• English
  • Business News
Sunday, October 5, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

RA’AYI: Sauye-sauyen Sheka Ba Zai Sa Ka Ci Zabe Ba A Nijeriya

by Yusuf Shuaibu
1 year ago
in Tambarin Dimokuradiyya
0
RA’AYI: Sauye-sauyen Sheka Ba Zai Sa Ka Ci Zabe Ba A Nijeriya
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Idan kana matukar son cin zabe a Nijeriya ba sai ka rika sauya sheka daga wannan jam’iyyar zuwa wancen. Babu wanda ya taba yin haka kuma ya cin zabe a Nijeriya tun lokacin da Turawan mulkin mallaka suka hada yankunan kasar nan a 1914.

Za a iya yin haka a matakin yanki da jiha, musamman a yankin da ke da dimbin kabilu. Amma a tarayya, mutum zai iya shan kasa idan ya yi hakan.

  • Bayan Cinnawa Masallaci Wuta, Mutane 11 Sun Rasu A Kano
  • Zanga-zangar Karin Kudin Wuta: Gwamnati Ta Shelanta Matakin Da Za Ta Dauka

Wadanda suke biyayya ga jam’iyyunsu ne kadai suka iya lashe zaben shugaban kasa ko na Firiminista a Nijeriya. Jam’iyyunku na iya shiga yin kwance ta hadewa da wata jam’iyya, ko ta sauya sunanta kuma mutum ya ci gaba da zama a cikinta. Amma a lokacin da ka bar jam’iyyaka ka kuma wata, mutane su ma za su bar ka.

Ko mai zai faru a cikin jam’iyyarka, ka zauna domin a warware lamarin. Ka tabbatar da kanka a can. Ka kasance mai gwagwarmaya wajen daga darajar jam’iyyarka. Idan har ba z aka iya jagorantar jam’iyyarka wajen warware matsaloli ba, to ba za ka iya shawo kan ra’ayin masu jefa kuri’a ba kan kabilanci na tunanin za ka iya fitar da kasa daga matsaloli.

Tafawa Balewa ya kasance dan jam’iyyar mutanen arewa. Bai taba sauya jam’iyya ba. Shagari dan jam’iyyar National Party of Nigeria, wanda ta koma jam’iyyar mutanen arewa. Bai taba sauya jam’iyya ba.

Labarai Masu Nasaba

ADC Ta Umarci Dukkan Mambobinta Su Yi Murabus Daga Tsoffin Jam’iyyunsu

Dage Zaben Shugabannin PDP Na Jihohi Ya Kara Ruruta Wutar Rikici A Jam’iyyar

Obasanjo da Yar’adua da Jonathan dukkaninsu sun kasance ‘ya’yan jam’iyyar PDP. Ba su taba canza jam’iyya ba.

Buhari ya kasance dan jam’iyyar APP, wacce daga baya aka sauya mata suna zuwa ANPP. Daga karshe jam’iyyar ta rarrabu, kuma Buhari ya kasance a jam’iyyar CPC, a 2013, jam’iyyar ta hade da sauran jam’iyyu wanda aka samu jam’iyyar APC.

Tinubu ya kasance dan jam’iyyar SDP, wanda Abacha ya rushe a 1993. Bayan haka, ya taimaka wajen kafa jam’iyyar AD, wanda ta hade da sauran jam’iyyu aka samu ACN a 2006. ACN ta hade da sauran jam’iyyu aka samu jam’iyyar APC a 2013.

Ya kamata ‘yan siyasan Nijeriya su dauki darashi da abun da ya faru a baya. Mafi kyan hasashe a yi da abin da ya gabata. Daga yanzu zuwa 2027, duk dan siyasan da ya bar jam’iyyarsa zuwa wata jam’iyya ba tare da an yi hadaka ba, to yana taba wa kansa lokaci da kudinsa ne idan har ya tsaya takarar shugaban kasa.

Duk kasar da ke kokarin samun daidaiton siyasa ba za ta iya samun shugaba da yake faman samun hankalinsa da na daidaituwar siyasa ba.

Kasar da ke mafa da gwagwarmayar siyasa ba za ta iya da shugaban da shi ma yana fama da lafiyar kwakwalwarsa da kuma daidaiton siyasarsa.

