• English
  • Business News
Friday, July 25, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

‘PHISHING’ Sabuwar Hanyar Kutse A Facebook, WhatsApp da Asusun Ajiyar Banki

by Ibrahim Sabo
3 years ago
in Rahotonni
0
‘PHISHING’ Sabuwar Hanyar Kutse A Facebook, WhatsApp  da Asusun Ajiyar Banki
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Tun bayan rubutun da ya gabata a wannan filin na Kimiyya da Fasahar Sadarwa, akan yadda mutum zai kare kansa daga masu kwacen Facebook da WhatsApp (Hackers), to har yanzu wasu suna kiran waya a kan wannan matsala, duk da sun saka makullan sirri masu sarkakiya.

Eh lallai babu shakka zuwa yanzu yawaitar kwacen shafin Facebook da WhatsApp din ya yi sauki kadan. Amma har yanzu ana samu kadan-kadan. Ko da kuwa ka saka makullan sirri (password) masu sarkakiya, to za su iya kwace maka shafin naka ta hanyar Phishing.

  • Yadda ‘Hackers’ Ke Amfani Da Hanyar Smishing Wajen Yin Kutse

Mene Ne Phishing?
Phishing wani tarko ne wato wani ‘common technikue’ ne wanda ake amfani dashi wurin kwacen makullan sirri na Facebook da WhatsApp (hacking password) har da asusun ajiya na Banki.
Phishing wata manhaja ce wadda ake cracking da copy na sirrukan masu website, page, da kuma sace wa users password, da labarai masu muhimmanci (sensitive information) kamar katin waya (credit card) da sauransu.

Daga cikin hanyoyin da ‘hackers’ din suke bi don kutse a shafukan mutane, har su kwace shafin ta hanyar Phishing shi ne, suna kirkirar ‘page’ na bogi, wanda ya yi kama da wani shafi na gaskiya. Wato za su kwaikwayi wani shafi su yi ta yada shi (sharing).

Da farko suna dubawa su ga me aka fi damuwa da shi, to sai su bude shafi mai kama da wancan din. Kuma sun fi bude shafi mai alaka da daukar ma’aikata, wanda zai samu tururuwar cike-cike na jama’ar.

Labarai Masu Nasaba

Rayuwar Aso Rock: Shugabannin Nijeriya 4 Da Suka Mutu Bayan Kammala Wa’adin Mulki

Nijeriya Na Kashe Naira Miliyan 4.3 A Kullum Don Ciyar Da Wadanda Ke Jiran Hukuncin Kisa

Mu dauki misali da shafin INEC na daukar ma’aikata da shafin N-Power. Masu kutsen ‘Hackers’ sun bude page a Facebook da website daban-daban duk na bogi da sunan N-Power. Jama’a da dama sun yi rubdugu da tururuwa wajen bin wadannan shafuka, a tunaninsu shafin N-Power ne na gaskiya.

A cikin wadannan shafukan nasu, za su ce ka saka email da password har da lambar waya. Wani lokacin har da lambar BBN suke tambaya. Ta haka za su samu bayananka (details), sai ya zama duk shafukanka na Facebook, whatsapp da asusun ajiyarka na Banki da sauransu duk za su iya kutsawa su shiga.

Mafi yawan mutane ana yaudararsu ne ta hanyar a yi musu abu kyauta (free). Masu Phishing suna kikirar shafin bogi na MTN, Airtel, ko Glo, sai suce ka saka email da password dinka za a baka kyautar “1GB ko 3GB data”. Da zarar ka saka shikenan sun samu bayananka, sai su yi abin da suke so yi da shi. Su kuma mafi yawan mutane suna da son abu na kyauta, to anan kuma, ake rasa muhimman abubuwa.

Kwanan nan hackers din suka yi amfani da manhajar Phishing suka kikiri wani shafin N-Power na bogi a WhatsApp, sai suce ka saka lambar wayarka, idan ka samu N-Power za su sanar da kai. Kowa idan ya saka, to ya samu. Sai su taya ka murna. Sai su ce ka tura a group din WhatsApp guda biyar. Duk abin da ka ji an ce maka ka tura a group biyar ko sama da haka. Kai ko a group daya aka ce ka tura, wannan shafin na bogi ne.

Akwai wani misali da wani ya bayar a kan irin yadda mutane suke son abu na kyauta.
Ya ce “akwai wani mutum ya gina gidan namun Daji (Zoo), sai yace kudin shiga Naira dubu biyar (5,000). Amma mutane suka ki shiga. Ya rage kudin zuwa dubu Hudu (4,000) nan ma dai aka ki shiga, sai ya sake rage wa zuwa zuwa dubu biyu (2,000) a hakan ma aka ki shiga”.

To sai ya yi wata dabara, yace “duk mai son shiga ya zo ya shiga kyauta” ai nan da nan gidan ‘zoo’ din nan ya cika makil da mutane. Sai kawai ya je ya kunce Zaki. Ai kuwa jama’a suka yi ta gudun ceton rai, kowa yana kokarin fita. Sai yace “duk mai son fita, sai ya bada dubu Goma (10,000), haka aka yi ta biyan dubu goma-goma ana fita. To ka ga irin halin da masu son abu na kyauta yake jefa su.

Idan har za ka yi amfani da wayoyin nan na zamani, to ka kiyaye duk wani abu da aka ce na kyauta ne. Ko ka ga wani shafi an ce maka ana daukan ma’aikata, to ka yi kwakkwaran bincike kafin ka cika.

