• English
  • Business News
Friday, August 1, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Ra’ayoyinku A Kan Nasarorin Da Jami’an Tsaro Ke Samu Kan ‘Yanta’dda A Dazukan Abuja

by Aisha Seyoji
3 years ago
in Rahotonni
0
Ra’ayoyinku A Kan Nasarorin Da Jami’an Tsaro Ke Samu Kan ‘Yanta’dda A Dazukan Abuja
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

A wannan makon mun kawo ra’ayoyinku ne a kan nasarorin da jami’an tsaro suka samu na fatattakar ‘yan ta’adda a yankin Abuja tun bayan umarnin da Shugaba Buhari ya bayar kwanakin baya, bayan da aka Kai wa rundunar da ke tsaronsa hari.

Omar Naseer Imam:

Masha Allah, Muna taya su da addu’a sosai kuma muna fatan wannan nasarar ya game Nijeriya gaba daya kananan jami’an tsaro suna kokari sosai sun bada ransu da duk wani farin cikinsu muna masu fatan alkhairi a koda yaushe.

  • Salman Rushdie: Wanda Ya Yi Batanci Ga Annabi Na Cikin Mawuyacin Hali Bayan Kai Masa Hari
  • Obasanjo Ya Roki Marayun Borno Su Yafe Wa ‘Yan Ta’addar Da Suka Kashe Iyayensu

Sulaiman Muhammad:

To aikuwa har yandu akwai matsala saboda ba a bin su inda suke zaune a cikin dajin kamar yadda suke kaiwa jama’a hari dare da rana suma haka ya kamata a yi musu da tuntuni an gama da wannan matsalar.

Labarai Masu Nasaba

Yadda Masu Bukata Ta Musamman Suka Rungumi Sabbin Dabarun Noma Domin Ciyar Da Kansu

Rayuwar Aso Rock: Shugabannin Nijeriya 4 Da Suka Mutu Bayan Kammala Wa’adin Mulki

It’z Sam Dambatta:

Babu abinda za mu ce sai dai godiya ga Allah (SWT) bisa wannan nasara da aka samu, Sannan muna kara jinjina ga jami’an tsaro bisa wannan aiki da sukai dama munsan za su iya sai dai idan ba a sa su ba. Sannan muna kara tawassali da sunayen Allah na Alhayyu Alkayyum da ya kara inganta mana zaman lafiya da tsaro a kasarmu baki daya.

Umar Bello Ubd:

Abin a yaba musu ne amma mu dama laifinsu muke gani saboda an basu kayan aiki kamar mutoci na shiga daji da bindigogi da nauran gano inda suke.

It’z Jameel Moh’d:

Allah sarki kasata Nijeriya gaskiya muna cikin wani hali Allah ya kawo mana dauki cikin sauki ana kashe bayin Allah wanda ba su ji basu gani ba, ‘yan ta,adda suna daji daina kashe bayin Allah ashe ‘yan ta’adda ne saboda kowa ya sani cewa inda gaske suke yi sun san inda suke suje a ranar daya su gama da su.

Muhd Basheer Sa’ad:

Alhamdulillah Masha Allah!, wannan umarni da aka bawa jami’ai na fatattakar ‘yan ta’adda ya yi amfani sosai kuma Allah ya basu nasara, da ace gwamnati za ta basu dama kamar yadda ta basu a yanzun da to shakka babu za a samu nasara. Gwamnati bata damu da talakawa ba shi ne magana kawai.

Adamu Yunusa Ibrahim:

Tabbas abin a yaba wa hukumomin tsaro ne, domin sun kusa yin sake. Da a ce tun farko ana iya magance matsalar da ba za ta kai girman haka ba. Kowa ya ga yadda Gwamnati ke tura babban kason kasafin kudi a duk shekara ta fannin tsaro, amma sam kwalliya ba ta biyan kudin sabulu. Don haka, matukar ana so a kawo karshen matsalolin tsaro a kasa baki daya, wajibi ne a fito da shirin ba sani ba sabo, kuma a yi tsayuwa irin ta masu daka wajen ganin an kakkabe bata garin da ke cikin al’umma.

