• English
  • Business News
Saturday, August 23, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

NPA Ta Buƙaci A Yi Nazari Kan Tsarin Bunƙasa Tashoshin Jiragen Ruwa Na Ƙasa Da Ƙasa

by Bello Hamza
8 months ago
in Labarai
0
NPA Ta Buƙaci A Yi Nazari Kan Tsarin Bunƙasa Tashoshin Jiragen Ruwa Na Ƙasa Da Ƙasa
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Manajin Darakta na Hukumar Tashar Jirgin Ruwa ta Kasa NPA, Dakta Abubakar Dantsoho, ya bukaci da a yi nazari kan wanzar da tsarin tashoshin Jiragen Ruwa kasa da kasa da samar da kayan tabbatar da tsaro ISPS, musamman domin a kara samarwa da fannin tsaron da ya kamata.

Abubakar ya yi wannan kiran ne, a jawabinsa a taron kasa na 2024 da kungiyar jami’an ma’aikata a Tashoshin Jirage Ruwa ta kasa wato SOFN.

  • Harajin “VAT” Zai Kara Wa Al’ummar Kasar Nan Kuncin Rayuwa Ne Kawai – Gambo Danpass
  • An Jinjina Wa Tawagar NPA Kan Samun Nasarar Sayar Da Danyen Mai Da Takardar Naira

Ya yi nuni da cewa, yin nazarin zai tabbatar da samar da wadataccen tsaro, musamman ta hanyar samar da kayan zamani na wanzar da tsaro, a daukacin tashoshin Jiragen Ruwa na kasar.

“A yayin da muke yin dubi da shekarun baya, ya kamata mu san gudunmawar da samar da tsaro ke bayawa a tekunan kasar nan, musamman domin a samu damar gudanar da hada-hadar kasuwanci na kasa da kasa tare da kuma tabbatar da, ana samar da kariya ga direbon Jiragen ruwa da kuma ma’aikatan da ke aiki a tashoshin Jiragen ruwa, “ inji shi.

Ya sanar da tsarin na ISPS Code wanda ya fara aiki gadan-gadan 2004, zai taimaka wajen kara samar da tsaro a tashoshin Jiragen ruwan kasar da kuma dakile dukkan wata barazana ta rashin tsaro a fannin.

Labarai Masu Nasaba

UNICEF Na Neman Naira Biliyan 240 Don Ayyukan Agaji A Nijeriya

Ɓarayin Waya Sun Hallaka Ɗalibin ATAP A Bauchi

A cewarsa, “Ga Nijeriya, tamkar kira ne na fara zuba hannun jari domin a kara habaka tsarin, wanda bai kawai bayar da kariya ga tashoshin Jiragen ruwan kasar ba, amma a kara kare martabar kasar mu, wacce take ita ce, uwa maba da mama, ga sauran kasashen da ke a cikin Afirka.

Ya sanar da cewa, shirye-shiyen wanzar da tsarin na ISPS Code 2020 a duniya, ya fuskance kalubale wanda suka hada da; ayyukan ta’addanci, ‘yan fashin teku, safarar haramtattun kaya da sauransu

Sai dai, Dantsoho ya sanar da cewa, yanu duniya na sauya wa ne, wanda hakan ya sanya hukumar ta NPA, ta gay a kamata ta rungumi tsarin na ISPS Code, tare da kuma wanzar dashi, gadan-gadan.

Dantsoho ya ci gaba da cewa, a namu bangaren a hukumar, muna bukatar sama da sauyi, wanda hakan ya sanya muka sabunta kayan aiki, musamman samar da kayan aiki na kimiyyar zamani, ana kuma kara samun masu zuba hannun jari da horar da jami’an tsaron mu, domin dakile dauk wata barazana da za ta iya kunno kai.

