• English
  • Business News
Thursday, May 15, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Onoja Da Asuku Sun Janye Daga Takarar Gwamnan Kogi, Yahaya Bello Ya Zabi Ododo A Matsayin Magajinsa

by Sadiq
2 years ago
in Manyan Labarai
0
Onoja Da Asuku Sun Janye Daga Takarar Gwamnan Kogi, Yahaya Bello Ya Zabi Ododo A Matsayin Magajinsa
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Gabanin shiga zaben fidda gwanin jam’iyyar APC a Jihar Kogi, mataimakin gwamnan jihar, Edward Onoja, da shugaban ma’aikatan gwamnatin Jihar, Mohammed Abdulkareem Asuku, sun janye daga neman takarar gwamnan jihar.

LEADERSHIP ta ruwaito cewa jam’iyyar APC mai mulki ta tsayar da zaben fidda gwani na takarar gwamna a ranar Juma’a 14 ga watan Afrilu, 2023.

  • Mun Shirya Shiga Zaben Da Za A Sake A Adamawa —PDP
  • Bayern Munich Ta Dakatar Da Sadio Mane

Matakin nasu na zuwa ne bayan wani muhimmin taron masu ruwa da tsaki da gwamnan jihar, Yahaya Bello ya shirya a hedikwatar jam’iyyar APC da ke Lokoja, babban birnin jihar a ranar Alhamis, inda gwamnan ya bayyana dan takarar da yake so.

An tattaro cewa gwamna Bello ya zabi tsohon babban mai binciken kudi na jihar, Alhaji Ahmed Usman Ododo, a matsayin wanda zai gaje shi.

A halin da ake ciki, Onoja da Asuku sun sanar da janyewarsu daga takarar gwamnan a shafukansu na Facebook jim kadan bayan kammala taron.

Labarai Masu Nasaba

ASUU Ta Yi Barazanar Maka JAMB A Kotu Biyo Bayan Samun Mummunan Sakamako A UTME

JAMB: Tangarɗar Na’ura Ne Ya Haifar Da Gagarumar Koma Baya A Sakamakon UTME Na 2025

Mataimakin gwamnan, Onoja, wanda mutane da yawa suka yi tunanin zai gaji Gwamna Bello a baya, ya wallafa wani sako a shafin Facebook, wanda ke cewa: “Allah ya kara daukaka ga rayuwa da lafiya. Ina godiya ga shugabana, Alhaji Yahaya Bello da dukkan magoya bayana saboda soyayya da addu’o’inku, hakuri da juriya, ina mai godiya har abada.”

A nasa bangaren, shugaban ma’aikatan gwamnan, Asuku, wanda kuma ake ganin yana kan gaba saboda kusancinsa da gwamnan, ya wallafa nasa jawabin kamar haka: “Alhamdulillah!
Dukkan yabo da yabo sun tabbata ga Allah madaukakin sarki mafi daukakar halittu baki daya kuma wanda ya kiyaye rayuwata da ta dangina da masoyana da su shaida wannan lokaci a rayuwata. Ina matukar godiya ga mai girma Gwamna, bisa dukkan abin da Allah Ya yi amfani da shi wajen aikatawa a rayuwata. Don haka nake mika kaina a bainar jama’a ga hukuncin da aka yanke a yau kuma zan ci gaba da kasancewa da aminci da sadaukar da kai ga jam’iyyata ta APC wajen samun nasara a zaben da za a yi a nan gaba.”

A wani lamari makamancin haka, sauran masu neman takara kamar Mista David Adebanji Jimoh; tsohon kwamishinan kudi, Asiwaju Ashiru Idris; Okala Yakubu, da Momoh Jubril su ma sun janye daga neman takarar gwamna.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: APCKogiTakarar GwamnaYahaya BelloZaben Fidda Gwani
ShareTweetSendShare
Previous Post

Mun Shirya Shiga Zaben Da Za A Sake A Adamawa —PDP

Next Post

Wariyar Launin Fata Da Amfani Da Makamai Barkatai Ne Ke Rura Wutar Harbe-Harben Kan Mai Tsautsayi A Amurka

Related

UTME
Manyan Labarai

ASUU Ta Yi Barazanar Maka JAMB A Kotu Biyo Bayan Samun Mummunan Sakamako A UTME

1 hour ago
JAMB Ta Amince Da Maki 140 Da 100 Mafi Karancin Maki Na Shiga Manyan Makarantu
Manyan Labarai

