ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Wednesday, November 12, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

NIS Ta Kalubalanci ‘Yan Jarida Kan Bayar Da Rahotannin Tafiye-tafiyen Kasashen Waje

by Sulaiman
2 years ago
tafiye-tafiye

Hukumar Kula da Shige da Fice ta Kasa (NIS) ta sake jaddada kira ga kafafen yada labarai su rubanya kwazonsu wajen bayar da rahotannin da suka kamata a kan tafiye-tafiyen kasashen waje ta barauniyar hanya da kuma fadakar da jama’a game da hadarin da ke tattare da hakan.

Hukumar ta yi kiran ne a yayin gudanar da wani taron wayar da kai ga ‘yan jaridu da ya gudana a Abuja a ranar Litinin, a otel din Reiz Continental.

  • Zargin Kisan Kai: Zargin Da Ake Wa Doguwa Ya Saba Da Kundin Tsarin Mulki – Kotu

Shugaban Hukumar, CGI Isah Idris Jere ya yi kiran ta bakin wakiliyarsa a taron, Babbar Jami’a Mai Kula da Sashen Tafiye-tafiye a shalkwatar hukumar, ACG Ngozi Odikpo. Wakiliyar ta gabatar da Makala a kan abubuwan da ya kamata ‘yan jarida su mayar da hankali a kai wajen bayar da rahotanninsu game da yadda jama’a ke kaura ta hanyar da ta dace da kuma masu bin barauniyar hanya, tana mai jaddada cewa, ya kamata kafafen yada labarai su rika hadawa da labarun mutanen da suka fada komar masu safarar bil’adama ba bisa ka’ida ba domin wayar da kan al’umma a kan mummunan hadarin da ke tattare da hakan.

ADVERTISEMENT

Har ila yau, tsohon shugaban hukumar ta NIS, Muhammad Babandede wanda ya yi jawabi a kan batutuwan da suka shafi tafiye-tafiye da suka halasta da wadanda suka haramta, da kuma su kansu mutanen da ke tafiye-tafiyen, ya nuna akwai bukatar kafafen yada labarai su rika bayar da rahotannin da suka dace na kiyaye mutuncin Nijeriya, yana mai ba da misali da irin kalaman da ake amfani da su wajen bayar da rahotannin da suka shafi kasa domin wayar da kan ‘yan kasa.

Ya nemi a rika fada wa ‘yan kasa gaskiyar abin da yake faruwa ta hanyar ilmantarwa da kuma fadakar da su game da tafiye-tafiye da ke kan ka’ida da kuma wadanda suka saba.

LABARAI MASU NASABA

Bayan Ganawa Da Tinubu, COAS Ya Tabbatar Wa ‘Yan Nijeriya Samun Ingantaccen Tsaro

Za Mu Ci Gaba Da Tallafa Wa ’Yansanda Domin Inganta Ayyukan Su A Zamfara – Gwamna Lawal

Kungiyar ‘Yan Jarida Masu Rubuta Labarun Tafiye-tafiyen Kasashen Waje ta Duniya (JIFORM) tare da hadin gwiwar Cibiyar Kula da Tafiye-tafiye ta Kasar Jamus (NGC) suka shirya taron a kan yadda za a inganta bayar da rahotannin da suka shafi tafiye-tafiye ba bisa ka’ida ba da hadarin hakan.

Wakazalika, Kwanturolan NIS na Jihar Ribas, CI James Sunday ya gabatar da makaloli biyu a wurin taron domin wayar da kan ‘yan jarida a kan hakkokin da suka rataya a wuyarsu na bayar da rahotannin tafiye-tafiyen da suka dace da wadanda suka saba wa doka.

Taron ya kuma samu halartar manyan baki daga ma’aikatu da hukumomin gwamnati da sauran kungiyoyi masu nasaba da kai-komon jama’a.

 

 

ShareTweetSendShare

MASU ALAKA

Coas
Manyan Labarai

Bayan Ganawa Da Tinubu, COAS Ya Tabbatar Wa ‘Yan Nijeriya Samun Ingantaccen Tsaro

November 11, 2025
Za Mu Ci Gaba Da Tallafa Wa ’Yansanda Domin Inganta Ayyukan Su A Zamfara – Gwamna Lawal
Labarai

Za Mu Ci Gaba Da Tallafa Wa ’Yansanda Domin Inganta Ayyukan Su A Zamfara – Gwamna Lawal

November 11, 2025
‘Yan Bindiga Sun Kashe Mutum 3 A Nasarawa
Labarai

‘Yan Bindiga Sun Kashe Mutum 3 A Nasarawa

November 11, 2025
Next Post
‘Yan Siyasar Japan Sun Sake Fuskantar Cikas Wajen Aiwatar Da Shirin Zubar Da Dagwalon Ruwan Nukiliya A Cikin Teku

‘Yan Siyasar Japan Sun Sake Fuskantar Cikas Wajen Aiwatar Da Shirin Zubar Da Dagwalon Ruwan Nukiliya A Cikin Teku

LABARAI MASU NASABA

Coas

Bayan Ganawa Da Tinubu, COAS Ya Tabbatar Wa ‘Yan Nijeriya Samun Ingantaccen Tsaro

November 11, 2025
Sin: Amurka Ba Ta Sa Lura Ga Kare Hakkin Dan Adam

Sin: Amurka Ba Ta Sa Lura Ga Kare Hakkin Dan Adam

November 11, 2025
Bikin CIIE Ya Nuna Yadda Sin Ke Ba Da Jagora Kan Harkokin Bude Kofa

Bikin CIIE Ya Nuna Yadda Sin Ke Ba Da Jagora Kan Harkokin Bude Kofa

November 11, 2025
Za Mu Ci Gaba Da Tallafa Wa ’Yansanda Domin Inganta Ayyukan Su A Zamfara – Gwamna Lawal

Za Mu Ci Gaba Da Tallafa Wa ’Yansanda Domin Inganta Ayyukan Su A Zamfara – Gwamna Lawal

November 11, 2025
CIIE Ya Kasance Gadar Sada Tattalin Arzikin Kasar Sin Da Na Duniya

CIIE Ya Kasance Gadar Sada Tattalin Arzikin Kasar Sin Da Na Duniya

November 11, 2025
CMG Ya Gabatar Da Sabbin Manhajoji 10 Da Ya Kirkiro Don Watsa Gasar Wasannin Motsa Jiki Ta Kasar Sin Karo Na 15

CMG Ya Gabatar Da Sabbin Manhajoji 10 Da Ya Kirkiro Don Watsa Gasar Wasannin Motsa Jiki Ta Kasar Sin Karo Na 15

November 11, 2025
‘Yan Bindiga Sun Kashe Mutum 3 A Nasarawa

‘Yan Bindiga Sun Kashe Mutum 3 A Nasarawa

November 11, 2025
Cikin Wata Ɗaya, ‘Yansanda Sun Kama Mutane 200 Da Ake Zargi Da Laifuka A Katsina

Cikin Wata Ɗaya, ‘Yansanda Sun Kama Mutane 200 Da Ake Zargi Da Laifuka A Katsina

November 11, 2025
CIIE Ya Ba ‘Yan Kasuwar Afirka Damar Habaka Cinikinsu Da Sin 

CIIE Ya Ba ‘Yan Kasuwar Afirka Damar Habaka Cinikinsu Da Sin 

November 11, 2025
Me Sabon Tarihin Da Aka Kafa A Baje Kolin CIIE Ke Nunawa?

Me Sabon Tarihin Da Aka Kafa A Baje Kolin CIIE Ke Nunawa?

November 11, 2025

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.