• English
  • Business News
Tuesday, October 7, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Onoja Da Asuku Sun Janye Daga Takarar Gwamnan Kogi, Yahaya Bello Ya Zabi Ododo A Matsayin Magajinsa

bySadiq
2 years ago
inManyan Labarai
0
Onoja Da Asuku Sun Janye Daga Takarar Gwamnan Kogi, Yahaya Bello Ya Zabi Ododo A Matsayin Magajinsa

Gabanin shiga zaben fidda gwanin jam’iyyar APC a Jihar Kogi, mataimakin gwamnan jihar, Edward Onoja, da shugaban ma’aikatan gwamnatin Jihar, Mohammed Abdulkareem Asuku, sun janye daga neman takarar gwamnan jihar.

LEADERSHIP ta ruwaito cewa jam’iyyar APC mai mulki ta tsayar da zaben fidda gwani na takarar gwamna a ranar Juma’a 14 ga watan Afrilu, 2023.

  • Mun Shirya Shiga Zaben Da Za A Sake A Adamawa —PDP
  • Bayern Munich Ta Dakatar Da Sadio Mane

Matakin nasu na zuwa ne bayan wani muhimmin taron masu ruwa da tsaki da gwamnan jihar, Yahaya Bello ya shirya a hedikwatar jam’iyyar APC da ke Lokoja, babban birnin jihar a ranar Alhamis, inda gwamnan ya bayyana dan takarar da yake so.

An tattaro cewa gwamna Bello ya zabi tsohon babban mai binciken kudi na jihar, Alhaji Ahmed Usman Ododo, a matsayin wanda zai gaje shi.

A halin da ake ciki, Onoja da Asuku sun sanar da janyewarsu daga takarar gwamnan a shafukansu na Facebook jim kadan bayan kammala taron.

Labarai Masu Nasaba

Kada Ku Yi Sanadiyar Rugujewar Matatar Mai Ta Dangote – Shettima Ga PENGASSAN 

Talaucin Da Ya Ninku Fiye Da Sau Biyu A Gwamnatin Tinubu, An Ƙuduri Aniyar Kawar Da Shi Nan Da Shekaru 5

Mataimakin gwamnan, Onoja, wanda mutane da yawa suka yi tunanin zai gaji Gwamna Bello a baya, ya wallafa wani sako a shafin Facebook, wanda ke cewa: “Allah ya kara daukaka ga rayuwa da lafiya. Ina godiya ga shugabana, Alhaji Yahaya Bello da dukkan magoya bayana saboda soyayya da addu’o’inku, hakuri da juriya, ina mai godiya har abada.”

A nasa bangaren, shugaban ma’aikatan gwamnan, Asuku, wanda kuma ake ganin yana kan gaba saboda kusancinsa da gwamnan, ya wallafa nasa jawabin kamar haka: “Alhamdulillah!
Dukkan yabo da yabo sun tabbata ga Allah madaukakin sarki mafi daukakar halittu baki daya kuma wanda ya kiyaye rayuwata da ta dangina da masoyana da su shaida wannan lokaci a rayuwata. Ina matukar godiya ga mai girma Gwamna, bisa dukkan abin da Allah Ya yi amfani da shi wajen aikatawa a rayuwata. Don haka nake mika kaina a bainar jama’a ga hukuncin da aka yanke a yau kuma zan ci gaba da kasancewa da aminci da sadaukar da kai ga jam’iyyata ta APC wajen samun nasara a zaben da za a yi a nan gaba.”

A wani lamari makamancin haka, sauran masu neman takara kamar Mista David Adebanji Jimoh; tsohon kwamishinan kudi, Asiwaju Ashiru Idris; Okala Yakubu, da Momoh Jubril su ma sun janye daga neman takarar gwamna.

