• Leadership Hausa
Saturday, April 1, 2023
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Sana’a Sa’a
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Sana’a Sa’a
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Noman Kankana Na Kara Bunkasa A Jihar Jigawa

by Abubakar Abba
2 months ago
in Noma Da Kiwo
0
Noman Kankana Na Kara Bunkasa A Jihar Jigawa
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Manoman kankana a jihar Jigawa na sa ran samun riba mai yawa saboda yadda ta yi kyau a bana.

A kowace shekara, a lokacin sanyi manoman na kankana a jihar Jigawa suke dibanta tare da sayar da ita a sassa daban-daban na kasar nan, har ma da wasu kasashen da ke makwabtaka da jihar.

  • Babban Taron LEADERSHIP Karo Na 14 Zai Gudana Ranar Talata
  • Karin Bayani Kan Harin Bom Din Da Ya Kashe Fulani 39 A Nasarawa — Ganau

Daya daga cikin manoman na kankana a jihar, mai suna Muhammad Afno wanda ya fito daga karamar hukumar Guri, ya bayyana cewa, ya sayar da kankanar mai yawa a bana, ya kuma samu riba mai yawa.

  Muhammad Afno ya ci gaba da cewa, ya sayar da kowace kankanar daya a kan naira 40,000.

A cewar Muhammad, ya shafe shekaru yana yin noman na kankana, wanda har ya yi auri mata biyu ya haifi ‘ya’ya goma, wadanda dukkaninsu yake ci gaba daukar dawainiyarsu ta hanyar wannan sana’ar.

Labarai Masu Nasaba

Manoman Rani Na Sa Ran Samar Da Shinkafa Da Alkama Mai Yawa A Taraba

Yadda Noman Karas Ke Kara Bunkasa

  .Muhammad ya ci gaba da cewa, akasari yana kai kankanar ce zuwa kasar Afrika ta Kudu da kuma wasu sassa na kudancin kasar nan domin sayar da ita.

Sai dai, Muhammad ya kola kan yadda rashin farashin man fetur a kasar nan ke zamo wa sana’ar ta sa kalubale wajen safarar ta.

Har ila yau, sauran manoman ta a yankin sun bayyana cewa, biyo bayan annobar ambaliyar ruwa da aka samu a kakar noman bara a yankin, hakan ya sa sun kara mayar da hankali wajen yin nomanta da rani.

.Shi ma wani manominta mai suna IbrahimTakazza ya sanar da cewa, ana samun riba mai yawa a nomanta, musamman a lokacin sanyi.

Bugu da kari, wani manominta mai suna Alhaji Ibrahim Mai Kolawa ya bayyana cewa,  bayan da ya sayar da ita ya samu rubin kudaden da ya kashe wajen nomanta.

Haka kuma, a yankin Karnaya da ke cikin karamar hukumar Dutse, akasarin manoman na kankana a yankin sun bayyana cewa, sun yi girbinta mai dimbin yawa tare da samun riba mai yawa, sabanin a shekarun baya.

An ruwaito cewa, kankana ta fi yin saurin girma a dausayin noma mai kyau domin kashi 90 a cikin dari na kankana ruwa ne, inda hakan ya sa take jima wa ba ta lalace ba.

Tags: JigawaKankanaNoma
ShareTweetSendShare
Previous Post

Masani: Sin Za Ta Iya Taka Muhimmiyar Rawa Wajen Bunkasa Ci Gaban Duniya A Shekarar 2023

Next Post

Bikin Bazara Na Gargajiyar Kasar Sin Ya Kara Azama Kan Farfadowar Tattalin Arzikin Duniya

Related

Manoman Rani Na Sa Ran Samar Da Shinkafa Da Alkama Mai Yawa A Taraba
Noma Da Kiwo

Manoman Rani Na Sa Ran Samar Da Shinkafa Da Alkama Mai Yawa A Taraba

6 days ago
Yadda Noman Karas Ke Kara Bunkasa
Noma Da Kiwo

Yadda Noman Karas Ke Kara Bunkasa

4 weeks ago
Masana Sun Kara Fito Da Dabarun Noman Shinkafa Ta Yadda Za A Kara Samun Riba
Noma Da Kiwo

