• English
  • Business News
Friday, July 11, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

NIS Ta Shirya Taro A Kan Alfanun Tattalin Arzikin Teku Ga Manyan ‘Yan Kasuwa A Ribas

by Sulaiman
2 years ago
in Labarai
0
Nis
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Gwamnatin Jihar Ribas karkashin jagorancin Gwamna Siminalayi Fubara tare da hadin guiwar Hukumar Shige da Fice ta Nijeriya (NIS) sun karbi bakuncin manyan ‘yan kasuwa a kokarin gwamnatin na habbaka tattalin arziki ta bangaren saka hannun jari a bangaren alfanun albarkatun cikin ruwa.

Taron bitar na kwana daya wanda hukumar NIS da gwamnatin jihar Ribas suka shirya, ana sa ran zai samar da wata dama da za ta taimaka wa jihar Ribas da gwamnatin tarayya wajen binciko tarun albarkatun arziki da ke cikin teku.

  • Za Mu Inganta NTA Ta Fara Gogayya Da Takwarorinta Na Duniya – Ministan Yada Labarai 
  • Jami’ar Aliko Dangote Ta Karyata Jita-jitar Daukar Ma’aikata Da Ake Yadawa

Mukaddashiyar Kwanturola Janar ta Hukumar NIS, Caroline Wuraola Adepoju, wadda ta halarci taron bitar da aka yi a Kamfanin Gwamnan Jihar, wanda Sakataren Gwamnatin Jihar, Dakta Tammy Danagogo ya wakilta, ta yaba wa tsare-tsaren Gwamnatin tarayya na sake habbaka tattalin arziki wanda ya kai ga amincewa da kafa ma’aikatar tattalin arziki ta ruwa ta tarayya don fadadawa da kuma karkata tattalin arzikin Nijeriya daga man fetur da iskar gas zuwa albarkatun ruwa da tekun da ke kewayen Nijeriya.

Jihohin da ke zagaye da ruwa da ‘yan gabar teku sun hada da: Rivers, Bayelsa, Delta, Edo, Ondo, Lagos, Anambra, Cross Ribas, Akwa Ibom, Kebbi da Neja.

Daga cikin wadanda suka halarci taron akwai tsohon Kwanturola Janar na Hukumar NIS, Dakta David Shikfu Paraddang; Shugaban Elshcon Group, Dakta Emi Membere – Otaji; Mataimakin Shugaban Kungiyoyin Kasuwanci, Masana’antu, Ma’adinai da Aikin Noma, Majalisar Dillalan Jiragen Ruwa wanda Mista Glory Onojedo ya wakilta; Shugaban hukumar kula da tashar jiragen ruwa ta Nijeriya (NPA), Mista Michael Adamu; Kodinetan shiyyar NIMASA ta Kudu-maso-Kudu, Mista Yusuf Barde; Shugaban kamfanin Sigma Nigeria Limited, Dakta Soky Amachree da shugabannin masana’antu masu zaman kansu.

Labarai Masu Nasaba

Rikicin Masarautar Kano Ya Kara Zafafa

Akwai Bukatar Hada Kai Da Aiki Tare Tsakanin Hukumomin Tsaro

Mahalarta taron sun yabawa Kwanturolan hukumar NIS mai kula da reshen Jihar Ribas da tawagarsa bisa shirya wannan taron karawa juna sani a lokacin da ake bukatar taron domin samun kyakkyawar fahimta akan sabuwar ma’aikatar ta yadda masu zuba jari za su nutsu da ma’aikatar da kuma tsare-tsarenta.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: Albarkatun ruwaNISTekun Lagos
ShareTweetSendShare
Previous Post

Kasashen Yamma Suna Tsotse Jinin ‘Yan Afirka Yayin Da Kasar Sin Ke Kawo Bege

Next Post

Ronaldo Ya Jefa Kwallo Biyu Yayin Da Portugal Ta Lallasa Bosnia Da Ci 5-0

Related

Rikicin Masarautar Kano Ya Kara Zafafa
Manyan Labarai

Rikicin Masarautar Kano Ya Kara Zafafa

1 hour ago
Yunkurin Magance Matsalar Tsaro Da Rigingimu A Arewa…
Manyan Labarai

Akwai Bukatar Hada Kai Da Aiki Tare Tsakanin Hukumomin Tsaro

2 hours ago
Ƴan Bindiga Sun Yi Wa Jami’an NSCDC Ƙwantan Ɓauna A Binuwe
Manyan Labarai

