ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Monday, December 22, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Ranar Jin Kai Ta Duniya (2024): Kiran Gaggawa A Kan Ceton Rayuka

by Leadership Hausa
1 year ago
jin kai

Kowace shekara, Ranar Jin Kai Ta Duniya (WHD) tana zama ranar tunatarwa mai amfani game da muhimmancin ayyukan jin kai a duniya. A wannan shekara, taken shi ne, #ActForHumanity’ ya jaddada alhakin gamayya da muke da shi na kare fararen hula da ma’aikatan jin qai da ke yi musu hidima a cikin rikice-rikicen duniya. 

A yayin da muke bikin wannan rana a ranar 19 ga Agusta, yana da matukar muhimmanci a yi tunani a kan manyan abubuwan da ke tattare da tashe-tashen hankula da ke faruwa, da kuma tsananin bukatar shugabannin kasashen duniya su dauki kwararan matakai. 

Rikice-rikice a duniya tun daga Gaza zuwa Sudan na ci gaba da yin barna ga fararen hula. Canjin yanayi kuma yana kara haifar da bukatun jin kai.

ADVERTISEMENT

A Arewa maso Gabas na Nijeriya, rikicin da aka dade ana yi ya haifar da munanan matsalolin jin kai, da raba miliyoyin mutane daga iyalensu, da kawo cikas ga rayuwa da kuma kara tabarbarewar karancin abinci da rashin abinci mai gina jiki.

A shekarar 2024 kadai, mutane miliyan 8.1 na bukatar agajin jin kai a jihohin Borno, Adamawa da Yobe (BAY) dake Arewa maso Gabas na Nijeriya. Wannan ya hada da ‘yan gudun hijira miliyan 2.1 (IDPs) da kuma mutane miliyan 4.1 a cikin al’ummomin da suka karbi bakuncin. Abokan aikin jin kai tare da gwamnatin Nijeriya na da burin kai wa mutane miliyan 4.4 na waxannan mutane agajin abinci, ruwa, matsuguni da sauran agajin gaggawa.

LABARAI MASU NASABA

Majalisar Dinkin Duniya Ta Amince Da Wata Sabuwar Yarjejeniya Domin Inganta Tsarin Shugabancin Duniya

Hukuma Ta Koka Da Yadda Masu Mulki Ke Tauye Hakkin Al’umma

jin kai

A Jihar Borno, Anna Monday, mai ‘ya’ya hudu, ta jure mawuyacin halin da ake ciki na gudun hijira. An tilasta mata fita daga gidanta zuwa cibiyar koyo na wucin gadi a cibiyar karbar baki a Pulka, wurin da aka tsara don masauki na dan lokaci amma yanzu mafaka na dogon lokaci ga mutane da yawa. Kimanin mata 30 ne ke kwana a cikin matsugunin yayin da mazan ke kwana a waje, lamarin da ke nuna rashin isasshen wurin kwana.

Amina Buba, mai ‘ya’ya hudu, ta yi gudun hijira daga kauyensu da ke Jihar Adamawa sakamakon munanan hare-haren da kungiyoyin ‘yan ta’adda’ suka kai musu. Gidanta ya kone, wanda hakan ya tilastawa ‘yan uwanta gudu da kaya a bayansu.

A sansanin ‘yan gudun hijira, Amina na kokawa don samun isassun abinci da ruwan sha mai tsafta ga ‘ya’yanta.

jin kai

Wata yarinya ‘yar Jihar Yobe mai suna Fatima Mohammadu ta rabu da danginta a wani hari da aka kai kauyensu. Masu aikin jin kai ne suka same ta suka kawo ta sansanin IDP.

Tausayin rabuwa da rashin ‘yan uwanta ya haifar da tabo mai zurfi. A sansanin, tana fuskantar kalubale kamar rashin samun ilimi da rashin isasshen abinci mai gina jiki.

Mata da maza har da yara a fadin Nijeriya sun gamu da rikicin kabilanci, matsalar yanayi ko wahalhalu. Mata da yara, galibi suna shan wahala mafi muni sakamakon tauye hakkinsu, gami da cin zarafin mata.

