• English
  • Business News
Sunday, September 7, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Putin Ya Fita Daga Raina – Trump

by Rabi'u Ali Indabawa and Sulaiman
2 months ago
in Labarai
0
Yadda Donal Trump Ya Lashe Zaben Shugabancin Amurka
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Donald Trump ya ce Vladmir Putin na Rasha ya sare masa, kamar yadda ya shaida wa BBC a tattauna ta musamman ta wayar tarho.

Shugaban na Amurka ya amsa tambaya lokacin da aka tambaye shi ko ya yarda da shugaban Rasha, ya yi martani cewa: ”Babu wanda na yarda da shi.”

  • Tarihin Yadda Cinikin Bayi Ya Fara A Nahiyar Afirka (6)
  • Wace Kasa Ce Take Son Zama “Kasa Ta Uku Mai Tsaro” A Wurin Amurka?

Trump na wadannan bayanai ne sa’o’i bayan ya sanar da shirin aike makamai ga Ukraine da gargadin lafta haraji kan Rasha muddin taki cimma yarjejeniyar tsagaita wuta nan da kwanaki 50.

A tattaunawar da ta tabo abubuwa daban-daban daga ofishinsa, shugaban ya nuna yana tare da Nato, wanda a baya yake suka, tare da bayyana cikakken goyon-bayan ayyukanta na tsaro.

Shugaban ya bada damar tattaunawa da shi na mintina 20, bayan BBC ta tuntube shi domin tsokaci kan cika shekara guda da kokarin hallaka shi a Butler da ke, Pennsylbania.

Labarai Masu Nasaba

Matsalar Tsaro: Gwamnonin Arewa Sun Bullo Da Sabbin Matakan Yaki Da Ta’addanci

Kwamishinan ‘Yansandan Abuja Ya Gargadi Jami’ansa Kan Arangama Da Direbobi A Titi

Da aka tambaye shi kan ko tsallake rijiya da baya a harin da aka kai masa ya sauya masa rayuwa, Trump ya ce baya son ya rinka yawan tuna wa da batun.

“Ya ce ba na son tunanin ko lamarin ya sauya ni, “In ji Trump. Zama ana nazari a kai, a cewarsa “na iya sauya mun rayuwa.”

Bayan ganawa da shugaban Nato Mark Rutte a fadar White House, shugaban ya yi amfani da damar da ya samu wajen bayanai da nuna takaicinsa da shugaban Rasha.

Trump ya ce ya yi tunanin za a cimma yarjejeniya a kan teburi da Rasha amma sai gashi an yi zama hudu ba a daidaita ba.

A lokacin da BBC ta yi masa tambaya idan hakan na nufi ya fita batun Putin, shugaban ya yi martani: ”Ina takaici kuma ya sare mun, amma dai ban kammala da shi ba. Amma dai ya bata mun rai.”

Da aka tambaye shi kan ko wace dabara zai yi amfani da ita wajen tursasa wa Bladimir Putin ya ”daina zub da jini” shugaban na Amurka ya ce, “Muna kokarin cimma hakan.”

“Za mu samu fahimtar juna, iya abin da zance kenan, kuma ina ganin muna hanyar cimma hakan,’ kuma shi da kansa ba zai sake rusa gini a Kyib ba.”

Sannan tattaunawar ta ci gaba a kan Nato, wanda a baya shugaba Trump ya sha caccaka a matsayin ”mara amfani”.

Da aka tambaye shi kan ko har yanzu yana kan wannan batu, ya ce, “A’a. Ina ganin a yanzu Nato ayyukanta sun inganta,” saboda hadakar, na ”biyan hakokin da ke wuyanta”.

Ya ce yana da yakinin hada hannu tare, saboda hakan na nufin kananan kasashe na iya kare kansu daga manyan kasashe.

An tambaye Trump kan makomar Burtaniya a duniya, sai ya ce yana ganin ”kasa ce mai kyau”, kuma yana da kadarori a kasar”.

Ya ce yana da anniyar kai ziyara a karo na biyu Burtaniya cikin watan Satumba wannan shekara.

Da aka masa tambaya me yake son cimma a ziyarar, Trump ya ce, “Ina son na samu lokaci mai armashi da girmama Sarki Charles, saboda mutumin kirki ne.”


