• English
  • Business News
Sunday, June 22, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

NIS Za Ta Ƙaddamar Da Cibiyar Bayar Da Sabon Ingantaccen Fasfo A Zariya Da Daura

...Yayin Da Ganduje Ya Kaddamar Da Katafariyar Cibiyar Wallafa Fasfo A Kano

by Sabo Ahmad
2 years ago
in Labarai
0
NIS Za Ta Ƙaddamar Da Cibiyar Bayar Da Sabon Ingantaccen Fasfo A Zariya Da Daura
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

A kokarin da take yi na inganta ayyukan samar da fasfo ga dimbin masu nema da ke zaune a Kano da kewaye, Hukumar Kula da Shige da Fice ta Kasa (NIS) ta kaddamar da Katafariyar Cibiyar Samar da Fasfo da za ta rika aiki ga ofisoshin fasfo na Jigawa, Katsina da kuma Dawakin Kudu da ke Kanon.

Da yake kaddamar da katafariyar cibiyar a ranar Laraba 11 ga Janairun 2023, Gwamna Abdullahi Umar na Jihar Kano ya taya NIS murna bisa dimbin nasarorin da take samu musamman kasancewarta ta farko da ta fara samar da sabon ingantaccen fasfo na zamani a duk fadin yankin Afirka.

Gwamnan wanda Kwamishinan Kasafin Kudi, Alhaji Danazumi Grazo ya wakilta ya jinjina wa NIS bisa kafa cibiyar a cikin Kano mai dimbin tarihi, yana mai cewa, ya yi amanna, zabar Kano da aka yi wajen kafa cibiyar ba zai rasa nasaba da yanayin zaman lafiya da ake mora a jihar ba.

A jawabinsa, Babban Shugaban NIS, Isah Jere Idris, MFR, ya tabbatar wa da ‘yan Nijeriya cewa, ana samun ci gaba a shirin sauya fasalin fasfo da ake yi a halin yanzu, musannam kan tsarin yadda za a yi saurin gane waɗanda suka shigo daga sassa daban-daban na duniya.

Shugaban ya ce, yanzu haka a Kano, sun ƙaddamar da cibiyar aikin yin e-Passport da aka inganta na zamani, kuma suna ci gaba da faɗaɗawa zuwa sauran wurare.
Wanda ya wakilce shi a wajen taron, ACG Sadat Hassan, ya ce, ya yi matuƙar farin ciki da jin irin ci gaban da ake samu a dukkan sassan yin fasfo ɗin a dukkan faɗin ƙasar nan, wanda ya nuna yadda mutanenmu ke bayar da cikakken haɗin kai. “Mun shirya za mu shafe mako biyu cif muna yin wannan aikin daga yanzu har zuwa ranar 21 ga wannan watan na Janairu, wanda kuma a wannan lokacin ne za kamala shirin.”

Labarai Masu Nasaba

Harin Amurka A Wurare 3 Na Nukiliyar Iran: Babu Wani Lahani A Harin Bama-baman – Iran

Kiran Gwamnatin Tarayya Ga ‘Yan Jarida: Ku Zama Jigo Wajen Gina Dimokuraɗiyyar Nijeriya

  • Tinubu Ne Kadai Zai Iya Magance Rashin Tsaro Da Tabarbarewar Tattalin Arziki – Buhari 

Ya kuma ƙara da cewa NIS za ta ci gaba da bayar da fasfo ɗin a tsakanin mako uku zuwa mako shida, kana iya tura bayananka, musamman ga mutanen da ba su da matsala wajen tura bayanan ko kuma a rubuta takardar buƙata.Ya ƙara faɗa da babbar murya cewa NIN na daga cikin shika-shikan yin fasfo wanda kuma dole a tabbatar da cewa, bayanan da ke cikinsu ba su saɓa ba.

“Muna ƙara samun ci gaba ne don haka muke kira ga masu neman fasfo ɗin su guji yin bayanan ƙarya su tabbatar sun yi bayanan da kansu kuma sun biya dukkan kuɗaɗen da hannunsu , za su shigar da bayanansu ta hanyar shiga wannan adireshi, passport.immigration.goɓ.ng.Za kuma mu ci gaba da ƙoƙarin kawo ƙarshen dukkan matsalolin da za a ci karo da su.”

Haka kuma ya ce, zai yi amfani da wannan damar wajen gode wa jama’a kan cikakken goyon bayan da suke samu a wajensu. Haka kuma ya nuna cewa, yanzu haka dai NIS ba ta ɗaukar mutane, kuma duk lokacin da za ta ɗauka za ta sanar a kafafe yaɗa labarai, wato lokacin da muka samu amincewar gwamnatin tarayya.

NIS

Shugaban hukumar, Jere ya tabbatar da cewa, jami’an hukumar a tsaye suke ƙyam wajen ganin ganin sun gudanar da ayyukansu kamar yadda doka ta tanada, saboda haka ne ne ma y ace kullun suke ƙara samun ci gaba wajen gudanar da ayyukansu musamman a ɓangaren gudanar da fasfo da ɓangaren tsaro da samun walwala.

Saboda haka ne ma NIS take son isar da saƙonta ga dukkan jama’a cewa akwai fasfo guda 110,000 da masu su ba su zo sun karɓa ba a jihohi 36 da ke ƙasar nan da Abuja. Saboda haka, shugaban hukumar ya raba manyan jami’an hukumar tun daga kan mataimakinsa zuwa shiyya-shiyya domin ganin an tafiyar ta tsarin bayar da fasfo ɗin kamar yadda ya kamata.