Hukumar tsaro ta farin kaya DSS da hukumar tsaro ta sirri SSS Da hukumar leken asiri ta kasa, da hukumar ‘yansanda da Sojojin kasa da na sama da na ruwa da hukumar Cibil Defence, da hukumar hana fasa kwauri ta kasa Customs da hukumar kula da shige da fice ta kasa Immigration, da duk wata hukuma da tsaron kasa ya rataya a wuyansu, ya zama wajibi su kara kaimi wajen kiyaye nauyin da ya rataya a wuyansu nan tsaron rayuka da dukiyoyin jama’ar kasa.

Domin ba su da wata kasa sai Nijeriya, idan Nijeriya ta durkushe su ma sun durkushe.

A karshe ina sake jinjina wa jami’an tsaron da su ke hana idanuwansu bacci domin gudanar da ayyukan su na yau da kullum har suka kakkabe bata gari daga yankin Abuja. Muna fata, za su kara kaimi wajen fadada Ayyukan su, a jihohin Sakkwato da Zamfara da Katsina da Kaduna.

Allah ya taimaki kauyukanmu da mazabunmu da kananan hukumominmu Gundumarmu da Jiharmu da Arewacin Nijeriya da Kasa baki daya. Amin.

Comrade Adamu Yunusa Ibrahim, Malami a Cibiyar Nazarin Hausa, Jami’ar Usmanu Danfodiyo, Sakkwato, Nijeriya.

Nuruddeen Muhammad Funtua:

A gaskiya wannan nasara muna matukar godiya ga Allah (S.W.A.) muna addu’a a gare su bisa wannan namijin kokari da suke yi Allah ya cigaba da basu nasara ya kuma kiyaye manasu a duk inda suke Allah ya kawo mana karshen wannan tashe-tashen hankula aduk fadin Nijeriya baki daya Ameen ya Hayyul kayum.

Yusuf Muhammad Jalingo:

Mude muna kara kalubalantan gwamnati da masu ruwa da tsaki wajen yadda ‘yan jarida suke kokarin nemo labarai wanda har za su iya kutsawa jeji su bankado inda ‘yan ta’adda suke su dauko labarai to haka muke so jami’an tsaro suma suyi haka ko fiye da haka wajen kaiwa ‘yan ta’adda hari da kuma dakile duk wani hari nasu, sai dai jami’an tsaro suna kokari, Allah ya kara lalata shirin masu sharri, Amiin.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: 'Yan ta'addaAbujadajiJami'an TsaroRa'ayi Riga
ShareTweetSendShare
Previous Post

Makarantar ‘Aram Mamu Academy’ Ta Yi Bikin Yaye Dalibai Karo Na Uku

Next Post

Daga Soyayyar Wata Yarinya Na Fara Waka —Abba Ganga

Related

Yadda Masu Bukata Ta Musamman Suka Rungumi Sabbin Dabarun Noma Domin Ciyar Da Kansu
Rahotonni

Yadda Masu Bukata Ta Musamman Suka Rungumi Sabbin Dabarun Noma Domin Ciyar Da Kansu

6 days ago
Rayuwar Aso Rock: Shugabannin Nijeriya 4 Da Suka Mutu Bayan Kammala Wa’adin Mulki
Rahotonni

Rayuwar Aso Rock: Shugabannin Nijeriya 4 Da Suka Mutu Bayan Kammala Wa’adin Mulki

6 days ago
Fyade
Rahotonni

Nijeriya Na Kashe Naira Miliyan 4.3 A Kullum Don Ciyar Da Wadanda Ke Jiran Hukuncin Kisa

