• English
  • Business News
Thursday, October 23, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

PDP Ta Zama Fanko, Ta Rasa Komai– Dele Momodu

by Abubakar Sulaiman
2 months ago
PDP

LABARAI MASU NASABA

Sojoji Sun Kashe ‘Yan Ta’adda 50, Sun Daƙile Hare-Hare A Borno

Tinubu Ya Rantsar Da Amupitan A Matsayin Sabon Shugaban INEC

Tsohon jigo a jam’iyyar PDP kuma mawallafin jaridar Ovation, Dele Momodu, ya kwatanta jam’iyyar da “ɗakin gawarwaki,” yana mai cewa wakilan jam’iyyar APC sun mamaye ta gaba ɗaya. Ya bayyana haka ne a cikin hirarsa da aka yi a shirin Sunrise Daily na gidan talabijin ɗin Channels a ranar Litinin, inda ya ce dole ya fice daga PDP zuwa jam’iyyar ADC saboda PDP ta rasa tasiri da nagarta.

Momodu ya ce matakin da ya ɗauka bai saɓa da ɗabi’arsa ta siyasa ba, domin tun da farko ya saba ficewa daga jam’iyya idan ta kauce daga abin da ya dace. Ya tuna yadda a shekarar 2011 ya yi takarar shugaban ƙasa a ƙarƙashin jam’iyyar NCP bayan ya bar Labour Party wacce ta ƙi tsayar da ɗan takara. Duk da cewa ya samu ƙuri’u sama da dubu 26 kacal a wancan lokacin, ya ce darasin da ya koya shi ne cewa jam’iyya sabuwa ba ta da sauƙin samun nasara a Nijeriya.

  • Dele Momodu Ya Fice Daga Jam’iyyar PDP Zuwa ADC
  • Ƴan PDP Na Fice Wa Na Barin Jam’iyyar Ga Wike Da Ƴan Koransa –  Dele Momodu

Ya bayyana cewa shiga PDP ya biyo bayan gamsuwa da rashin tasirin gwamnatin APC ta shugaba Muhammadu Buhari. Amma a zaɓen fidda gwani na PDP a 2022, inda ya kasa samun ƙuri’a ko guda, ya fahimci cewa manyan attajirai ne ke mallakar jam’iyyar. A cewarsa, wannan ya nuna ƙarara cewa kuɗi da son zuciya sun mamaye tsarin dimokuraɗiyyar jam’iyyar.

Momodu ya bayyana PDP a matsayin jam’iyya mai shirin mutuwa, wacce wasu mutane ke so kawai ta ci gaba da kasancewa a ICU saboda son kai. Ya ce ba ya ganin jam’iyyar za ta iya ceto kanta daga wannan halin. Ya ƙara da cewa shi a matsayinsa na ɗan jarida da mai sharhi a harkokin jama’a zai ci gaba da lura da al’amura, amma ba zai iya zama ɓangare na jam’iyya da aka riga aka yi hijira ba.

ShareTweetSendShare

MASU ALAKA

Sojoji Sun Kashe Mayakan Boko Haram 6, Sun Kama Wasu A Borno
Manyan Labarai

Sojoji Sun Kashe ‘Yan Ta’adda 50, Sun Daƙile Hare-Hare A Borno

October 23, 2025
Tinubu Ya Rantsar Da Amupitan A Matsayin Sabon Shugaban INEC
Manyan Labarai

Tinubu Ya Rantsar Da Amupitan A Matsayin Sabon Shugaban INEC

October 23, 2025
Yadda DSS Suka Kama Masu Safarar Makamai Ga ‘Yan Bindiga A Jihar Kaduna
Manyan Labarai

Yadda DSS Suka Kama Masu Safarar Makamai Ga ‘Yan Bindiga A Jihar Kaduna

October 23, 2025
Next Post
DSS Ta Ba Sowore Mako Ɗaya Ya Janye Maganarsa Kan Tinubu

DSS Ta Ba Sowore Mako Ɗaya Ya Janye Maganarsa Kan Tinubu

LABARAI MASU NASABA

Shugaban Senegal: Kasar Sin Ta Zama Abin Koyi Ga Kasashe Masu Tasowa

Shugaban Senegal: Kasar Sin Ta Zama Abin Koyi Ga Kasashe Masu Tasowa

October 23, 2025
Sojoji Sun Kashe Mayakan Boko Haram 6, Sun Kama Wasu A Borno

Sojoji Sun Kashe ‘Yan Ta’adda 50, Sun Daƙile Hare-Hare A Borno

October 23, 2025
Me Ake Fatan Gani A Shirin Sin Na Raya Kasa Na Shekaru Biyar Biyar Na Gaba

Me Ake Fatan Gani A Shirin Sin Na Raya Kasa Na Shekaru Biyar Biyar Na Gaba

October 23, 2025
Harkokin Ciniki Da Zuba Jari Tsakanin Sin Da Afirka Sun Samu Ci Gaba Mafi Girma a Shekaru 5 Da Suka Gabata

Harkokin Ciniki Da Zuba Jari Tsakanin Sin Da Afirka Sun Samu Ci Gaba Mafi Girma a Shekaru 5 Da Suka Gabata

October 23, 2025
Uwargidan Tinubu Ta Ƙaddamar Da Ɗakin Karatu Na E-learning A Zamfara

Uwargidan Tinubu Ta Ƙaddamar Da Ɗakin Karatu Na E-learning A Zamfara

October 23, 2025
Kungiyar IOMed Za Ta Taka Rawar Gani Wajen Gina Al’umma Mai Makomar Bai Daya 

Kasar Sin Ta Karyata Rahoto Na Zuki-ta-malle Da Wata Cibiyar Binciken Amurka Ta Fitar Game Da Hadin Gwiwar Sin Da Yammacin Afirka

October 23, 2025
An Kammala Taron JKS Inda Aka Amince Da Shawarwari Kan Shirin Ci Gaban Kasar Sin Na Shekaru Biyar-biyar Karo Na 15

An Kammala Taron JKS Inda Aka Amince Da Shawarwari Kan Shirin Ci Gaban Kasar Sin Na Shekaru Biyar-biyar Karo Na 15

October 23, 2025
Tinubu Ya Rantsar Da Amupitan A Matsayin Sabon Shugaban INEC

Tinubu Ya Rantsar Da Amupitan A Matsayin Sabon Shugaban INEC

October 23, 2025
Sanarwar Bayan Taron Jks: Mene Ne Sirrin Kwarin Gwiwar Kasar Sin?

Sanarwar Bayan Taron Jks: Mene Ne Sirrin Kwarin Gwiwar Kasar Sin?

October 23, 2025
Wani Soja Ya Kashe Kansa Bayan Kashe Matarsa A Jihar Neja

Sojoji Sun Kama Fitaccen Ɗan Bindiga Babawo Badoo Da Wasu 37 A Filato 

October 23, 2025

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.