ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Thursday, June 25, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Ra’ayoyinku A Kan Nasarorin Da Jami’an Tsaro Ke Samu Kan ‘Yanta’dda A Dazukan Abuja

by Aisha Seyoji
4 years ago

A wannan makon mun kawo ra’ayoyinku ne a kan nasarorin da jami’an tsaro suka samu na fatattakar ‘yan ta’adda a yankin Abuja tun bayan umarnin da Shugaba Buhari ya bayar kwanakin baya, bayan da aka Kai wa rundunar da ke tsaronsa hari.

Omar Naseer Imam:

Masha Allah, Muna taya su da addu’a sosai kuma muna fatan wannan nasarar ya game Nijeriya gaba daya kananan jami’an tsaro suna kokari sosai sun bada ransu da duk wani farin cikinsu muna masu fatan alkhairi a koda yaushe.

ADVERTISEMENT
  • Salman Rushdie: Wanda Ya Yi Batanci Ga Annabi Na Cikin Mawuyacin Hali Bayan Kai Masa Hari
  • Obasanjo Ya Roki Marayun Borno Su Yafe Wa ‘Yan Ta’addar Da Suka Kashe Iyayensu

Sulaiman Muhammad:

To aikuwa har yandu akwai matsala saboda ba a bin su inda suke zaune a cikin dajin kamar yadda suke kaiwa jama’a hari dare da rana suma haka ya kamata a yi musu da tuntuni an gama da wannan matsalar.

LABARAI MASU NASABA

An Nemi Shugabanni Su Rungumi Tafarkin Adalci A Tsakanin Al’ummunsu

Ƴan Bindiga Sun Tilasta Wa Ƙauyukan Sakkwato Biyan Sabon Haraji

It’z Sam Dambatta:

Babu abinda za mu ce sai dai godiya ga Allah (SWT) bisa wannan nasara da aka samu, Sannan muna kara jinjina ga jami’an tsaro bisa wannan aiki da sukai dama munsan za su iya sai dai idan ba a sa su ba. Sannan muna kara tawassali da sunayen Allah na Alhayyu Alkayyum da ya kara inganta mana zaman lafiya da tsaro a kasarmu baki daya.

Umar Bello Ubd:

Abin a yaba musu ne amma mu dama laifinsu muke gani saboda an basu kayan aiki kamar mutoci na shiga daji da bindigogi da nauran gano inda suke.

It’z Jameel Moh’d:

Allah sarki kasata Nijeriya gaskiya muna cikin wani hali Allah ya kawo mana dauki cikin sauki ana kashe bayin Allah wanda ba su ji basu gani ba, ‘yan ta,adda suna daji daina kashe bayin Allah ashe ‘yan ta’adda ne saboda kowa ya sani cewa inda gaske suke yi sun san inda suke suje a ranar daya su gama da su.

Muhd Basheer Sa’ad:

Alhamdulillah Masha Allah!, wannan umarni da aka bawa jami’ai na fatattakar ‘yan ta’adda ya yi amfani sosai kuma Allah ya basu nasara, da ace gwamnati za ta basu dama kamar yadda ta basu a yanzun da to shakka babu za a samu nasara. Gwamnati bata damu da talakawa ba shi ne magana kawai.

Adamu Yunusa Ibrahim:

Tabbas abin a yaba wa hukumomin tsaro ne, domin sun kusa yin sake. Da a ce tun farko ana iya magance matsalar da ba za ta kai girman haka ba. Kowa ya ga yadda Gwamnati ke tura babban kason kasafin kudi a duk shekara ta fannin tsaro, amma sam kwalliya ba ta biyan kudin sabulu. Don haka, matukar ana so a kawo karshen matsalolin tsaro a kasa baki daya, wajibi ne a fito da shirin ba sani ba sabo, kuma a yi tsayuwa irin ta masu daka wajen ganin an kakkabe bata garin da ke cikin al’umma.

Hukumar tsaro ta farin kaya DSS da hukumar tsaro ta sirri SSS Da hukumar leken asiri ta kasa, da hukumar ‘yansanda da Sojojin kasa da na sama da na ruwa da hukumar Cibil Defence, da hukumar hana fasa kwauri ta kasa Customs da hukumar kula da shige da fice ta kasa Immigration, da duk wata hukuma da tsaron kasa ya rataya a wuyansu, ya zama wajibi su kara kaimi wajen kiyaye nauyin da ya rataya a wuyansu nan tsaron rayuka da dukiyoyin jama’ar kasa.

Domin ba su da wata kasa sai Nijeriya, idan Nijeriya ta durkushe su ma sun durkushe.

A karshe ina sake jinjina wa jami’an tsaron da su ke hana idanuwansu bacci domin gudanar da ayyukan su na yau da kullum har suka kakkabe bata gari daga yankin Abuja. Muna fata, za su kara kaimi wajen fadada Ayyukan su, a jihohin Sakkwato da Zamfara da Katsina da Kaduna.

Allah ya taimaki kauyukanmu da mazabunmu da kananan hukumominmu Gundumarmu da Jiharmu da Arewacin Nijeriya da Kasa baki daya. Amin.

Comrade Adamu Yunusa Ibrahim, Malami a Cibiyar Nazarin Hausa, Jami’ar Usmanu Danfodiyo, Sakkwato, Nijeriya.

Nuruddeen Muhammad Funtua:

A gaskiya wannan nasara muna matukar godiya ga Allah (S.W.A.) muna addu’a a gare su bisa wannan namijin kokari da suke yi Allah ya cigaba da basu nasara ya kuma kiyaye manasu a duk inda suke Allah ya kawo mana karshen wannan tashe-tashen hankula aduk fadin Nijeriya baki daya Ameen ya Hayyul kayum.