Saboda haka ne ma ake shawartar ‘yan Nijeriya waɗanda suka yi fasfo ɗin ba su karɓa ba su je ofishin yin fasfo na NIS ɗin su duba nasu.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

ShareTweetSendShare
Previous Post

Firaministan Habasha Ya Gana Da Ministan Harkokin Wajen Kasar Sin Qin Gang

Next Post

An Yi Shawarwari Karo Na 8 Bisa Manyan Tsare-Tsare Tsakanin Sin Da AU

Related

Harin Amurka A Wurare 3 Na Nukiliyar Iran: Babu Wani Lahani A Harin Bama-baman – Iran
Manyan Labarai

Harin Amurka A Wurare 3 Na Nukiliyar Iran: Babu Wani Lahani A Harin Bama-baman – Iran

4 hours ago
Kiran Gwamnatin Tarayya Ga ‘Yan Jarida: Ku Zama Jigo Wajen Gina Dimokuraɗiyyar Nijeriya
Labarai

Kiran Gwamnatin Tarayya Ga ‘Yan Jarida: Ku Zama Jigo Wajen Gina Dimokuraɗiyyar Nijeriya

6 hours ago
Matsalolin Rayuwa: Matasan Suleja Na Buƙatar Ƙarfafa Gwuiwa
Labarai

Matsalolin Rayuwa: Matasan Suleja Na Buƙatar Ƙarfafa Gwuiwa

6 hours ago
Batun Rushe Gidaje A Unguwar Rimin Zakara Ba Gaskiya Ba Ne – Alhaji Naziru 
Labarai

Batun Rushe Gidaje A Unguwar Rimin Zakara Ba Gaskiya Ba Ne – Alhaji Naziru 

9 hours ago
FIRS Ta Umarci A Rika Bude Ofishoshin Karbar Haraji A karshen Mako
Labarai

FIRS Ta Umarci A Rika Bude Ofishoshin Karbar Haraji A karshen Mako

18 hours ago
EFCC Ta Gurfanar Da Wasu Kamfanoni Biyu Gaban Kuliya Bisa Damfarar Naira Miliyan 80
Labarai

EFCC Ta Gurfanar Da Wasu Kamfanoni Biyu Gaban Kuliya Bisa Damfarar Naira Miliyan 80

20 hours ago
Next Post
An Yi Shawarwari Karo Na 8 Bisa Manyan Tsare-Tsare Tsakanin Sin Da AU

An Yi Shawarwari Karo Na 8 Bisa Manyan Tsare-Tsare Tsakanin Sin Da AU

LABARAI MASU NASABA

Fim Babbar Hanya Ce Ta Nishaɗantar Da Al’umma -D Malam Dan Bola (2)

Fim Babbar Hanya Ce Ta Nishaɗantar Da Al’umma -D Malam Dan Bola (2)

June 22, 2025
Bernado Silba Ya Zama Sabon Kyaftin Din Manchester City 

Bernado Silba Ya Zama Sabon Kyaftin Din Manchester City 

June 22, 2025
Harin Amurka A Wurare 3 Na Nukiliyar Iran: Babu Wani Lahani A Harin Bama-baman – Iran

Harin Amurka A Wurare 3 Na Nukiliyar Iran: Babu Wani Lahani A Harin Bama-baman – Iran

June 22, 2025
Abin Da Ya Sa Ilimi Yake Da Muhimmanci Ga Rayuwar Al’umma (6)

Hikimar Yunƙurin Sake Farfaɗo Da Noman Filanten A Jihar Nasarawa

June 22, 2025
Me Zai Faru Idan Iran Ta Datse Mashigar Hormuz Sanadiyar Hare-Haren Isra’ila?

Me Zai Faru Idan Iran Ta Datse Mashigar Hormuz Sanadiyar Hare-Haren Isra’ila?

June 22, 2025
Kiran Gwamnatin Tarayya Ga ‘Yan Jarida: Ku Zama Jigo Wajen Gina Dimokuraɗiyyar Nijeriya

Kiran Gwamnatin Tarayya Ga ‘Yan Jarida: Ku Zama Jigo Wajen Gina Dimokuraɗiyyar Nijeriya

June 22, 2025
Matsalolin Rayuwa: Matasan Suleja Na Buƙatar Ƙarfafa Gwuiwa

Matsalolin Rayuwa: Matasan Suleja Na Buƙatar Ƙarfafa Gwuiwa

June 22, 2025
Babban Al’amari Ne A Samu Ƴar Shekara 6 Ta Haddace Qur’ani A Makarantar Raudatul Jannah – Mai Sikeli

Babban Al’amari Ne A Samu Ƴar Shekara 6 Ta Haddace Qur’ani A Makarantar Raudatul Jannah – Mai Sikeli

June 22, 2025
Liverpool Za Ta Kece Raini Da Bournemouth, Arsena Za Ta Bakunci Man Utd A Wasan Mako Na Firimiya Ta Baɗi

Liverpool Za Ta Kece Raini Da Bournemouth, Arsena Za Ta Bakunci Man Utd A Wasan Mako Na Firimiya Ta Baɗi

June 22, 2025
Batun Rushe Gidaje A Unguwar Rimin Zakara Ba Gaskiya Ba Ne – Alhaji Naziru 

Batun Rushe Gidaje A Unguwar Rimin Zakara Ba Gaskiya Ba Ne – Alhaji Naziru 

June 22, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.