JAMB: Tangarɗar Na’ura Ne Ya Haifar Da Gagarumar Koma Baya A Sakamakon UTME Na 2025

7 hours ago
Tattalin Arziƙin Nijeriya Ya Bunƙasa, Amma Farashin Kayayyaki Na Ci Gaba Da Tashi – Bankin Duniya
Manyan Labarai

Tattalin Arziƙin Nijeriya Ya Bunƙasa, Amma Farashin Kayayyaki Na Ci Gaba Da Tashi – Bankin Duniya

12 hours ago
Sojoji 20 Sun Ɓace Bayan Harin Da ISWAP Suka Kai Marte
Manyan Labarai

Sojoji 20 Sun Ɓace Bayan Harin Da ISWAP Suka Kai Marte

16 hours ago
Ko Kanawa Za Su Yafe Wa Ganduje?
Manyan Labarai

Kotu Ta Ce Za A Ci Gaba Da Shari’ar Ganduje Kan Zargin Aikata Rashawa A Kano

17 hours ago
Gwamnan Zamfara Ya Raba Katin ATM Ga Mutane 400,000 Da Suka Ci Gajiyar Shirin ‘Cash Transfer’ A Jihar
Manyan Labarai

Gwamnan Zamfara Ya Raba Katin ATM Ga Mutane 400,000 Da Suka Ci Gajiyar Shirin ‘Cash Transfer’ A Jihar

1 day ago
Next Post
Wariyar Launin Fata Da Amfani Da Makamai Barkatai Ne Ke Rura Wutar Harbe-Harben Kan Mai Tsautsayi A Amurka

Wariyar Launin Fata Da Amfani Da Makamai Barkatai Ne Ke Rura Wutar Harbe-Harben Kan Mai Tsautsayi A Amurka

LABARAI MASU NASABA

UTME

ASUU Ta Yi Barazanar Maka JAMB A Kotu Biyo Bayan Samun Mummunan Sakamako A UTME

May 14, 2025
Xi Jinping Ya Gana Da Takwarorinsa Na Kasashen Colombia Da Chile

Xi Jinping Ya Gana Da Takwarorinsa Na Kasashen Colombia Da Chile

May 14, 2025
Gwamnatin Tarayya Da Majalisar Dokoki Za Su Haɗa  Gwiwa Kan Sake Duba Dokar Laifukan Intanet — Minista

Gwamnatin Tarayya Da Majalisar Dokoki Za Su Haɗa  Gwiwa Kan Sake Duba Dokar Laifukan Intanet — Minista

May 14, 2025
Yadda Kasar Sin Ke Kokarin Gina Tashar Bincike A Sama Da Tubalin Kasar Duniyar Wata

Yadda Kasar Sin Ke Kokarin Gina Tashar Bincike A Sama Da Tubalin Kasar Duniyar Wata

May 14, 2025
gaza

Kasafin Kudi Na Naira Tiriliyan 1.78 Na Abuja Ya Tsallake Karatu Na Biyu A Majalisa

May 14, 2025
Kasar Sin Za Ta Inganta Cikakken Tsarin Fitar Da Ma’adanai Zuwa Ketare Don Kiyaye Tsaron Kasa

Kasar Sin Za Ta Inganta Cikakken Tsarin Fitar Da Ma’adanai Zuwa Ketare Don Kiyaye Tsaron Kasa

May 14, 2025
Tinubu Ya Yaba Wa Sule Lamiɗo A Taron Ƙaddamar Da Littafin Tarihin Rayuwasa

Tinubu Ya Yaba Wa Sule Lamiɗo A Taron Ƙaddamar Da Littafin Tarihin Rayuwasa

May 14, 2025
Manyan Ayyuka Guda Biyar Za Su Raya Makomar Al’ummomin Kasar Sin Da kasashen Latin Amurka Da Caribbean Ta Bai Daya

Manyan Ayyuka Guda Biyar Za Su Raya Makomar Al’ummomin Kasar Sin Da kasashen Latin Amurka Da Caribbean Ta Bai Daya

May 14, 2025
Yadda Aka Gina Ofishin ‘Yansanda Na Zamani A Abuja

Yadda Aka Gina Ofishin ‘Yansanda Na Zamani A Abuja

May 14, 2025
JAMB Ta Amince Da Maki 140 Da 100 Mafi Karancin Maki Na Shiga Manyan Makarantu

JAMB: Tangarɗar Na’ura Ne Ya Haifar Da Gagarumar Koma Baya A Sakamakon UTME Na 2025

May 14, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.