Hadin kai na rashin tsaro, karancin isa ga mutanen da abin ya shafa, da rashin isassun kudi da albarkatu suna kawo cikas ga isar da muhimman ayyuka, yana barin miliyoyin mutane cikin bukatun jin kai.

A Arewa maso Gabas na Nijeriya, hare-hare kan fararen hula da ma’aikatan jin kai ya zama ruwan dare gama-gari tare da keta dokokin jin kai na kasa da kasa.

A ranar 29 ga watan Yuni, ga misali, fararen hula da dama ne suka mutu, wasu da dama kuma suka jikkata a wasu hare-haren kunar bakin wake da aka kai a Gwoza, Borno. Bayan wata guda, iyalai da dama sun rasa ‘yan uwansu a wani harin kunar bakin wake da aka kai a Konduga, shi ma a Borno. Wadannan al’amura sun nuna ci gaba da barazana ga rayuwar fararen hula a cikin rikice-rikice, da kuma nuna bukatar gaggawa na inganta matakan kariya, ciki har da tsauraran ka’idojin kasa da kasa da kuma bukatar a ba da cikakken bayani game da cin zarafi.

Kowace rana, ma’aikatan jin kai, daga gwamnati, kungiyoyi masu zaman kansu, Majalisar Dinkin Duniya (UN), kungiyoyin jama’a, ma’aikatan Nijeriya da na duniya suna ba da gudummawa don ceton rayuka da dawo da mutane. Al’ummomin da suka karbi bakuncin suna karbar mutanen da ke cikin gida duk da cewa ba su da abin da za su raba saboda bil’adama.

  • Babban Kwamandan Boko Haram Da Wasu Mutane 9 Sun Mika Wuya Ga Sojoji A Borno

Ranar Jin Kai Ta Duniya ta fi dacewa fiye da kowane lokaci. Duniya ba ta taba ganin bukatar jin kai da ta fi girma ba. Adadin mutanen da ke fama da rikici da sauran rikice-rikicen jin kai na da yawa. Ba a tava samun bukatu na gaggawa na kare fararen hula ba, da kuma gane muhimmiyar rawar da ma’aikatan agaji ke takawa.

Shugabannin duniya da vangarorin da ke fama da rikici suna da muhimmiyar rawar da za su taka wajen magance rikice-rikice da kuma kare ma’aikatan jin kai. Ba wai kawai su yi Allah wadai da keta dokokin jin kai na kasa da kasa ba, har ma su dauki kwararan matakai don hukunta wadanda ke da hannu a cikin laifuffukan.

Godiya ga kudade daga masu ba da gudummawa, masu ba da agaji suna isa ga miliyoyin mutane kowace shekara tare da taimakon ceton rai. Amma suna bukatar kwakkwaran tallafi don ci gaba da gudanar da muhimman ayyukansu na tallafawa kokarin gwamnati. Wannan ya hada da albarkatun kudi, samun damar jin kai, da kyakkyawar niyya ta siyasa.

A yau, kashi daya bisa hudu na albarkatun da ake bukata don magance bukatun jin kai na gaggawa a duniya da kuma a Arewa maso Gabashin Nijeriya ne aka samu. Idan ba tare da wadannan albarkatu ba, ba za mu iya tallafawa Anna, Amina, da Fatima don tsira da sake gina rayuwarsu ba.

Bayan ayyukan jin kai, ayyukan da suka shafi ci gaba suna da mahimmanci yayin da bukatun jin kai kuma suka samo asali ne daga rashin ayyukan yau da kullum, rashin wadatar rayuwa, da rashin samun aikin yi ga matasa.

Taken #ActFor Humanity” ba kawai take ba ne; kira ne zuwa ga aiki ba. Yana nufin kowane dayanmu ya tashi tsaye game da wadanda ba za su iya tsayawa kansu ba, don yin magana game da rashin adalci, da aiki zuwa duniyar da ake mutunta ka’idojin jin kai, kuma ana kiyaye rayuka.

A wannan Ranar Taimakon Jama’a ta Duniya, dukanmu mu yi alkawarin yin aiki don dan’adam, na yau da kuma na gaba.

