• English
  • Business News
Wednesday, May 14, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Ra’ayoyinku A Kan Nasarorin Da Jami’an Tsaro Ke Samu Kan ‘Yanta’dda A Dazukan Abuja

by Aisha Seyoji
3 years ago
in Rahotonni
0
Ra’ayoyinku A Kan Nasarorin Da Jami’an Tsaro Ke Samu Kan ‘Yanta’dda A Dazukan Abuja
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

A wannan makon mun kawo ra’ayoyinku ne a kan nasarorin da jami’an tsaro suka samu na fatattakar ‘yan ta’adda a yankin Abuja tun bayan umarnin da Shugaba Buhari ya bayar kwanakin baya, bayan da aka Kai wa rundunar da ke tsaronsa hari.

Omar Naseer Imam:

Masha Allah, Muna taya su da addu’a sosai kuma muna fatan wannan nasarar ya game Nijeriya gaba daya kananan jami’an tsaro suna kokari sosai sun bada ransu da duk wani farin cikinsu muna masu fatan alkhairi a koda yaushe.

  • Salman Rushdie: Wanda Ya Yi Batanci Ga Annabi Na Cikin Mawuyacin Hali Bayan Kai Masa Hari
  • Obasanjo Ya Roki Marayun Borno Su Yafe Wa ‘Yan Ta’addar Da Suka Kashe Iyayensu

Sulaiman Muhammad:

To aikuwa har yandu akwai matsala saboda ba a bin su inda suke zaune a cikin dajin kamar yadda suke kaiwa jama’a hari dare da rana suma haka ya kamata a yi musu da tuntuni an gama da wannan matsalar.

Labarai Masu Nasaba

Gwamna Umar Namadi Ya Dauki Matakan Kai Jihar Jigawa Babban Matsayi

Ficewar Kasar Nijar Daga Rundunar Hadin Gwiwa Ta Kasa Da Kasa Barazana Ce Ga Tsaro -Hedikwatar Tsaro

It’z Sam Dambatta:

Babu abinda za mu ce sai dai godiya ga Allah (SWT) bisa wannan nasara da aka samu, Sannan muna kara jinjina ga jami’an tsaro bisa wannan aiki da sukai dama munsan za su iya sai dai idan ba a sa su ba. Sannan muna kara tawassali da sunayen Allah na Alhayyu Alkayyum da ya kara inganta mana zaman lafiya da tsaro a kasarmu baki daya.

Umar Bello Ubd:

Abin a yaba musu ne amma mu dama laifinsu muke gani saboda an basu kayan aiki kamar mutoci na shiga daji da bindigogi da nauran gano inda suke.

It’z Jameel Moh’d:

Allah sarki kasata Nijeriya gaskiya muna cikin wani hali Allah ya kawo mana dauki cikin sauki ana kashe bayin Allah wanda ba su ji basu gani ba, ‘yan ta,adda suna daji daina kashe bayin Allah ashe ‘yan ta’adda ne saboda kowa ya sani cewa inda gaske suke yi sun san inda suke suje a ranar daya su gama da su.

Muhd Basheer Sa’ad:

Alhamdulillah Masha Allah!, wannan umarni da aka bawa jami’ai na fatattakar ‘yan ta’adda ya yi amfani sosai kuma Allah ya basu nasara, da ace gwamnati za ta basu dama kamar yadda ta basu a yanzun da to shakka babu za a samu nasara. Gwamnati bata damu da talakawa ba shi ne magana kawai.

Adamu Yunusa Ibrahim:

Tabbas abin a yaba wa hukumomin tsaro ne, domin sun kusa yin sake. Da a ce tun farko ana iya magance matsalar da ba za ta kai girman haka ba. Kowa ya ga yadda Gwamnati ke tura babban kason kasafin kudi a duk shekara ta fannin tsaro, amma sam kwalliya ba ta biyan kudin sabulu. Don haka, matukar ana so a kawo karshen matsalolin tsaro a kasa baki daya, wajibi ne a fito da shirin ba sani ba sabo, kuma a yi tsayuwa irin ta masu daka wajen ganin an kakkabe bata garin da ke cikin al’umma.

Hukumar tsaro ta farin kaya DSS da hukumar tsaro ta sirri SSS Da hukumar leken asiri ta kasa, da hukumar ‘yansanda da Sojojin kasa da na sama da na ruwa da hukumar Cibil Defence, da hukumar hana fasa kwauri ta kasa Customs da hukumar kula da shige da fice ta kasa Immigration, da duk wata hukuma da tsaron kasa ya rataya a wuyansu, ya zama wajibi su kara kaimi wajen kiyaye nauyin da ya rataya a wuyansu nan tsaron rayuka da dukiyoyin jama’ar kasa.

Domin ba su da wata kasa sai Nijeriya, idan Nijeriya ta durkushe su ma sun durkushe.

A karshe ina sake jinjina wa jami’an tsaron da su ke hana idanuwansu bacci domin gudanar da ayyukan su na yau da kullum har suka kakkabe bata gari daga yankin Abuja. Muna fata, za su kara kaimi wajen fadada Ayyukan su, a jihohin Sakkwato da Zamfara da Katsina da Kaduna.

Allah ya taimaki kauyukanmu da mazabunmu da kananan hukumominmu Gundumarmu da Jiharmu da Arewacin Nijeriya da Kasa baki daya. Amin.

Comrade Adamu Yunusa Ibrahim, Malami a Cibiyar Nazarin Hausa, Jami’ar Usmanu Danfodiyo, Sakkwato, Nijeriya.

