• English
  • Business News
Tuesday, June 17, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

PDP Ta Fito Da Sabon Salon Yakin Neman Zabe A Sakkwato

by Sharfaddeen Sidi Umar, Sokoto
3 years ago
in Siyasa
0
PDP Ta Fito Da Sabon Salon Yakin Neman Zabe A Sakkwato
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Babba jigo a kwamitin yakin neman zaben Jam’iyyar PDP a Jihar Sakkwato, Honarabul Aminu Bala Bodinga ya bayyana cewar jam’iyyar a Jihar ta fito da sabon salon yakin neman zabe ne domin kawar da matsaloli da kalubalen da jam’iyyar ke fuskanta domin samun nasarar Babban Zaben 2023.

  • An Tsige Shugaban Jam’iyyar NNPP A Kaduna

Honarabul Aminu Bala wanda kuma shine Kwamishinan Filaye da Gidaje ya bayyana cewar sabon salon yakin neman zabe da suka bullo da shi mai tasiri ne da alfanu ga jam’iyyar PDP da al’ummar Jihar Sakkwato bakidaya.

Jigon dan siyasar ya bayyana hakan ne a yau a tattaunawarsa da manema labarai a wajen ci- gaba da taron masu ruwa da tsaki da jam’iyyar PDP ke gudanarwa da Karamar Hukumar Gudu a otel din Giginya.

Ya ce sabon salo ne suka fito da shi domin zama da kowace Karamar Hukuma a tattauna ido da ido a baje siyasa da matsalolinta a faifai akasin yadda ake yi a can baya. Ya ce a yanzu su kan zauna da dukkanin masu ruwa da tsaki a lamurran jam’iyya, a saurari matsaloli ta yadda wadanda ake iya gyarawa a gyara kai tsaye wadanda kuma ake alkawali sai a dauki alkawali zuwa bayan zabe.

Ya ce wani muhimmin lamari shine ko da akwai ‘ya’yan jam’iyya wadanda ke da sabani da juna, ba za a kammala taron ba sai an daidata su an fahimci juna, don haka ya bayyana cewar muhimmancin taron ya fi gaban a nanata.

Labarai Masu Nasaba

Dalilin Mara Wa Tinubu Baya Ba Tare da Ambaton Shettima Ba – Shugaban APC Na Arewa Maso Gabas

APCn Kaduna Ta Mara Wa Tinubu, Uba Sani Da Kakakin Majalisa Abbas Baya Don Wa’adi Na Biyu

“Tarukan da ake zuwa yakin neman zabe a Kananan Hukumomi shugabanni ne kawai ke samun damar magana ba tare da bayar da dama ga dukkanin jama’a su samu damar cewa wani abu ba, ko gabatar da korafi ba saboda rashin lokaci amma a wannan taron na masu ruwa da tsaki, akwai cikakken lokaci da damar sauraren kowa da kowa.” Ya bayyana.

“Misali a yanzu Karamar Hukumar Gudu ce muke zama da ita, kuma zaben 2019 da ya gabata mun samu gagarumar nasara a Gudu 100%, don haka a wannan zaben ma akalla muna son ka da mu kasa samun kashi 90% in sha Allah.”

A taron wanda Shugaban Kwamitin Yakin Neman Zaben PDP a Jihar, Tsohon Ministan Sufuri, Honarabul Yusuf Sulaiman ya jagoranta ya bayyana za su aiwatar da kakkarfan kamfen din da zai tabbatar da samun nasarar jam’iyyar PDP a dukkanin matakai daga sama har kasa bakidaya.

A jawabinsa Mataimakin Dan Takarar Gwamnan Jihar Sakkwato, Honarabul Sagir Bafarawa ya bayyana cewar Karamar Hukumar Gudu ta jam’iyyar PDP ce gaba da baya don haka ba su da shakku a kan ta.

“Gudu ko kadan ba wajen zuwan APC ba ne, al’ummar Gudu bakidaya PDP suke yi domin ita ce jam’iyyar da suka yi amannar za ta rika kawar da matsalolin su da inganta jin dadin su.”