2 weeks ago
APC
Manyan Labarai

2027: Gangamin ‘Yan Adawa Ya Sa APC Fafutukar Neman Mafita

2 weeks ago
Majalisar Dokokin Nijeriya Ta Sanar Da Dakatar Da Ayyukanta Saboda Alhinin Rasuwar Buhari
Labarai

Na Shiga Aikin Soja Domin Gujewa Yin Auren Fari Da Ƙuruciya — Buhari

3 weeks ago
Ko Yanzu Tinubu Ya Yi Rawar Gani, Kuma Yana Ƙoƙari Sosai – Buhari
Rahotonni

Muhimman Abubuwa 10 Da Kowa Zai So Ya Sani Game Da Marigayi Shugaban Ƙasa Buhari

3 weeks ago
Next Post
Daga Soyayyar Wata Yarinya Na Fara Waka —Abba Ganga

Daga Soyayyar Wata Yarinya Na Fara Waka —Abba Ganga

LABARAI MASU NASABA

Ya Kamata A Sake Yi Wa Tsarin Ɗaukar Kuratan Ƴansanda Garanbawul

Ya Kamata A Sake Yi Wa Tsarin Ɗaukar Kuratan Ƴansanda Garanbawul

August 1, 2025
Mujallar Qiushi Za Ta Wallafi Jawabin Xi Jinping Game Da Kiyaye Muhallin Halittu

Mujallar Qiushi Za Ta Wallafi Jawabin Xi Jinping Game Da Kiyaye Muhallin Halittu

July 31, 2025
Dangote Ya Bada Shawarar Samar Da Gidaje Masu Rahusa Da ‘Yan Nijeriya Za Su Iya Mallaka

Dangote Ya Bada Shawarar Samar Da Gidaje Masu Rahusa Da ‘Yan Nijeriya Za Su Iya Mallaka

July 31, 2025
NIN-SIM: Masu Hulda Da Kamfanonin Sadarwa Sun Koka Kan Katse Layinsu Daga Tsarin Kira

Kamfanonin Sadarwa Za Su Ci Gaba Da Rajistar Sabon SIM – NIMC

July 31, 2025
Matsayar Bai Daya Da Sin Da Amurka Suka Cimma Ta Fuskar Haraji Na Da Babbar Ma’ana

Matsayar Bai Daya Da Sin Da Amurka Suka Cimma Ta Fuskar Haraji Na Da Babbar Ma’ana

July 31, 2025
Mutane 44 Suka Mutu Bayan Mamakon Ruwa Da Aka Tafka A Beijing

Mutane 44 Suka Mutu Bayan Mamakon Ruwa Da Aka Tafka A Beijing

July 31, 2025
Yadda Yajin Aikin Ma’aikatan Jinya Ya Bar Baya Da Kura A Asibitocin Jihar Filato

Yadda Yajin Aikin Ma’aikatan Jinya Ya Bar Baya Da Kura A Asibitocin Jihar Filato

July 31, 2025
Zargin Da Wasu ’Yan Siyasar Amurka Ke Yi Wa Sin Na Fitar Da Hajoji Fiye Da Kima Ya Sabawa Hujjoji Na Hakika

Zargin Da Wasu ’Yan Siyasar Amurka Ke Yi Wa Sin Na Fitar Da Hajoji Fiye Da Kima Ya Sabawa Hujjoji Na Hakika

July 31, 2025
Gwamnatin Borno Ta Nada Kwamitin Aiwatar Da Mafi Karancin Albashi

Gwamna Zulum Ya Sauke Kwamishinoni Biyu Tare Da Maye Gurbinsu Da Wasu

July 31, 2025
Uganda Ta Jinjinawa Gudummawar Sin Ga Manufofin Wanzar Da Zaman Lafiya A Yankin Kahon Afirka

Uganda Ta Jinjinawa Gudummawar Sin Ga Manufofin Wanzar Da Zaman Lafiya A Yankin Kahon Afirka

July 31, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.