Abun takaici a Nijeriya shi ne, ka bar jam’iyyarka a gwagwarmayar neman shugaban kasa, sannan ka zama dan takara na wata jam’iyya.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: Sauya ShekaSiyasa
ShareTweetSendShare
Previous Post

Wutar Lantarki Ta Yi Ajalin Wani Mutum A Bayelsa

Next Post

Zaben Ondo: 20 Ga Mayu Ita Ce Ranar Mika Sunayen ‘Yan Takara Ta Karshe – INEC

Related

ADC Ta Dakatar Da Shugabanta Da Wasu Jiga-jigai 3 A Kebbi
Tambarin Dimokuradiyya

ADC Ta Umarci Dukkan Mambobinta Su Yi Murabus Daga Tsoffin Jam’iyyunsu

1 day ago
Dage Zaben Shugabannin PDP Na Jihohi Ya Kara Ruruta Wutar Rikici A Jam’iyyar
Tambarin Dimokuradiyya

Dage Zaben Shugabannin PDP Na Jihohi Ya Kara Ruruta Wutar Rikici A Jam’iyyar

1 day ago
Yadda Na Kawo Karshen Yajin Aikin ASUU Cikin Kwana Daya – Jonathan
Tambarin Dimokuradiyya

Lalacewar Tsarin Zabe Babbar Barazana Ce Ga Dorewar Dimokuradiyyar Afirka — Jonathan

1 week ago
Fursunoni Ba Za Su Samu Damar Kada Kuri’a Ba A Zaben 2023 – INEC
Tambarin Dimokuradiyya

Rudani Ya Kunno Kai Yayin Da INEC Ta Ki Amincewa Da Shugabancin ADC

4 weeks ago
‘Yan Nijeriya Suna Shan Wahala A Lokacin Da Gwamnatin Tinubu Ta Fi Damuwa Da Aljihunta – Sule Lamido
Tambarin Dimokuradiyya

‘Yan Nijeriya Suna Shan Wahala A Lokacin Da Gwamnatin Tinubu Ta Fi Damuwa Da Aljihunta – Sule Lamido

4 weeks ago
Daraktoci Da Jami’an FCT 7 Na Fuskantar Tuhume-tuhume Kan Badakar Fili
Tambarin Dimokuradiyya

2027: Idan Kana Son Tarwatsa PDP, To Ka Dawo Da Peter Obi – Wike

4 weeks ago
Next Post
Zaben Ondo: 20 Ga Mayu Ita Ce Ranar Mika Sunayen ‘Yan Takara Ta Karshe – INEC

Zaben Ondo: 20 Ga Mayu Ita Ce Ranar Mika Sunayen ‘Yan Takara Ta Karshe – INEC

LABARAI MASU NASABA

Me Yarjejeniyar Kawo Karshen Yakin Gaza Da Amurka Ta Tsara Ta Kunsa?

Me Yarjejeniyar Kawo Karshen Yakin Gaza Da Amurka Ta Tsara Ta Kunsa?

October 4, 2025
Firaministan Pakistan: Shugaba Xi Jinping Shugaba Ne Mai Hangen Nesa

Firaministan Pakistan: Shugaba Xi Jinping Shugaba Ne Mai Hangen Nesa

October 4, 2025
Kokarin Da ‘Yan Wasan Nijeriya Suka Yi Wajen Lashe Kyautar Ballon d’Or

Kokarin Da ‘Yan Wasan Nijeriya Suka Yi Wajen Lashe Kyautar Ballon d’Or

October 4, 2025
Jonathan Ya Ƙaryata Batun Danganta Buhari Da Boko Haram

Jonathan Ya Ƙaryata Batun Danganta Buhari Da Boko Haram

October 4, 2025
Sin Ta Yi Kira Ga Kasa Da Kasa Su Ki Amincewa Da Takunkumin Bangare Daya

Sin Ta Yi Kira Ga Kasa Da Kasa Su Ki Amincewa Da Takunkumin Bangare Daya

October 4, 2025
Kasar Sin Ta Soki Matakan Harajin Amurka “Na Ramuwa” A WTO

Kasar Sin Ta Soki Matakan Harajin Amurka “Na Ramuwa” A WTO

October 4, 2025
Jami’ar Nsukka Ta Ce Shaidar Digirin Ministan Fasaha, Uche Nnaji, Ta Bogi Ce

Jami’ar Nsukka Ta Ce Shaidar Digirin Ministan Fasaha, Uche Nnaji, Ta Bogi Ce

October 4, 2025
Jami’in MDD: Shawarar GGI Za Ta Jagoranci Duniya Zuwa Samun Kyakkyawar Makoma Mai Cike Da Adalci

Jami’in MDD: Shawarar GGI Za Ta Jagoranci Duniya Zuwa Samun Kyakkyawar Makoma Mai Cike Da Adalci

October 4, 2025
Nijeriya Ta Samu Kwarin Gwiwar Zuwa Kofin Duniya

Nijeriya Ta Samu Kwarin Gwiwar Zuwa Kofin Duniya

October 4, 2025
Bayan Janyewar Sojojin Kamaru, Boko Haram Sun Dawo Kashe-Kashe A Borno

Bayan Janyewar Sojojin Kamaru, Boko Haram Sun Dawo Kashe-Kashe A Borno

October 4, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.