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

ShareTweetSendShare
Previous Post

An Tsige Shugaban Jam’iyyar NNPP A Kaduna

Next Post

‘Yan Daba Sun Raunata Soja Da ‘Yan Kwana-Kwana 2 Yayin Da Gobara Ta Tashi A Gidan Mai A Kwara

Related

Sirikin Buhari Ya Fice Daga Jam’iyyar APC A Kaduna
Manyan Labarai

Dalilin Mara Wa Tinubu Baya Ba Tare da Ambaton Shettima Ba – Shugaban APC Na Arewa Maso Gabas

8 hours ago
APCn Kaduna Ta Mara Wa Tinubu, Uba Sani Da Kakakin Majalisa Abbas Baya Don Wa’adi Na Biyu
Siyasa

APCn Kaduna Ta Mara Wa Tinubu, Uba Sani Da Kakakin Majalisa Abbas Baya Don Wa’adi Na Biyu

2 days ago
Gwamnatin Kano Ta Ƙaryata Karɓo Bashin Dala Miliyan 6.6
Labarai

Gwamnatin Kano Ta Ƙaryata Karɓo Bashin Dala Miliyan 6.6

4 days ago
Zamfara: APC Za Ta Maka PDP A Kotu Kan Zargin Matawalle Da Hannu A Satar Mutane
Manyan Labarai

Zamfara: APC Za Ta Maka PDP A Kotu Kan Zargin Matawalle Da Hannu A Satar Mutane

5 days ago
A Bai Wa Kudu Tikitin Takara A 2027 Ko PDP Ta Ruguje – Wani Jigo A PDP
Siyasa

A Bai Wa Kudu Tikitin Takara A 2027 Ko PDP Ta Ruguje – Wani Jigo A PDP

6 days ago
Shehu Sani Ya Buƙaci Shugabannin Arewa Su Mara Wa Tinubu Baya Ya Yi Shekaru 8 A Kan Mulki
Manyan Labarai

Shehu Sani Ya Buƙaci Shugabannin Arewa Su Mara Wa Tinubu Baya Ya Yi Shekaru 8 A Kan Mulki

2 weeks ago
Next Post
‘Yan Daba Sun Raunata Soja Da ‘Yan Kwana-Kwana 2 Yayin Da Gobara Ta Tashi A Gidan Mai A Kwara

'Yan Daba Sun Raunata Soja Da ‘Yan Kwana-Kwana 2 Yayin Da Gobara Ta Tashi A Gidan Mai A Kwara

LABARAI MASU NASABA

Kaftin Din Super Eagles, Ahmed Musa Ya Bukaci A Gaggauta Kawo Karshen Kashe-kashen Rayuka A Benuwe

Kaftin Din Super Eagles, Ahmed Musa Ya Bukaci A Gaggauta Kawo Karshen Kashe-kashen Rayuka A Benuwe

June 17, 2025
Masu Karanta Adabin Shafin Intanet Na Sin Sun Kai Miliyan 575

Masu Karanta Adabin Shafin Intanet Na Sin Sun Kai Miliyan 575

June 17, 2025
Sin Ta Fara Aiwatar Da Matakin Soke Haraji Kan Kayayyakin Kasashen Afirka 53

Sin Ta Fara Aiwatar Da Matakin Soke Haraji Kan Kayayyakin Kasashen Afirka 53

June 17, 2025
JAMB Ta Amince Da Maki 140 Da 100 Mafi Karancin Maki Na Shiga Manyan Makarantu

2025 UTME: Cibiyoyin Zana Jarabawar 11 Na Fuskantar Barazanar Dakatarwa – JAMB

June 17, 2025
Xi Ya Gabatar Da Muhimmin Jawabi A Taron Koli Na Sin Da Kasashen Tsakiyar Asiya Karo Na Biyu

Xi Ya Gabatar Da Muhimmin Jawabi A Taron Koli Na Sin Da Kasashen Tsakiyar Asiya Karo Na Biyu

June 17, 2025
Daga Taklimakan Zuwa Sahara: Karin Abubuwan Al’ajabi Na Faruwa Bisa Hadin Gwiwar Sin Da Afirka A Fannin Yaki Da Kwararar Hamada

Daga Taklimakan Zuwa Sahara: Karin Abubuwan Al’ajabi Na Faruwa Bisa Hadin Gwiwar Sin Da Afirka A Fannin Yaki Da Kwararar Hamada

June 17, 2025
‘Yan Bindiga Sun Kashe Jami’an Tsaro 4 Da Manoma A Katsina

‘Yan Bindiga Sun Kashe Jami’an Tsaro 4 Da Manoma A Katsina

June 17, 2025
Matatar Mai ta Haifa Ta Dakatar Da Ayyukanta Bayan Harin Iran

Matatar Mai ta Haifa Ta Dakatar Da Ayyukanta Bayan Harin Iran

June 17, 2025
Sirikin Buhari Ya Fice Daga Jam’iyyar APC A Kaduna

Dalilin Mara Wa Tinubu Baya Ba Tare da Ambaton Shettima Ba – Shugaban APC Na Arewa Maso Gabas

June 17, 2025
Sabon Shirin Gwamnatin Katsina: Za A Fara Sauya Tunanin Tubabbun ‘Yan Bindiga

Sabon Shirin Gwamnatin Katsina: Za A Fara Sauya Tunanin Tubabbun ‘Yan Bindiga

June 17, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.