ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Friday, July 17, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Onoja Da Asuku Sun Janye Daga Takarar Gwamnan Kogi, Yahaya Bello Ya Zabi Ododo A Matsayin Magajinsa

by Sadiq
3 years ago
Kogi

Gabanin shiga zaben fidda gwanin jam’iyyar APC a Jihar Kogi, mataimakin gwamnan jihar, Edward Onoja, da shugaban ma’aikatan gwamnatin Jihar, Mohammed Abdulkareem Asuku, sun janye daga neman takarar gwamnan jihar.

LEADERSHIP ta ruwaito cewa jam’iyyar APC mai mulki ta tsayar da zaben fidda gwani na takarar gwamna a ranar Juma’a 14 ga watan Afrilu, 2023.

  • Mun Shirya Shiga Zaben Da Za A Sake A Adamawa —PDP
  • Bayern Munich Ta Dakatar Da Sadio Mane

Matakin nasu na zuwa ne bayan wani muhimmin taron masu ruwa da tsaki da gwamnan jihar, Yahaya Bello ya shirya a hedikwatar jam’iyyar APC da ke Lokoja, babban birnin jihar a ranar Alhamis, inda gwamnan ya bayyana dan takarar da yake so.

ADVERTISEMENT

An tattaro cewa gwamna Bello ya zabi tsohon babban mai binciken kudi na jihar, Alhaji Ahmed Usman Ododo, a matsayin wanda zai gaje shi.

A halin da ake ciki, Onoja da Asuku sun sanar da janyewarsu daga takarar gwamnan a shafukansu na Facebook jim kadan bayan kammala taron.

LABARAI MASU NASABA

Mutfwang Ya Buƙaci Sojoji Su Ƙara Ƙaimi A Aikinsu

Ba Zan Iya Jure Halayen El-Rufai Ba Shi Yasa Na Fice Daga ADC – Salihu Lukman

Mataimakin gwamnan, Onoja, wanda mutane da yawa suka yi tunanin zai gaji Gwamna Bello a baya, ya wallafa wani sako a shafin Facebook, wanda ke cewa: “Allah ya kara daukaka ga rayuwa da lafiya. Ina godiya ga shugabana, Alhaji Yahaya Bello da dukkan magoya bayana saboda soyayya da addu’o’inku, hakuri da juriya, ina mai godiya har abada.”

A nasa bangaren, shugaban ma’aikatan gwamnan, Asuku, wanda kuma ake ganin yana kan gaba saboda kusancinsa da gwamnan, ya wallafa nasa jawabin kamar haka: “Alhamdulillah!
Dukkan yabo da yabo sun tabbata ga Allah madaukakin sarki mafi daukakar halittu baki daya kuma wanda ya kiyaye rayuwata da ta dangina da masoyana da su shaida wannan lokaci a rayuwata. Ina matukar godiya ga mai girma Gwamna, bisa dukkan abin da Allah Ya yi amfani da shi wajen aikatawa a rayuwata. Don haka nake mika kaina a bainar jama’a ga hukuncin da aka yanke a yau kuma zan ci gaba da kasancewa da aminci da sadaukar da kai ga jam’iyyata ta APC wajen samun nasara a zaben da za a yi a nan gaba.”

A wani lamari makamancin haka, sauran masu neman takara kamar Mista David Adebanji Jimoh; tsohon kwamishinan kudi, Asiwaju Ashiru Idris; Okala Yakubu, da Momoh Jubril su ma sun janye daga neman takarar gwamna.

MASU ALAKA

Mutfwang Ya Buƙaci Sojoji Su Ƙara Ƙaimi A Aikinsu
Manyan Labarai

Mutfwang Ya Buƙaci Sojoji Su Ƙara Ƙaimi A Aikinsu

July 16, 2026
Gwamnatin Tarayya Na Biyan Tallafin Man Fetur A Asirce – El-Rufai
Siyasa

Ba Zan Iya Jure Halayen El-Rufai Ba Shi Yasa Na Fice Daga ADC – Salihu Lukman

July 16, 2026
M.A. Abubakar Ya Zaɓi Farouk Mustapha A Matsayin  Mataimakinsa
Manyan Labarai

M.A. Abubakar Ya Zaɓi Farouk Mustapha A Matsayin Mataimakinsa

July 16, 2026
Next Post
Wariyar Launin Fata Da Amfani Da Makamai Barkatai Ne Ke Rura Wutar Harbe-Harben Kan Mai Tsautsayi A Amurka

Wariyar Launin Fata Da Amfani Da Makamai Barkatai Ne Ke Rura Wutar Harbe-Harben Kan Mai Tsautsayi A Amurka

LABARAI MASU NASABA

Pew: Sin Ta fi Amurka Samun Amincewar Al’ummun Duniya

Pew: Sin Ta fi Amurka Samun Amincewar Al’ummun Duniya

July 16, 2026
Sin Ta Fitar Da Tsarin Sanya Ido Don Inganta Muhalli Da Muhallin Halittu Na Shekarar 2026 Zuwa 2030

Sin Ta Fitar Da Tsarin Sanya Ido Don Inganta Muhalli Da Muhallin Halittu Na Shekarar 2026 Zuwa 2030

July 16, 2026
Nazari Game Da Damammakin Da Sin Ta Samar Cikin Rahoton Ci Gaban Tattalin Arzikinta Na Rabin Farkon Shekara

Nazari Game Da Damammakin Da Sin Ta Samar Cikin Rahoton Ci Gaban Tattalin Arzikinta Na Rabin Farkon Shekara

July 16, 2026
Gwamna Bala Ya Rushe Kwamitin Gudanarwar Wikki Tourists Bayan Rashin Nasararta A Gasar NPFL

Gwamna Bala Ya Rushe Kwamitin Gudanarwar Wikki Tourists Bayan Rashin Nasararta A Gasar NPFL

July 16, 2026
Tasirin Da Sabbin Hare-haren Amurka Da Iran Za Su Iya Haifarwa Duniya

Tasirin Da Sabbin Hare-haren Amurka Da Iran Za Su Iya Haifarwa Duniya

July 16, 2026
Sin Na Kokarin Sanya Ci Gaban Fasaha Ya Inganta Bunkasa Da Wadatar Dan Adam

Sin Na Kokarin Sanya Ci Gaban Fasaha Ya Inganta Bunkasa Da Wadatar Dan Adam

July 16, 2026
Tinubu Ya Miƙa Wa Shettima Takardar Tabbatar Da Shi Abokin Takararsa A Zaɓen 2027

Tinubu Ya Miƙa Wa Shettima Takardar Tabbatar Da Shi Abokin Takararsa A Zaɓen 2027

July 16, 2026
Xi Jinping Ya Gana Da Shugaban Kazakhstan

Xi Jinping Ya Gana Da Shugaban Kazakhstan

July 16, 2026
Mutfwang Ya Buƙaci Sojoji Su Ƙara Ƙaimi A Aikinsu

Mutfwang Ya Buƙaci Sojoji Su Ƙara Ƙaimi A Aikinsu

July 16, 2026
An Yi Bikin Rattaba Hannu Kan Yarjejeniyar Kafa Kungiyar Hadin Gwiwar Fasahar AI Ta Duniya A Shanghai

An Yi Bikin Rattaba Hannu Kan Yarjejeniyar Kafa Kungiyar Hadin Gwiwar Fasahar AI Ta Duniya A Shanghai

July 16, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.