Leadership Hausa Newspapers
No Result
View All Result
  • LABARAI
  • WASANNI
  • RAHOTANNI
  • SIYASA
  • KASUWANCI
  • ADABI
  • RA’AYINMU
  • TATTAUNAWA
  • BIDIYO
  • MAKALAR YAU
  • LABARAI
  • WASANNI
  • RAHOTANNI
  • SIYASA
  • KASUWANCI
  • ADABI
  • RA’AYINMU
  • TATTAUNAWA
  • BIDIYO
  • MAKALAR YAU
No Result
View All Result
Leadership Hausa Newspapers
No Result
View All Result
ADVERTISEMENT
Home DAN JARIDA

Ra’ayoyin Makaranta Da Dillalan LEADERSHIP A YAU

by Tayo Adelaja
September 25, 2017
in DAN JARIDA
3 min read
WhatsAppShare on FacebookShare on TwitterShare on Telegram

Tun daga ranar da aka wayi gari jaridar LEADERSHIP A YAU ta fara fitowa a kullum masu  karanta jardar a lokacin da take fitowa a ranar Juma’a suka fara tsokaci daban-daban, kuma sun bayyana ra’ayoyinsu ne a zantawar da suka yi da wakilinmu da ke Zariya.

  • Alhaji Sale Moriki

Wani masanin harkokin tsaro, shugaban al’umma, Mai Unguwar Layin Zamfarawa, kuma uba a kungiyar ‘yan kasuwar sayar da takin zamani ya bayyana cewa in har ana maganar jaridar harshen Hausa ne, ya fara karanta jaridar ne GASKIYA TA FI KWABO da aka fara bugata a shekara r ta 1939.

Alhaji Moriki ya ce tun daga waccan shekarar, ya rungumi jaridun Hausa da hannu bibiyu, kuma ya ce yana yin tsokaci ga al’amura da dama da suka shafi ci gaban Nijeriya.Ya kara da cewar, duk mai karanta jaridun Hausa, ya san sunansa ba bakon suna ba ne a shafukan jaridun.

Amma game da fitowar LEADRSHIP A YAU a kullum, Alhaji Sale Moriki ya ce duk wanda ya kalli jardar ya san ta yi fitowar muricin kan dutse, na yadda ta tsara jaridar da kuma yadda ake kokarin ganin an rubuta abubuwan da masu karatun jaridar suke so.

Ya kuma tabbatar da cewar yadda al’ummar da suke karanta jaridar suka rungumi jaridar da hannu bibiyu, to wajibi ne masu dauko rahotanni da ake sawa a jaridar su kara tashi tsaye, na ganin sun ba marada kunya, da suke ganin sun dauko aiki mai yawa.

Alhaji Sale Moriki ya kammala da cewar, zai kyau jaridar ta fito da wani shafi da masu karanta jaridar za su rika rubuta ra’ayoyinsu da ya shafi jaridar ko kuma wasu al’amurra da suka shafi ci gaban al’umma na ciki da wajen Nijeriya.

  • Malam Bawa Mai Sayar Da Jarida

A lokacin da wakilinmu ya ziyarci PZ, cibiyar sayar da jaridu ta

Zariya ya yi tozali da Malam Bawa, wanda duk mai sayen jarida ko jaridu a PZ ya san sunan, ba bakon suna ba ne fiye da shekaru talatin da suka  gabata.

Malam Bawa ya ce, ranar da ya ji labarin LEADERSHIP A YAU za ta fara fitowa a kullum, sai ya ce sun dauki matakan share wa masu karatun jaridun Hausa hawaye, domin a halin yanzu, ya fi kowa sanin bukatar da al’umma ke yi na jaridun Hausa a Zariya.

Sai dai ya ce, abu biyu yake son shugabannin jardar LEADERSHIP A YAU su kiyaye, abu biyun su ne, a sa ido a ga ana kawo jaridar a kan lokaci. Na biyu, a kara yawan jaridar da ake kawowa Zariya. Kamar yadda ya ce jaridun da ake kawowa ba sa isan kashi biyu a cikin goma na masu bukatar karantata.

  • Malam Sani Aliyu Basawa

Shi kuma wannan matashi ne da ya shafe fiye da shekara goma yana sayar da jaidu a PZ Sabon Garin Zariya. Ya ce babbar shawarar da zai bayar, a kula da kawo jaridar a kan lokaci, kuma a kara yawan jaridar da ake turowa Zariya. Kamar yadda ya ce, su da suke sayar da jardu, sun fi kowa sanin yadda al’umma ke son jardar LEADERSHIP A YAU.

Daga nan sai Malam Sani Basawa ya jinjina wa ma’aikata da mahukuntan wannan jarida na wannan babban aiki da suka dora wa kansu da nufin share wa masu son karanta jaridun Hausa hawaye.

SendShareTweetShare
Previous Post

Soja Ya Harbe Wani Matashin Manomi Har Lahira A Adamawa

Next Post

LEADERSHIP A Yau Za Ta Taimaka Wa Daliban Kwalejin Horas Da Malamai —Dakta Baraka Abubakar

RelatedPosts

Sabuwar Kasuwar Safarar Mata Ta Bude A Haifaraban

Kallon Talabijin Da Jin Radiyo Suka Sa Ni Kafa Kamfanin Jarida – Yahaya

by Tayo Adelaja
3 years ago
0

Filin Dan jarida ya samu nasarar tattaunawa da mawallafin jaridar...

Yadda Na Tsinci Kaina A Aikin Jarida — Malikawa

Yadda Na Tsinci Kaina A Aikin Jarida — Malikawa

by Tayo Adelaja
3 years ago
0

Tare da Muhammad Awwal Umar email:awalumar7@gmail.com 08093947702   Wakilinmu Mustapha...

Ni Na Kirkiri Gidan Rediyon Kusharki – Musa

Ni Na Kirkiri Gidan Rediyon Kusharki – Musa

by Tayo Adelaja
3 years ago
0

tare da Muhammad Awwal Umar email:awalumar7@gmail.com 08093947702 A yau filin...

Next Post

LEADERSHIP A Yau Za Ta Taimaka Wa Daliban Kwalejin Horas Da Malamai —Dakta Baraka Abubakar

Leave a Reply Cancel reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

Domin sanya talla ko karin bayani a tuntube wannan numbar +2348126152609.

ADVERTISEMENT
  • LABARAI
  • WASANNI
  • RAHOTANNI
  • SIYASA
  • KASUWANCI
  • ADABI
  • RA’AYINMU
  • TATTAUNAWA
  • BIDIYO
  • MAKALAR YAU
Advertise with us

© 2020 Leadership Group .

No Result
View All Result
  • LABARAI
  • WASANNI
  • RAHOTANNI
  • SIYASA
  • KASUWANCI
  • ADABI
  • RA’AYINMU
  • TATTAUNAWA
  • BIDIYO
  • MAKALAR YAU

© 2020 Leadership Group .

Go to mobile version