Ƴan Bindiga Sun Yi Wa Jami’an NSCDC Ƙwantan Ɓauna A Binuwe

12 hours ago
An Kama Magungunan Jabu Na Fiye Da Naira Biliyan Ɗaya A Kano
Labarai

An Kama Magungunan Jabu Na Fiye Da Naira Biliyan Ɗaya A Kano

13 hours ago
Majalisar Ta Kwace Shugabacin Kwamitin Da Natasha Ke Jagoranta
Labarai

Majalisar Ta Kwace Shugabacin Kwamitin Da Natasha Ke Jagoranta

15 hours ago
Shiri Na Shekaru Biyar Biyar: Sirrin Tabbatar Da Ci Gaban Kasar Sin
Ra'ayi Riga

Shiri Na Shekaru Biyar Biyar: Sirrin Tabbatar Da Ci Gaban Kasar Sin

16 hours ago
Next Post
Ronaldo

Ronaldo Ya Jefa Kwallo Biyu Yayin Da Portugal Ta Lallasa Bosnia Da Ci 5-0

LABARAI MASU NASABA

NPA Ta Tarbi Babban Jirgin ‘Ruwa MB Ocean Dragon’ Don Bunkasa Ayyukanta

NPA Ta Tarbi Babban Jirgin ‘Ruwa MB Ocean Dragon’ Don Bunkasa Ayyukanta

July 11, 2025
Rikicin Masarautar Kano Ya Kara Zafafa

Rikicin Masarautar Kano Ya Kara Zafafa

July 11, 2025
Yunkurin Magance Matsalar Tsaro Da Rigingimu A Arewa…

Akwai Bukatar Hada Kai Da Aiki Tare Tsakanin Hukumomin Tsaro

July 11, 2025
Ƙwallon Mata: Nijeriya Ta Kai Matakin Kwata Fainal Bayan Doke Botswana

Ƙwallon Mata: Nijeriya Ta Kai Matakin Kwata Fainal Bayan Doke Botswana

July 10, 2025
Mataimakin Babban Magatakardan MDD: Sin Aminiya Ce Da Afirka Za Ta Iya Dogaro Da Ita

Mataimakin Babban Magatakardan MDD: Sin Aminiya Ce Da Afirka Za Ta Iya Dogaro Da Ita

July 10, 2025
Li Qiang Ya Gana Da Manyan Jami’an Masar Da ALLi Qiang Ya Gana Da Manyan Jami’an Masar Da AL

Li Qiang Ya Gana Da Manyan Jami’an Masar Da ALLi Qiang Ya Gana Da Manyan Jami’an Masar Da AL

July 10, 2025
Ƴan Bindiga Sun Yi Wa Jami’an NSCDC Ƙwantan Ɓauna A Binuwe

Ƴan Bindiga Sun Yi Wa Jami’an NSCDC Ƙwantan Ɓauna A Binuwe

July 10, 2025
Yadda JKS Ta Jure Tsawon Tarihin Gwagwarmaya Da Cimma Nasarori

Yadda JKS Ta Jure Tsawon Tarihin Gwagwarmaya Da Cimma Nasarori

July 10, 2025
An Kama Magungunan Jabu Na Fiye Da Naira Biliyan Ɗaya A Kano

An Kama Magungunan Jabu Na Fiye Da Naira Biliyan Ɗaya A Kano

July 10, 2025
Xi Jinping Ya Aike Da Sakon Taya Murnar Bude Taron Ministocin Kasa Da Kasa Na Tattaunawa Kan Wayewar Kan Bil Adam

Xi Jinping Ya Aike Da Sakon Taya Murnar Bude Taron Ministocin Kasa Da Kasa Na Tattaunawa Kan Wayewar Kan Bil Adam

July 10, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.