Abu muhimmi da mutum zai kiyaye shi ne, duk abin da aka ce maka ka saka email, password, lambar waya, lambar asusun ajiya, NIN number, da lambar BBN, to ka yi kwakkwaran bincike, bincike mai zurfi fa sosai, don wadanda suka daukar wa kansu wannan sana’a ta kutse a asusun ajiyar mutane da kutse a shafukan sada zumunta na mutane kullum suna kara fito da sabbin dabaru.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

ShareTweetSendShare
Previous Post

Za A Yi Jana’izar Tsohon Shugaban Jami’ar ABU, Farfesa Abdullahi Mahdi Da Yammacin Ranar Asabar

Next Post

Kai Wa Ofishoshinmu Hari Na Iya Kawo Cikas Ga Zaben 2023 – INEC

Related

Rayuwar Aso Rock: Shugabannin Nijeriya 4 Da Suka Mutu Bayan Kammala Wa’adin Mulki
Rahotonni

Rayuwar Aso Rock: Shugabannin Nijeriya 4 Da Suka Mutu Bayan Kammala Wa’adin Mulki

3 hours ago
Fyade
Rahotonni

Nijeriya Na Kashe Naira Miliyan 4.3 A Kullum Don Ciyar Da Wadanda Ke Jiran Hukuncin Kisa

7 days ago
APC
Manyan Labarai

2027: Gangamin ‘Yan Adawa Ya Sa APC Fafutukar Neman Mafita

7 days ago
Majalisar Dokokin Nijeriya Ta Sanar Da Dakatar Da Ayyukanta Saboda Alhinin Rasuwar Buhari
Labarai

Na Shiga Aikin Soja Domin Gujewa Yin Auren Fari Da Ƙuruciya — Buhari

2 weeks ago
Ko Yanzu Tinubu Ya Yi Rawar Gani, Kuma Yana Ƙoƙari Sosai – Buhari
Rahotonni

Muhimman Abubuwa 10 Da Kowa Zai So Ya Sani Game Da Marigayi Shugaban Ƙasa Buhari

2 weeks ago
2027: Shugabannin Hamayya Sun Bazama Neman Goyon Baya A Yankunansu
Manyan Labarai

2027: Shugabannin Hamayya Sun Bazama Neman Goyon Baya A Yankunansu

2 weeks ago
Next Post
Kai Wa Ofishoshinmu Hari Na Iya Kawo Cikas Ga Zaben 2023 – INEC

Kai Wa Ofishoshinmu Hari Na Iya Kawo Cikas Ga Zaben 2023 - INEC

LABARAI MASU NASABA

Sin Da EU Suna Kokarin Samun Moriyar Juna A Shekaru 50 Masu Zuwa

Sin Da EU Suna Kokarin Samun Moriyar Juna A Shekaru 50 Masu Zuwa

July 25, 2025
Dalilin Da Ya Sa Har Yanzu Obi Da El-Rufai Ba Su Shiga ADC A Hukumance Ba — Kakakin Jam’iyyar 

Dalilin Da Ya Sa Har Yanzu Obi Da El-Rufai Ba Su Shiga ADC A Hukumance Ba — Kakakin Jam’iyyar 

July 25, 2025
Dangote Ya Sake Zama Wanda Ya Fi Kowa Kudi A Afrika Karo Na 12

Dangote Ya Ajiye Muƙamin Shugabancin Kamfaninsa Na Siminti

July 25, 2025
Binciken Jin Raayoyi Na CGTN: Duniya Ta Saba Da “Kauracewar” Amurka

Binciken Jin Raayoyi Na CGTN: Duniya Ta Saba Da “Kauracewar” Amurka

July 25, 2025
Jam’iyyar PDP Ta Janye Daga Shiga ZaÉ“en Ƙananan Hukumomi A Kebbi

2027: Masu Neman Takarar Shugaban Kasa A PDP Sun Kara Matsa Kaimi Bayan Ficewar Atiku

July 25, 2025
Xi Jinping Ya Karbi Takardun Nadi Daga Sabbin Jakadun Kasashen Waje

Xi Jinping Ya Karbi Takardun Nadi Daga Sabbin Jakadun Kasashen Waje

July 25, 2025
Rayuwar Aso Rock: Shugabannin Nijeriya 4 Da Suka Mutu Bayan Kammala Wa’adin Mulki

Rayuwar Aso Rock: Shugabannin Nijeriya 4 Da Suka Mutu Bayan Kammala Wa’adin Mulki

July 25, 2025
Wakilin Sin Ya Karyata Amurka Game Da Batun Yankin Xinjiang Na Sin a Taron Kwamitin Sulhun MDD

Wakilin Sin Ya Karyata Amurka Game Da Batun Yankin Xinjiang Na Sin a Taron Kwamitin Sulhun MDD

July 25, 2025
Gwamnan Jigawa Ya Rattaba Hannu Kan Kudirin Dokar Tabbatar Da Hisbah

Gwamnan Jigawa Ya Rattaba Hannu Kan Kudirin Dokar Tabbatar Da Hisbah

July 25, 2025
Kamfanin Sinotruk Na Kasar Sin Ya Kaddamar Da Sabbin Motocin Dakon Kaya A Kenya

Kamfanin Sinotruk Na Kasar Sin Ya Kaddamar Da Sabbin Motocin Dakon Kaya A Kenya

July 25, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.