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

ShareTweetSendShare
Previous Post

Kasar Sin Ta Ba Da Rahoton Samun Ci Gaban Aikin Gona Mara Gurbata Muhalli Ba Tare Da Tangarda Ba

Next Post

An Yi Taron Farko Na Shugabannin Matasa Na Dandalin Zaman Lafiya Da Tsaro Na Sin Da Afirka

Related

Arewa
Rahotonni

Matsalar Tsaro: Gwamnonin Arewa Sun Bullo Da Sabbin Matakan Yaki Da Ta’addanci

20 minutes ago
Da Ɗumi-ɗumi: ‘Yansanda Sun Tarwatsa Masu Zanga-zangar Adawa Da Dokar Ta-ɓaci A Ribas
Labarai

Kwamishinan ‘Yansandan Abuja Ya Gargadi Jami’ansa Kan Arangama Da Direbobi A Titi

44 minutes ago
Yin Ƙidaya Na Da Muhimmanci Ga Ci Gaban Al’umma – Kwamishina Sa’adatu
Labarai

Yin Ƙidaya Na Da Muhimmanci Ga Ci Gaban Al’umma – Kwamishina Sa’adatu

3 hours ago
Gwamnati Ta Kaddamar Da Sabbin Darussan Karatu A Makarantun Nijeriya
Labarai

Gwamnati Ta Kaddamar Da Sabbin Darussan Karatu A Makarantun Nijeriya

4 hours ago
Zulum Ya Tabbatar Da Harin Boko Haram Ya Ci Rayukan Mutane 63 
Labarai

Zulum Ya Tabbatar Da Harin Boko Haram Ya Ci Rayukan Mutane 63 

6 hours ago
Mun Tara Kuɗi Sama Da Naira Miliyan 170 Na Fatun Layya – Sheikh Bala Lau 
Manyan Labarai

Mun Tara Kuɗi Sama Da Naira Miliyan 170 Na Fatun Layya – Sheikh Bala Lau 

7 hours ago
Next Post
An Yi Taron Farko Na Shugabannin Matasa Na Dandalin Zaman Lafiya Da Tsaro Na Sin Da Afirka

An Yi Taron Farko Na Shugabannin Matasa Na Dandalin Zaman Lafiya Da Tsaro Na Sin Da Afirka

LABARAI MASU NASABA

Arewa

Matsalar Tsaro: Gwamnonin Arewa Sun Bullo Da Sabbin Matakan Yaki Da Ta’addanci

September 7, 2025
Da Ɗumi-ɗumi: ‘Yansanda Sun Tarwatsa Masu Zanga-zangar Adawa Da Dokar Ta-ɓaci A Ribas

Kwamishinan ‘Yansandan Abuja Ya Gargadi Jami’ansa Kan Arangama Da Direbobi A Titi

September 7, 2025
Yin Ƙidaya Na Da Muhimmanci Ga Ci Gaban Al’umma – Kwamishina Sa’adatu

Yin Ƙidaya Na Da Muhimmanci Ga Ci Gaban Al’umma – Kwamishina Sa’adatu

September 7, 2025
ASUU

Malaman Jami’o’i Sun Zama Abin Tausayi —Kungiyar ASUU

September 7, 2025
Gwamnati Ta Kaddamar Da Sabbin Darussan Karatu A Makarantun Nijeriya

Gwamnati Ta Kaddamar Da Sabbin Darussan Karatu A Makarantun Nijeriya

September 7, 2025
Zulum Ya Tabbatar Da Harin Boko Haram Ya Ci Rayukan Mutane 63 

Zulum Ya Tabbatar Da Harin Boko Haram Ya Ci Rayukan Mutane 63 

September 7, 2025
Mun Tara Kuɗi Sama Da Naira Miliyan 170 Na Fatun Layya – Sheikh Bala Lau 

Mun Tara Kuɗi Sama Da Naira Miliyan 170 Na Fatun Layya – Sheikh Bala Lau 

September 7, 2025
Fyade

Matsalar Ciwon Kwakwalwa A Gidajen Yarin Kasar Nan

September 7, 2025
Kuri’ar Jin Ra’ayoyi Ta CGTN: Sake Maido Da Ma’aikatar Yaki A Amurka Ya Nuna Babu Dakatawa A Yaki Hatta A Wajen Sa Suna 

Kuri’ar Jin Ra’ayoyi Ta CGTN: Sake Maido Da Ma’aikatar Yaki A Amurka Ya Nuna Babu Dakatawa A Yaki Hatta A Wajen Sa Suna 

September 6, 2025
Rikicin NNPP A Kano: Wani Tsagi Ya Soki Korar Abdulmumini Jibrin Kofa

Rikicin NNPP A Kano: Wani Tsagi Ya Soki Korar Abdulmumini Jibrin Kofa

September 6, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.