Tags: APCKogiTakarar GwamnaYahaya BelloZaben Fidda Gwani
ShareTweetSendShare
Sadiq

Sadiq

Related

Kada Ku Yi Sanadiyar Rugujewar Matatar Mai Ta Dangote – Shettima Ga PENGASSAN 
Manyan Labarai

Kada Ku Yi Sanadiyar Rugujewar Matatar Mai Ta Dangote – Shettima Ga PENGASSAN 

12 hours ago
Tinubu
Manyan Labarai

Talaucin Da Ya Ninku Fiye Da Sau Biyu A Gwamnatin Tinubu, An Ƙuduri Aniyar Kawar Da Shi Nan Da Shekaru 5

16 hours ago
Uba Sani Ya Amince Da Biyan Naira Biliyan ₦2.3 Ga Tsofaffin Ma’aikata Da Iyalansu
Manyan Labarai

Uba Sani Ya Amince Da Biyan Naira Biliyan ₦2.3 Ga Tsofaffin Ma’aikata Da Iyalansu

23 hours ago
Next Post
Wariyar Launin Fata Da Amfani Da Makamai Barkatai Ne Ke Rura Wutar Harbe-Harben Kan Mai Tsautsayi A Amurka

Wariyar Launin Fata Da Amfani Da Makamai Barkatai Ne Ke Rura Wutar Harbe-Harben Kan Mai Tsautsayi A Amurka

LABARAI MASU NASABA

Kotu Ta Aike Da Ɗan TikTok Gidan Gyaran Hali Kan Bidiyon Batsa A Kano

Kotu Ta Aike Da Ɗan TikTok Gidan Gyaran Hali Kan Bidiyon Batsa A Kano

October 6, 2025
Kada Ku Yi Sanadiyar Rugujewar Matatar Mai Ta Dangote – Shettima Ga PENGASSAN 

Kada Ku Yi Sanadiyar Rugujewar Matatar Mai Ta Dangote – Shettima Ga PENGASSAN 

October 6, 2025
Habakar Yin Sayayya A Lokacin Hutu Ta Nuna Kirkira Da Irin Ci Gaban Da Tattalin Arzikin Kasar Sin Ke Samu   

Habakar Yin Sayayya A Lokacin Hutu Ta Nuna Kirkira Da Irin Ci Gaban Da Tattalin Arzikin Kasar Sin Ke Samu   

October 6, 2025
Karamin Ofishin Jakadancin Sin Da Ke Legas Ya Yi Bikin Bunkasa Al’adu Na Bikin Tsakiyar Kaka

Karamin Ofishin Jakadancin Sin Da Ke Legas Ya Yi Bikin Bunkasa Al’adu Na Bikin Tsakiyar Kaka

October 6, 2025
Minista Nnaji Ya Yi Ƙarar Jami’ar UNN Kan Rikicin Takardun Kammala Makaranta

Minista Nnaji Ya Yi Ƙarar Jami’ar UNN Kan Rikicin Takardun Kammala Makaranta

October 6, 2025
Nazari Ya Gano Falalen Dutse Na Yanki Mai Nisa A Duniyar Wata Ya Fi Tsananin Sanyi Fiye Da Na Yanki Na Kusa

Nazari Ya Gano Falalen Dutse Na Yanki Mai Nisa A Duniyar Wata Ya Fi Tsananin Sanyi Fiye Da Na Yanki Na Kusa

October 6, 2025
Yanzu-Yanzu: Kwara United Ta Sallami Kocinta, Tunde Sanni

Yanzu-Yanzu: Kwara United Ta Sallami Kocinta, Tunde Sanni

October 6, 2025
Tinubu

Talaucin Da Ya Ninku Fiye Da Sau Biyu A Gwamnatin Tinubu, An Ƙuduri Aniyar Kawar Da Shi Nan Da Shekaru 5

October 6, 2025
Yadda Rashin Isassun Malaman Turanci Da Lissafi Ke Shafar Ingancin Ilimi A Nijeriya (3)

TRCN Ta Koka Kan Yawaitar Malaman Da Ba Su Cancanta Ba A Nijeriya 

October 6, 2025
Rwanda Da Huawei Sun Kaddamar Da Shirin DigiTruck Domin Bunkasa Fasaha A Fadin Kasar

Rwanda Da Huawei Sun Kaddamar Da Shirin DigiTruck Domin Bunkasa Fasaha A Fadin Kasar

October 6, 2025

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.