Nuruddeen Muhammad Funtua:

A gaskiya wannan nasara muna matukar godiya ga Allah (S.W.A.) muna addu’a a gare su bisa wannan namijin kokari da suke yi Allah ya cigaba da basu nasara ya kuma kiyaye manasu a duk inda suke Allah ya kawo mana karshen wannan tashe-tashen hankula aduk fadin Nijeriya baki daya Ameen ya Hayyul kayum.

Yusuf Muhammad Jalingo:

Mude muna kara kalubalantan gwamnati da masu ruwa da tsaki wajen yadda ‘yan jarida suke kokarin nemo labarai wanda har za su iya kutsawa jeji su bankado inda ‘yan ta’adda suke su dauko labarai to haka muke so jami’an tsaro suma suyi haka ko fiye da haka wajen kaiwa ‘yan ta’adda hari da kuma dakile duk wani hari nasu, sai dai jami’an tsaro suna kokari, Allah ya kara lalata shirin masu sharri, Amiin.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: 'Yan ta'addaAbujadajiJami'an TsaroRa'ayi Riga
ShareTweetSendShare
Previous Post

Makarantar ‘Aram Mamu Academy’ Ta Yi Bikin Yaye Dalibai Karo Na Uku

Next Post

Daga Soyayyar Wata Yarinya Na Fara Waka —Abba Ganga

Related

Gwamna Umar Namadi Ya Dauki Matakan Kai Jihar Jigawa Babban Matsayi
Rahotonni

Gwamna Umar Namadi Ya Dauki Matakan Kai Jihar Jigawa Babban Matsayi

4 weeks ago
Janar Tiani Ya Fara Sabon Mulkin Shekaru Biyar A Nijar
Rahotonni

Ficewar Kasar Nijar Daga Rundunar Hadin Gwiwa Ta Kasa Da Kasa Barazana Ce Ga Tsaro -Hedikwatar Tsaro

1 month ago
An Gudanar Da Taron Zaman Lafiya Tsakanin Manoma Da Makiyaya
Rahotonni

An Gudanar Da Taron Zaman Lafiya Tsakanin Manoma Da Makiyaya

1 month ago
Donald Trump Zai Gurfana A Gaban Kotu Kan Tuhumar Da Ake Masa
Rahotonni

Amurka Ta Sayi Kayayyakin Nijeriya Na Dala Miliyan 643 A Wata 2 – Rahoto

1 month ago
Gwamnoni 20 Na Fuskantar Matsin Lambar NULGE Kan Rashin Aiwatar Da Mafi Karanci Albashi
Rahotonni

Gwamnoni 20 Na Fuskantar Matsin Lambar NULGE Kan Rashin Aiwatar Da Mafi Karanci Albashi

1 month ago
Tinubu
Manyan Labarai

Yadda Tinubu Ya Shirya Wa Kansa Mafitar Siyasa Kafin Zaben 2027

2 months ago
Next Post
Daga Soyayyar Wata Yarinya Na Fara Waka —Abba Ganga

Daga Soyayyar Wata Yarinya Na Fara Waka —Abba Ganga

LABARAI MASU NASABA

Gwamnatin Tarayya Da Majalisar Dokoki Za Su Haɗa  Gwiwa Kan Sake Duba Dokar Laifukan Intanet — Minista

Gwamnatin Tarayya Da Majalisar Dokoki Za Su Haɗa  Gwiwa Kan Sake Duba Dokar Laifukan Intanet — Minista

May 14, 2025
Yadda Kasar Sin Ke Kokarin Gina Tashar Bincike A Sama Da Tubalin Kasar Duniyar Wata

Yadda Kasar Sin Ke Kokarin Gina Tashar Bincike A Sama Da Tubalin Kasar Duniyar Wata

May 14, 2025
gaza

Kasafin Kudi Na Naira Tiriliyan 1.78 Na Abuja Ya Tsallake Karatu Na Biyu A Majalisa

May 14, 2025
Kasar Sin Za Ta Inganta Cikakken Tsarin Fitar Da Ma’adanai Zuwa Ketare Don Kiyaye Tsaron Kasa

Kasar Sin Za Ta Inganta Cikakken Tsarin Fitar Da Ma’adanai Zuwa Ketare Don Kiyaye Tsaron Kasa

May 14, 2025
Tinubu Ya Yaba Wa Sule Lamiɗo A Taron Ƙaddamar Da Littafin Tarihin Rayuwasa

Tinubu Ya Yaba Wa Sule Lamiɗo A Taron Ƙaddamar Da Littafin Tarihin Rayuwasa

May 14, 2025
Manyan Ayyuka Guda Biyar Za Su Raya Makomar Al’ummomin Kasar Sin Da kasashen Latin Amurka Da Caribbean Ta Bai Daya

Manyan Ayyuka Guda Biyar Za Su Raya Makomar Al’ummomin Kasar Sin Da kasashen Latin Amurka Da Caribbean Ta Bai Daya

May 14, 2025
Yadda Aka Gina Ofishin ‘Yansanda Na Zamani A Abuja

Yadda Aka Gina Ofishin ‘Yansanda Na Zamani A Abuja

May 14, 2025
JAMB Ta Amince Da Maki 140 Da 100 Mafi Karancin Maki Na Shiga Manyan Makarantu

JAMB: Tangarɗar Na’ura Ne Ya Haifar Da Gagarumar Koma Baya A Sakamakon UTME Na 2025

May 14, 2025
A Sa Hikima Da Dabara Yayin Da Ake “Wasan Kati ” Da Kasar Amurka

A Sa Hikima Da Dabara Yayin Da Ake “Wasan Kati ” Da Kasar Amurka

May 14, 2025
Ɗan Wasan Super Eagles Na Tsaka Mai Wuya Bayan An Yi Masa Tiyata

Ɗan Wasan Super Eagles Na Tsaka Mai Wuya Bayan An Yi Masa Tiyata

May 14, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.