• English
  • Business News
Sunday, September 7, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Nnamdi Kanu Ya Nemi Diyyar Biliyan 100 Kan Ci Gaba Da Tsare Shi Da Gwamnatin Tarayya Ke Yi 

by Sadiq
3 years ago
in Manyan Labarai
0
Nnamdi Kanu Ya Nemi Diyyar Biliyan 100 Kan Ci Gaba Da Tsare Shi Da Gwamnatin Tarayya Ke Yi 
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Shugaban masu fafutukar kafa kasar Biyafara (IPOB), Nnamdi Kanu, ya shigar da karar gwamnatin tarayya a gaban kotu kan ci gaba da tsare shi da hukumar tsaro ta farin kaya (DSS) ke yi.

A karar da aka shigar a babban kotun tarayya da ke Abuja, Kanu na neman a gaggauta sakin sa daga hukumar DSS tare da biyansa diyyar Naira biliyan 100 saboda tauye hakkinsa na ‘yanci da mutuncin dan Adam.

  • Ana Zargin Wani Mahaifi Da Karya Hannun Jaririnsa Saboda Yana Damunsa Da Kuka
  • Rashin Tsaro: Amurka Ta Umarci Jami’anta Su Fice Daga Abuja

Kanu ya ce karar ta zama dole ne biyo bayan gazawar gwamnatin tarayya na yin biyayya ga hukuncin da kotun daukaka kara ta yanke a ranar 13 ga Oktoba, wanda ya yi watsi da tuhumar ta’addancin da ake yi masa.

Kotun, wadda Mista Mike Ozekhome, SAN, ya shigar a madadin Kanu, mai kwanan wata 21 ga Oktoba na dauke da kara mai lamba FHC/ABJ/CS/1945/2022.

Kanu ya ce an yi shari’ar ne bisa tanadin kundin tsarin mulkin 1999.

Labarai Masu Nasaba

El-Rufai Ba Mai Gidana Ba Ne – In Ji Gwamna Uba Sani⁩

Ƴan Ta’adda Sun Kai Hari Kachia, Sun Kashe Mutum 8, Sun Sace Wasu Da Dama

“Saboda sashe na 46 (1) na Kundin Tsarin Mulki na 1999 da doka ta 1 da ta 2(1) na Dokokin Hakki (Tabbatar da Hukunci), duk mutumin da aka yi zargin cewa wani daga cikin tanade-tanaden na 4 na kundin tsarin mulkin kasar da ya ke, wanda yake da hakkin, ko ya kasance, ko kuma ana iya cin karo da shi a kowace jiha dangane da shi, na iya neman babbar kotun jihar domin ta yi masa hukunci.”

A cikin karar, Kanu yana son a bayyana cewa ci gaba da tsare shi da gwamnati ke yi daga ranar 13 ga Oktoba zuwa yau, ba daidai ba ne, zalunci, rashin sanin ya kamata ne, kuma ba bisa ka’ida ba.

“Ya keta hakkina na mutunta bil Adama, ‘yancin kai kamar yadda sashe na 34, 35, 36, 39, da 41 na kundin tsarin mulkin 1999 ya tabbatar.

Kanu kuma ya nemi a umarci wadanda ake kara da su sake shi daga hannunsu ba tare da wani sharadi ba.

Ya sake neman a hana wadanda ake kara shiga hakkinsa ko mu’amala da shi ta hanyar da ta dace da hakkinsa na asali da kundin tsarin mulki na 1999 ya ba shi.

Bugu da kari, yana neman a biya shi diyyar Naira biliyan 100 ga wadanda ake kara saboda tauye masa hakkinsa.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: BiyafaraDiyyar Naira Biliyan 100DSSGwamnatin TarayyaKotuNnamdi KanuTsarews
ShareTweetSendShare
Previous Post

Ana Zargin Wani Mahaifi Da Karya Hannun Jaririnsa Saboda Yana Damunsa Da Kuka

Next Post

Da Dumi-Dumi: Bankin CBN Zai Sake Sauya Fasalin Naira N200, N500 Da N1,000

Related

El-Rufai Ba Mai Gidana Ba Ne – In Ji Gwamna Uba Sani⁩
Manyan Labarai

El-Rufai Ba Mai Gidana Ba Ne – In Ji Gwamna Uba Sani⁩

40 minutes ago
Ƴan Ta’adda Sun Kai Hari Kachia, Sun Kashe Mutum 8, Sun Sace Wasu Da Dama
Manyan Labarai