Ya sanar da cewa, hukumar tare da  hukumomin Gwamnatin Tarayya da na jihohi, masu kula da kayan aiki a tashoshin Jiragen ruwan kasar da kuma aboan hadakar mu na kasa da kasa, suna gudanar da aiki, kafada da kafada domin kara tabbatar da tsaro a fannin.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: Gwarinpa
ShareTweetSendShare
Previous Post

Manyan Batutuwa 10 Da Suka Mamaye Siyasar Nijeriya A 2024

Next Post

Alhaji Amadu Umar Ya Zama Sarkin Hausawan Garin Agbara A Jihar Ogun

Related

UNICEF Na Neman Naira Biliyan 240 Don Ayyukan Agaji A Nijeriya
Labarai

UNICEF Na Neman Naira Biliyan 240 Don Ayyukan Agaji A Nijeriya

7 hours ago
Ɓarayin Waya Sun Hallaka Ɗalibin ATAP A Bauchi
Labarai

Ɓarayin Waya Sun Hallaka Ɗalibin ATAP A Bauchi

8 hours ago
JAMB Ta Kaddamar Da Kwamitin Bincike Kan Satar Jarabawa
Labarai

JAMB Ta Kaddamar Da Kwamitin Bincike Kan Satar Jarabawa

8 hours ago
Raguwar Hauhawar Farashi: ‘Yan Nijeriya Da ‘Yan Kasuwa Ba Su Ga Saukin A Zahirance Ba
Labarai

Raguwar Hauhawar Farashi: ‘Yan Nijeriya Da ‘Yan Kasuwa Ba Su Ga Saukin A Zahirance Ba

9 hours ago
Mahara Sun Kai Hari Banki A Kogi
Manyan Labarai

’Yansanda Sun Kama Jagororin ‘Yan Bindiga A Abuja, Sun Ƙwato Makamai Da ₦7.4m

12 hours ago
Likitoci Sun Gano Wuka Da Aka Burma A Kirjin Wani Mutum Tsawon Shekara 8 
Labarai

Likitoci Sun Gano Wuka Da Aka Burma A Kirjin Wani Mutum Tsawon Shekara 8 

12 hours ago
Next Post
Alhaji Amadu Umar Ya Zama Sarkin Hausawan Garin Agbara A Jihar Ogun

Alhaji Amadu Umar Ya Zama Sarkin Hausawan Garin Agbara A Jihar Ogun

LABARAI MASU NASABA

Wajibi Ne Sassan Kasa Da Kasa Su Raya Ruhin Jin Kan Bil’adama

Wajibi Ne Sassan Kasa Da Kasa Su Raya Ruhin Jin Kan Bil’adama

August 22, 2025
UNICEF Na Neman Naira Biliyan 240 Don Ayyukan Agaji A Nijeriya

UNICEF Na Neman Naira Biliyan 240 Don Ayyukan Agaji A Nijeriya

August 22, 2025
Sin Ta Samu Karin Kamfanoni Kusan Miliyan 20 A Cikin Shirin Shekaru Biyar Karo Na 14

Sin Ta Samu Karin Kamfanoni Kusan Miliyan 20 A Cikin Shirin Shekaru Biyar Karo Na 14

August 22, 2025
Ɓarayin Waya Sun Hallaka Ɗalibin ATAP A Bauchi

Ɓarayin Waya Sun Hallaka Ɗalibin ATAP A Bauchi

August 22, 2025
JAMB Ta Kaddamar Da Kwamitin Bincike Kan Satar Jarabawa

JAMB Ta Kaddamar Da Kwamitin Bincike Kan Satar Jarabawa

August 22, 2025
Wadanda Suka Mutu A Wani Hadarin Ginin Gada A Sin Sun Karu Zuwa 12

Wadanda Suka Mutu A Wani Hadarin Ginin Gada A Sin Sun Karu Zuwa 12

August 22, 2025
Raguwar Hauhawar Farashi: ‘Yan Nijeriya Da ‘Yan Kasuwa Ba Su Ga Saukin A Zahirance Ba

Raguwar Hauhawar Farashi: ‘Yan Nijeriya Da ‘Yan Kasuwa Ba Su Ga Saukin A Zahirance Ba

August 22, 2025
Kamfanin Novo Nordisk Na Denmark Zai Ci Gaba Da Zuba Jari A Kasar Sin A Bana

Kamfanin Novo Nordisk Na Denmark Zai Ci Gaba Da Zuba Jari A Kasar Sin A Bana

August 22, 2025
Xi Jinping Zai Halarci Taron Kolin SCO Na 2025

Xi Jinping Zai Halarci Taron Kolin SCO Na 2025

August 22, 2025
Ruben Dias Ya Rattaba Hannu Kan Sabon Kwantiragi A Manchester City

Ruben Dias Ya Rattaba Hannu Kan Sabon Kwantiragi A Manchester City

August 22, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.