• English
  • Business News
Saturday, July 5, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

PDP Ta Mayar Da Martani Mai Zafi Ga APC Kan Neman Ayyana Dokar Ta-ɓaci A Zamfara

by Leadership Hausa and Sulaiman
10 months ago
in Labarai
0
PDP
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Jami’iyyar PDP a Jihar Zamfara, ta bayyana kiran da jam’iyyar APC ƙarƙashin jagorancin tsofaffin Gwamnanonin jihar, Bello Matawalle da Sanata Abdulaziz Yari suka yi na ayyana dokar ta-baci a jihar a matsayin “hassada” da ci gaban da aka samu a ƙarƙashin jagorancin Gwamna Dauda Lawal.

 

A wata sanarwa da Sakataren Yaɗa Labaran Jami’iyyar PDP na Zamfara, Halliru Andi ya fitar a ranar, 22 ga Satumba, 2024, ta ce, “Gwamnatin PDP ta mayar da hankali ne wajen gyara kura-kuran da gwamnatocin baya suka tafka na tsawon shekaru a jihar.

  • Zamfara Ta Bayar Da Gudunmawar Miliyan 100 Ga Waɗanda Ambaliya Ta Shafa a Borno 
  • Gwamnatin Zamfara Ta Tabbatar Da Mutuwar Mutane 40 A Hatsarin Kwale-kwale

“Kiran a kafa dokar ta-baci ba shi da tushe balle makama kuma rashin mutunta al’ummar jihar Zamfara ne. Jam’iyyar APC ta yi biris da abubuwan da suka shafi tsohon Gwamna Bello Matawalle, wanda rashin sanin makamar aikin sa ne ya ƙara dagula harkar tsaro a jihar.

 

Labarai Masu Nasaba

ALGON Ta Taya Gwamnan Sani Murnar Samun Lambar Yabo Ta Kasa

Kwankwaso Ba Zai Sake Yi Mana Takarar Shugabancin Ƙasa Ba A Zaɓen 2027 Ba – NNPP

“Rashin tabbatar da tsaro da gwamnatinsa ta yi ya samo asali ne yayin da ta riƙa ƙirƙirar samar wa ’yan ta’adda da wurin zama da sunan “sulhu”, ciki har da bayar da motocin Hilux da kuma tukuicin kuɗi ga ’yan bindigar, tare da ba su damar shiga gidan gwamnati kai tsaye. Wannan ya sa al’ummar Zamfara suka gamu da mugun nufi na wannan sakaci, inda ’yan bindiga ke afka wa al’umma sannan su koma su fake a bayan masu mulki.

 

“Ikirarin rashin gaskiya na cewa, Gwamna Dauda Lawal na yin zagon ƙasa a yaƙin da ake yi da ’yan bindiga a Jihar Zamfara, wani yunƙuri ne na siyasa domin kawo cikas ga ƙoƙarin da muke yi na magance matsalar rashin tsaro a jihar,” in ji sanarwar.

 

Ta ƙara da cewa, “Gwamna Lawal shi ne na farko a tarihin jiharmu da ya ba da fifiko kan harkokin tsaro tare da jajircewa na gaskiya, sabanin yadda gwamnatocin APC da suka shuɗe suka yi.

 

“Ba kamar jam’iyyar APC da ta siyasantar da matsalar rashin tsaro ba, gwamnatin PDP ta himmatu wajen tabbatar da zaman lafiya da kwanciyar hankali a jihar Zamfara. Nasarorin da muka samu a kan ‘yan bindiga sun samo asali ne daga jajircewar Gwamna Lawal, na ƙin yin sulhu da masu laifi. Wannan matsaya mai ƙarfi ta kafa tabbataccen alƙibla a yaƙinmu da ‘yan ta’addan.

 

“Gwamnatin PDP ƙarƙashin jagorancin Gwamna Dauda Lawal ta ɗauki muhimman matakai da suka haɗa da kafa Rundunar Tsaron Kare Al’umma ‘Askarawan Zamfara’ (CPG) da kuma samar da asusun kula da tsaro domin tallafawa jami’an tsaro. Makonni kaɗan da suka gabata Gwamna Lawal ya raba motoci domin inganta ayyukan hukumomin tsaro, inda ya nuna jajircewarsa kan wannan lamari mai matuƙar muhimmanci,” in ji sanarwa.

 

Sanarwar ta ce, “Zargin da APC ke yi, farfaganda ce kawai. Ko kaɗan tsohon Gwamna Matawalle bai bayyana aniyar haɗa kai da Gwamna Lawal wajen magance matsalar rashin tsaro ba. Bugu da ƙari, Matawalle, wanda yanzu shi ne ƙaramin ministan tsaro, ya nuna rashin ƙwarewa da kuma rashin tausayawa ga al’ummar Zamfara. Tattaunawar da ya yi a asirce da ’yan bindiga, ba tare da sanin Gwamna Lawal ba, kai tsaye ya ruguza tsayuwar gwamnatin da ta yi hannun riga da batun yin sulhu da ‘yan bindiga. Bayan rashin nasarar wannan tattaunawar, ya yi ikirarin ƙarya cewa Gwamna Lawal ya amince da Naira biliyan 1.3 a cikin wata takarda da aka ƙirƙira domin sulhuntawa da ’yan ta’adda, magana mara tushe.”

 

Ta ce, “Muna kira ga shugaban ƙasa Bola Ahmed Tinubu da ya kori Bello Matawalle daga muƙaminsa na ƙaramin ministan tsaro. Rashin amincinsa da rashin cancantar wannan matsayi ya bayyana ƙarara a cikin ayyukan da ya yi a baya, wanda ba kawai ya lalata yaƙin da ake yi da ‘yan binidiga a halin yanzu ba ne, har ma kawo haɗari ga lafiyar ‘yan ƙasarmu. Ya zama wajibi gwamnatin tarayya ta binciki matakan da Matawalle ya ɗauka, musamman alaƙar sa da shugabannin ’yan bindiga, waɗanda ke zama cikas ga shugabanci nagari.”