Ƴan Ta’adda Sun Kai Hari Kachia, Sun Kashe Mutum 8, Sun Sace Wasu Da Dama

2 hours ago
NWDC Za Ta Sanya Hannu Kan MoU Na Dala Miliyan 200 Don Inganta Noma
Manyan Labarai

NWDC Za Ta Sanya Hannu Kan MoU Na Dala Miliyan 200 Don Inganta Noma

3 hours ago
Gwamnatin Tarayya Ta Kira Taron Gaggawa Don Hana Yajin Aikin NUPENG
Manyan Labarai

Gwamnatin Tarayya Ta Kira Taron Gaggawa Don Hana Yajin Aikin NUPENG

7 hours ago
Mun Tara Kuɗi Sama Da Naira Miliyan 170 Na Fatun Layya – Sheikh Bala Lau 
Manyan Labarai

Mun Tara Kuɗi Sama Da Naira Miliyan 170 Na Fatun Layya – Sheikh Bala Lau 

15 hours ago
An Fara Biyan Ma’aikata Sabon Mafi Ƙarancin Albashin N70,000 A Borno
Manyan Labarai

Boko Haram Ta Hallaka Mutane 61 A Jihar Borno

1 day ago
Next Post
Da Dumi-Dumi: Bankin CBN Zai Sake Sauya Fasalin Naira N200, N500 Da N1,000

Da Dumi-Dumi: Bankin CBN Zai Sake Sauya Fasalin Naira N200, N500 Da N1,000

LABARAI MASU NASABA

Kudin Ajiya Na Sin A Ketare Ya Karu A Watan Agusta

Kudin Ajiya Na Sin A Ketare Ya Karu A Watan Agusta

September 7, 2025
El-Rufai Ba Mai Gidana Ba Ne – In Ji Gwamna Uba Sani⁩

El-Rufai Ba Mai Gidana Ba Ne – In Ji Gwamna Uba Sani⁩

September 7, 2025
Sojoji Sun Kashe Riƙaƙƙen Ɗan Bindiga Kachalla Balla Da Wasu Biyar A Kogi

Sojoji Sun Kashe Riƙaƙƙen Ɗan Bindiga Kachalla Balla Da Wasu Biyar A Kogi

September 7, 2025
An Fara Jigila Kai Tsaye Daga Lardin Zhejiang Na Sin Zuwa Nahiyar Afrika

An Fara Jigila Kai Tsaye Daga Lardin Zhejiang Na Sin Zuwa Nahiyar Afrika

September 7, 2025
Kungiyoyin Gasar Firimiya Sun Kashe Dala Biliyan 4 A Kasuwar Saye Da Sayar Da ‘Yan Kwallo Ta Bana

Kungiyoyin Gasar Firimiya Sun Kashe Dala Biliyan 4 A Kasuwar Saye Da Sayar Da ‘Yan Kwallo Ta Bana

September 7, 2025
Ƴan Ta’adda Sun Kai Hari Kachia, Sun Kashe Mutum 8, Sun Sace Wasu Da Dama

Ƴan Ta’adda Sun Kai Hari Kachia, Sun Kashe Mutum 8, Sun Sace Wasu Da Dama

September 7, 2025
NWDC Za Ta Sanya Hannu Kan MoU Na Dala Miliyan 200 Don Inganta Noma

NWDC Za Ta Sanya Hannu Kan MoU Na Dala Miliyan 200 Don Inganta Noma

September 7, 2025
Sin Da AU Sun Yi Alkawarin Daukaka Tsaro Da Adalci A Duniya

Sin Da AU Sun Yi Alkawarin Daukaka Tsaro Da Adalci A Duniya

September 7, 2025
Duk Wanda Ya Girme Ni Ubangidana Ne A Harkar Fim – Hauwa Garba (2)

Duk Wanda Ya Girme Ni Ubangidana Ne A Harkar Fim – Hauwa Garba (2)

September 7, 2025
Rundunar Sojojin Sin Ta Yi Tsokaci Game Da Ratsawar Jiragen Ruwan Yakin Canada Da Australiya A Mashigin Tekun Taiwan

Rundunar Sojojin Sin Ta Yi Tsokaci Game Da Ratsawar Jiragen Ruwan Yakin Canada Da Australiya A Mashigin Tekun Taiwan

September 7, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.