Masana Sun Kara Fito Da Dabarun Noman Shinkafa Ta Yadda Za A Kara Samun Riba

4 weeks ago
Faduwar Farashin Kaudar Tumatir Zai Rage Wa Manoma Karfin Gwiwa
Noma Da Kiwo

Faduwar Farashin Kaudar Tumatir Zai Rage Wa Manoma Karfin Gwiwa

1 month ago
Manoman Alkama 50,000 Suka Samu Tallafi A Jihohi 13 —FMAN
Noma Da Kiwo

Manoman Alkama 50,000 Suka Samu Tallafi A Jihohi 13 —FMAN

1 month ago
Abin Da Ya Sa Manoma Suka Ki Sayar Wa Da ‘Yan  Kasuwa Amfanin Gonakansu
Noma Da Kiwo

Abin Da Ya Sa Manoma Suka Ki Sayar Wa Da ‘Yan  Kasuwa Amfanin Gonakansu

1 month ago
Next Post
Bikin Bazara Na Gargajiyar Kasar Sin Ya Kara Azama Kan Farfadowar Tattalin Arzikin Duniya

Bikin Bazara Na Gargajiyar Kasar Sin Ya Kara Azama Kan Farfadowar Tattalin Arzikin Duniya

LABARAI MASU NASABA

An Yanke Wa Wasu ‘Yan China 2 Hukuncin Daurin Shekaru 12 A Sakkwato

An Yanke Wa Wasu ‘Yan China 2 Hukuncin Daurin Shekaru 12 A Sakkwato

March 31, 2023
Sin Ta Harba Sabon Rukunin Taurarin Dan Adam Irin Su Na Farko A Duniya

Sin Ta Harba Sabon Rukunin Taurarin Dan Adam Irin Su Na Farko A Duniya

March 31, 2023
Zababben Gwamnan Katsina Ya Gana Da Buhari, Ya Ce Matsalar Tsaro Zai Fi Bai Wa Muhimmanci 

Zababben Gwamnan Katsina Ya Gana Da Buhari, Ya Ce Matsalar Tsaro Zai Fi Bai Wa Muhimmanci 

March 31, 2023
Kasar Sin Ta Bayar Da Shawarwari Dangane Da Yadda Za A Aiwatar Da Sanarwar Vienna Yadda Ya Kamata

Kasar Sin Ta Bayar Da Shawarwari Dangane Da Yadda Za A Aiwatar Da Sanarwar Vienna Yadda Ya Kamata

March 31, 2023
Mutum 14 Sun Shiga Hannun ‘Yan Sanda A Kano Kan Aikata Fashi Da Makami

Mutum 14 Sun Shiga Hannun ‘Yan Sanda A Kano Kan Aikata Fashi Da Makami

March 31, 2023
Ana Fatan A Hada Kai Wajen Shawo Kan Kalubalen Dake Addabar Duniya

Ana Fatan A Hada Kai Wajen Shawo Kan Kalubalen Dake Addabar Duniya

March 31, 2023
Ba Zan Tsoma Baki A Gwamnatin Abba Ba –Kwankwaso

Ba Zan Tsoma Baki A Gwamnatin Abba Ba –Kwankwaso

March 31, 2023
Taron Kolin Demokuradiyya Na Amurka Ya Shaidawa Duniya Ma’auni Biyu Da Amurka Ta Dauka Kan Batun Demokuradiyya

Taron Kolin Demokuradiyya Na Amurka Ya Shaidawa Duniya Ma’auni Biyu Da Amurka Ta Dauka Kan Batun Demokuradiyya

March 31, 2023
Har Yanzu Ni Ke Da Cikakken Iko A Matsayin Gwamnan Kano —Ganduje Ga Abba Gida-Gida

Har Yanzu Ni Ke Da Cikakken Iko A Matsayin Gwamnan Kano —Ganduje Ga Abba Gida-Gida

March 31, 2023
Boao: Kasar Sin Ta Karfafa Gwiwar Kasa Da Kasa

Boao: Kasar Sin Ta Karfafa Gwiwar Kasa Da Kasa

March 31, 2023
ADVERTISEMENT
Advertise with us

© 2022 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2022 Leadership Media Group - All Right Reserved.