 

“A ƙarshe muna kira ga jam’iyyar APC da ta mayar da hankali kan al’amuran da suka shafi jihar Zamfara, maimakon yin tuhume-tuhume da karkatar da hankalin al’umma. Gwamna Dauda Lawal dai ya tsaya tsayin daka kan ƙudirinsa na kawo sauyi a jihar, kuma ba zai sa ya yi ƙasa a gwiwa ba da ikirarin da ‘yan adawa ke yi. Al’ummar Zamfara na buƙatar zaman lafiya, kuma wannan gwamnati ta himmatu wajen ganin ta cika wannan alƙawarin da ta ɗauka,” in ji sanarwar.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: SiyasaTa'addancin 'yan bindiga
ShareTweetSendShare
Previous Post

Kotu Ta Ba Da Belin Mawaki P Diddy Mai Safarar Mata

Next Post

An Gudanar Da Bikin Da Ya Shafi Makamashi Na Nan Gaba A Birnin New York

Related

ALGON Ta Taya Gwamnan Sani Murnar Samun Lambar Yabo Ta Kasa
Labarai

ALGON Ta Taya Gwamnan Sani Murnar Samun Lambar Yabo Ta Kasa

3 hours ago
Kwankwaso Ba Zai Sake Yi Mana Takarar Shugabancin Ƙasa Ba A Zaɓen 2027 Ba – NNPP
Manyan Labarai

Kwankwaso Ba Zai Sake Yi Mana Takarar Shugabancin Ƙasa Ba A Zaɓen 2027 Ba – NNPP

3 hours ago
An Yi Wa ‘Yar Shekara 18 Fyade Har Lahira A Taraba
Kotu Da Ɗansanda

An Kama Matashin Da Ya Yi Garkuwa Da Abokinsa Tare Da Karbar Kudin Fansa

6 hours ago
Gwamna Ademola Adeleke Ya Ƙaryata Jita-Jitar Sauya Sheƙa Daga PDP Zuwa APC
Manyan Labarai

Gwamna Ademola Adeleke Ya Ƙaryata Jita-Jitar Sauya Sheƙa Daga PDP Zuwa APC

7 hours ago
Abin Da Ya Sa ‘Yan Nijeriya Ba Su Mori Dimokuradiyya Ba Har Yanzu –Jega
Labarai

Shirin Tinubu Kan Kiwon Dabbobi Zai Samar Da Ayyukan Yi Miliyan 5 Ga Matasa – Jega

9 hours ago
‘Yan Kasuwa Na Kalubalantar Rage Faranshin Man Dangote
Labarai

‘Yan Kasuwa Na Kalubalantar Rage Faranshin Man Dangote

10 hours ago
Next Post
An Gudanar Da Bikin Da Ya Shafi Makamashi Na Nan Gaba A Birnin New York

An Gudanar Da Bikin Da Ya Shafi Makamashi Na Nan Gaba A Birnin New York

LABARAI MASU NASABA

Bukatar Ma’aurata Su Rika Bayyana Wa Junansu Gaskiyar Yanayin Samunsu

Bukatar Ma’aurata Su Rika Bayyana Wa Junansu Gaskiyar Yanayin Samunsu

July 5, 2025
Yadda Ake Gasasshen Biredi (Sandwich)

Yadda Ake Gasasshen Biredi (Sandwich)

July 5, 2025
Gyaran Jiki Da Kyawun Fata (5)

Gyaran Jiki Da Kyawun Fata (5)

July 5, 2025
ALGON Ta Taya Gwamnan Sani Murnar Samun Lambar Yabo Ta Kasa

ALGON Ta Taya Gwamnan Sani Murnar Samun Lambar Yabo Ta Kasa

July 5, 2025
Kwankwaso Ba Zai Sake Yi Mana Takarar Shugabancin Ƙasa Ba A Zaɓen 2027 Ba – NNPP

Kwankwaso Ba Zai Sake Yi Mana Takarar Shugabancin Ƙasa Ba A Zaɓen 2027 Ba – NNPP

July 5, 2025
Cututtukan Da Aka Fi Fama Da Su lokacin Damina Da Yadda Za A Kauce Musu

Cututtukan Da Aka Fi Fama Da Su lokacin Damina Da Yadda Za A Kauce Musu

July 5, 2025
Abin Da Ya Sa Ilimi Yake Da Muhimmanci Ga Rayuwar Al’umma (8)

Abin Da Ya Sa Ilimi Yake Da Muhimmanci Ga Rayuwar Al’umma (8)

July 5, 2025
An Yi Wa ‘Yar Shekara 18 Fyade Har Lahira A Taraba

An Kama Matashin Da Ya Yi Garkuwa Da Abokinsa Tare Da Karbar Kudin Fansa

July 5, 2025
Gwamna Ademola Adeleke Ya Ƙaryata Jita-Jitar Sauya Sheƙa Daga PDP Zuwa APC

Gwamna Ademola Adeleke Ya Ƙaryata Jita-Jitar Sauya Sheƙa Daga PDP Zuwa APC

July 5, 2025
Dalilin Kwararru Na Bukatar Kafa Cibiyoyin Bincike Kan Nau’ikan Dabbobi A Nijeriya

Dalilin Kwararru Na Bukatar Kafa Cibiyoyin Bincike Kan Nau’ikan Dabbobi A Nijeriya

July 5, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.