Yusuf Muhammad Jalingo:

Mude muna kara kalubalantan gwamnati da masu ruwa da tsaki wajen yadda ‘yan jarida suke kokarin nemo labarai wanda har za su iya kutsawa jeji su bankado inda ‘yan ta’adda suke su dauko labarai to haka muke so jami’an tsaro suma suyi haka ko fiye da haka wajen kaiwa ‘yan ta’adda hari da kuma dakile duk wani hari nasu, sai dai jami’an tsaro suna kokari, Allah ya kara lalata shirin masu sharri, Amiin.

Aisha Seyoji
+ postsBio
  • Aisha Seyoji
    https://hausa.leadership.ng/author/aisha-seyoji/
    Mata Mu Kara Hakuri A Zamantakewar Aure -Aisha Seyoji
  • Aisha Seyoji
    https://hausa.leadership.ng/author/aisha-seyoji/
    Wa Suka Fi Cancanta A Nada Ministocin Tinubu?
  • Aisha Seyoji
    https://hausa.leadership.ng/author/aisha-seyoji/
    Ra’ayoyinku A Kan Ba Da Bashi Ga Daliban Manyan Makarantu
  • Aisha Seyoji
    https://hausa.leadership.ng/author/aisha-seyoji/
    Abin Haushi, Mata Sun Mayar Da Maza Tamkar Bola

MASU ALAKA

Nijeriya
Rahotonni

An Nemi Shugabanni Su Rungumi Tafarkin Adalci A Tsakanin Al’ummunsu

June 20, 2026
Ambaliyar Ruwa Ta Lalata Gidaje 14,940 A Sokoto
Rahotonni

Ƴan Bindiga Sun Tilasta Wa Ƙauyukan Sakkwato Biyan Sabon Haraji

June 20, 2026
IMF
Rahotonni

Tattalin Arziƙin Ƙasa: Masana Sun Buƙaci Tinubu Ya Yi Hattara Da Shawarar IMF

June 20, 2026
Next Post
Daga Soyayyar Wata Yarinya Na Fara Waka —Abba Ganga

Daga Soyayyar Wata Yarinya Na Fara Waka —Abba Ganga

LABARAI MASU NASABA

Ndume Ya Bayyana Dalilin Da Ya Sa Yake Goyon Bayan Ƙudirin Kafa ‘Yansandan Jihohi

Ndume Ya Bayyana Dalilin Da Ya Sa Yake Goyon Bayan Ƙudirin Kafa ‘Yansandan Jihohi

June 25, 2026
EFCC Za Ta Gurfanar Da Shugaban Miyetti Allah Kan Zargin Almundahanar Dala Miliyan 2.53

EFCC Za Ta Gurfanar Da Shugaban Miyetti Allah Kan Zargin Almundahanar Dala Miliyan 2.53

June 25, 2026
Maroko Ta Zama Ƙasa Ta Farko Daga Afirka Da Ta Tsallaka Zuwa Zagaye Na 32 A Gasar Kofin Duniya

Maroko Ta Zama Ƙasa Ta Farko Daga Afirka Da Ta Tsallaka Zuwa Zagaye Na 32 A Gasar Kofin Duniya

June 25, 2026
Zan Ware 10bn Don Inganta Ilimin Matasa Idan Na Ci Zabe – Atiku

‘Yan Nijeriya Ba Sa Bukatar ‘Yan Jarida Su Faɗa Musu Suna Jin Yunwa — Atiku

June 25, 2026
Dokar Sin Ta Gurfanar Da Masu Rajin Ballewar Kabilun Kasar Da Ke Kasashen Waje Ta Dace

Dokar Sin Ta Gurfanar Da Masu Rajin Ballewar Kabilun Kasar Da Ke Kasashen Waje Ta Dace

June 24, 2026
’Yan Kasuwa Na Kasashen Waje Sun Yaba Wa Yanayin Kasuwanci Na Sin

’Yan Kasuwa Na Kasashen Waje Sun Yaba Wa Yanayin Kasuwanci Na Sin

June 24, 2026
Yadda Uba Sani Ya Farfaɗo Da Asibitin Da Aka Yi Watsi Da Shi Tsawon Shekaru 40 – Hakimin Makarfi

Yadda Uba Sani Ya Farfaɗo Da Asibitin Da Aka Yi Watsi Da Shi Tsawon Shekaru 40 – Hakimin Makarfi

June 24, 2026
Dandalin DAVOS Na Bana: Fage Ne Da “Kirkire-Kirkiren Sin” Ya Sadu Da “Kyakkyawan Fatan Afirka”

Dandalin DAVOS Na Bana: Fage Ne Da “Kirkire-Kirkiren Sin” Ya Sadu Da “Kyakkyawan Fatan Afirka”

June 24, 2026
Binciken CGTN: Amfanarwa A Aikace Shi Ne Nagartaccen Ma’aunin Tantance Ainihin Kimar Sabbin Fasahohi

Binciken CGTN: Amfanarwa A Aikace Shi Ne Nagartaccen Ma’aunin Tantance Ainihin Kimar Sabbin Fasahohi

June 24, 2026
Kasar Sin Na Kara Zama Babban Ginshikin Ci Gaban Tattalin Arzikin Duniya Na Gaba

Kasar Sin Na Kara Zama Babban Ginshikin Ci Gaban Tattalin Arzikin Duniya Na Gaba

June 24, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.