Na yi imani cewa za ku tsaya tare da ni don ba da hadin kai ga mutanen da rikici da bala’i ya shafa da kuma jajirtattun maza da mata wadanda ke ba da taimako. Bai kamata su zama abin tashin hankali ba amma dole ne a kiyaye su ko ta wani hanya.

 Mohamed Malick Fall shi ne mai kula da ayyukan jin kai na Majalisar Dinkin Duniya a Nijeriya.

 

ShareTweetSendShare

MASU ALAKA

Majalisar Dinkin Duniya Ta Amince Da Wata Sabuwar Yarjejeniya Domin Inganta Tsarin Shugabancin Duniya
Makala

Majalisar Dinkin Duniya Ta Amince Da Wata Sabuwar Yarjejeniya Domin Inganta Tsarin Shugabancin Duniya

September 24, 2024
Hukuma Ta Koka Da Yadda Masu Mulki Ke Tauye Hakkin Al’umma
Labarai

Hukuma Ta Koka Da Yadda Masu Mulki Ke Tauye Hakkin Al’umma

June 14, 2024
Hadiza Bala Usman Ta Gargadi Masu Gangamin Bata Mata Suna
Makala

Hadiza Bala Usman Ta Gargadi Masu Gangamin Bata Mata Suna

June 23, 2023
Next Post
Karfafa Hadin Gwiwar Tattalin Arziki Da Cinikayya Tsakanin Sin Da Vietnam

Karfafa Hadin Gwiwar Tattalin Arziki Da Cinikayya Tsakanin Sin Da Vietnam

LABARAI MASU NASABA

Gwamnatin Tarayya Ta Tabbatar Da Ceton Dukkan Ɗalibai 230 Da Aka Sace A Neja

Gwamnatin Tarayya Ta Tabbatar Da Ceton Dukkan Ɗalibai 230 Da Aka Sace A Neja

December 22, 2025
Gobara Ta Haddasa Mummunar Asara A Kasuwar Kayan Katako A Kano

Gobara Ta Haddasa Mummunar Asara A Kasuwar Kayan Katako A Kano

December 22, 2025
An Sako Ragowar Ɗalibai Da Malamai Da Aka Sace A Makarantar Katolika Ta Neja

An Sako Ragowar Ɗalibai Da Malamai Da Aka Sace A Makarantar Katolika Ta Neja

December 21, 2025
Raphinha Da Yamal Sun Ci Ƙwallaye Yayin Da Barcelona Ta Doke Villarreal

Raphinha Da Yamal Sun Ci Ƙwallaye Yayin Da Barcelona Ta Doke Villarreal

December 21, 2025
Davido Zai Raƙashe A Bikin Buɗe Gasar AFCON 2025 A Morocco

Davido Zai Raƙashe A Bikin Buɗe Gasar AFCON 2025 A Morocco

December 21, 2025
Yankin Rijiyoyin Mai Na Teku Mafi Girma Na Kasar Sin Ya Ba Da Rahoton Yawan Mai Da Iskar Gas Da Ya Fitar A Shekara

Yankin Rijiyoyin Mai Na Teku Mafi Girma Na Kasar Sin Ya Ba Da Rahoton Yawan Mai Da Iskar Gas Da Ya Fitar A Shekara

December 21, 2025
An Bukaci Bunkasa Fannin Kiwo A Hadin Gwiwar Sin Da Afirka

An Bukaci Bunkasa Fannin Kiwo A Hadin Gwiwar Sin Da Afirka

December 21, 2025
Akpabio, Ganduje, Ogundoyin Sun Halarci Naɗa Seyi Tinubu Sarauta

Akpabio, Ganduje, Ogundoyin Sun Halarci Naɗa Seyi Tinubu Sarauta

December 21, 2025
Tashar Teku Ta Ciniki Mai ‘Yanci Ta Hainan Ta Bude Sabon Babin Hadin Gwiwar Sin Da Kasashen Afirka

Tashar Teku Ta Ciniki Mai ‘Yanci Ta Hainan Ta Bude Sabon Babin Hadin Gwiwar Sin Da Kasashen Afirka

December 21, 2025
Tinubu

Dambarwar Naɗa Muƙamai Da Soke Su A Gwamnatin Tinubu

December 21, 2025

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.