANNI
  • SIYASA
  • KASUWANCI
  • ADABI
  • RA’AYINMU
  • TATTAUNAWA
  • BIDIYO
  • MAKALAR YAU
No Result
View All Result
Leadership Hausa Newspapers
No Result
View All Result
Home LABARAI

NIS Ta Kaddamar Da Sansanin Jami’anta Na Iyakar Kasa A Efraya Ta Jihar Kuros Riba

by Abdulrazaq Yahuza Jere
February 19, 2021
in LABARAI
2 min read
Kaddamar Da Sansani

Shugaban NIS Muhammad Babandede (na uku daga hagu), Kwanturolan NIS na Jihar Kuros Riba Mista Okey Ezugwu (a hagu), Babban Sakataren Tsaro na Jihar Kuros Riba Dakta Alfred Mboto (na biyu a hagu) da sauran manyan baki yayin kaddamar da sansanin jami’an na NIS a Efraya ta Jihar Kuros Riba.

WhatsAppShare on FacebookShare on TwitterShare on Telegram

A ci gaba da kokarin da yake yi na karfafa ayyukan jami’ai a kan iyakokin kasa da bakin-haure ke amfani da su wajen silalowa cikin kasa, Shugaban Hukumar Kula da Shige da Fice ta Kasa (NIS), CGI Muhammad Babandede ya kaddamar da karin wani sansani na iyaka a yankin Efraya na Jihar Kuros Riba.

Ya kaddamar da sansanin ne a ranar Juma’ar nan 19 ga Fabarairun 2021.

Da yake jawabi a yayin kaddamarwar, Babandede ya bayyana cewa samar da sansanin wani karin tagomashi ne a kokarin da hukumar ke yi na tabbatar da cewa an gina sansanin jami’ai a dukkan iyakokin kasar nan domin samun nasarar aiwatar da tsare-tsare na kula da iyakoki kamar yadda ya kamata.

Ya ce a karkashinsa, hukumar ta ba da fifiko ga gina wadannan sansanonin ne domin shawo kan karancin ababen more rayuwa na aiki da ake bukata domin jami’ai su ji dadin gudanar da ayyukansu, inda ya nunar da cewa sansanonin sun bai wa NIS damar magance kalubalen da ake gamuwa da su wajen dakile aikata miyagun laifuka a iyakokin kasa irin su fashin daji da safarar bil’adama.

Babandede ya gode wa manyan bakin da suka halarci bikin kaddamarwar. Musamman ya jinjina wa Gwamnan Kuros Riba Sanata Ben Ayade da Basaraken Karamar Hukumar Etung, Ntue Atue, Dakta Emmanuel Oru Ojong da kuma shugaban karamar hukumar yankin.

Sanarwar da ta fito daga Jami’in hulda da jama’a na NIS, DCI Sunday James, ta ce shugaban hukumar ya sake nanata kudirinsa na ziyartar duk sassan da jami’ansa ke aiki domin share musu hayawayensu da kansa ba sako ba, domin nuna shugabanci nagari.

SendShareTweetShare
Previous Post

Sin Ta Jaddada Adawa Da Sukar Da Canada Ta Yi Mata Game Da Tsare Wasu ‘Yan Kasar

Next Post

Mbappe Da Haaland Za Su Shafe Messi Da Ronaldo Nan Gaba Kadan

RelatedPosts

Jami’ar Tarayya Ta Gusau Ta Musanta Labarin Harin ‘Yan Bindiga

Jami’ar Tarayya Ta Gusau Ta Musanta Labarin Harin ‘Yan Bindiga

by Abdulrazaq Yahuza Jere
11 hours ago
0

Daga Hussaini Yero, Shugabannin Jami'ar gwamnatin Tarayya dake Gusau (FUG)...

An Yi Wa Buhari Da Osinbajo Allurar Rigakafin Korona

An Yi Wa Buhari Da Osinbajo Allurar Rigakafin Korona

by Abdulrazaq Yahuza Jere
15 hours ago
0

Daga Sulaiman Ibrahim An yi wa Shugaba Muhammadu Buhari da...

Mukabalar

Kotu Ta Dakatar Da Yin Mukabalar Sheikh Abduljabbar Da Malaman Kano.

by Abdulrazaq Yahuza Jere
21 hours ago
0

Daga Abdullahi Muhammad Sheka, Wata kotu a Jihar Kano ta...

Next Post
Haaland

Mbappe Da Haaland Za Su Shafe Messi Da Ronaldo Nan Gaba Kadan

Domin sanya talla ko karin bayani a tuntube wannan numbar +2348126152609.

ADVERTISEMENT
  • LABARAI
  • WASANNI
  • RAHOTANNI
  • SIYASA
  • KASUWANCI
  • ADABI
  • RA’AYINMU
  • TATTAUNAWA
  • BIDIYO
  • MAKALAR YAU
Advertise with us

© 2020 Leadership Group .

No Result
View All Result
  • LABARAI
  • WASANNI
  • RAHOTANNI
  • SIYASA
  • KASUWANCI
  • ADABI
  • RA’AYINMU
  • TATTAUNAWA
  • BIDIYO
  • MAKALAR YAU

© 2020 Leadership Group .

Go to mobile version