• English
  • Business News
Sunday, July 6, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Ranar Lafiyar Ƙwaƙwalwa Ta Duniya: Majalisar Ɗinkin Duniya Ta Horas Da ‘Yan Jarida A Abuja

Akwai 'Yan Nijeriya Miliyan 20 Da Ke Fama Da Matsalar Ƙwakwalwa

by yahuzajere
2 years ago
in Labarai
0
Ranar Lafiyar Ƙwaƙwalwa Ta Duniya: Majalisar Ɗinkin Duniya Ta Horas Da ‘Yan Jarida A Abuja

Dandazon 'yan jaridar da aka horas tare da kwararrun da suka bayar da horo bayan kammala horaswar a ranar Talata

Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Majalisar Ɗinkin Duniya ta shirya horaswa ta musamman ga ‘yan jarida daga ɓangarori daban-daban a kan muhimmancin kula da lafiyar ƙwaƙwalwa domin taimaka wa wayar da kan jama’a game da abubuwan da ke shafar lafiyar ƙwaƙwalwa da yadda za a magance su ko a rage kaifinsu.

A yayin horaswar masana daban-daban sun gabatar da ƙasidu da suka yi bayani game da ‘yancin Ɗan’adam wajen samun kiwon lafiyar ƙwaƙwalwa da muhimmancin abin da matakan riga-kafin kamuwa da cututtukan da suka shafi ƙwaƙwalwa.

  • Majalisar Dinkin Duniya Ta Jaddada ‘Yancin Dan Adam Wajen Samun Kiwon Lafiyar Kwakwalwa
  • Kisan Dan Jarida: ‘Yansandan Sun Kama Wadanda ake Zargi Da Hannu A Zamfara

Bugu da ƙari an horas da ‘yan jaridan a kan alaƙar aikinsu da kiwon lafiyar ƙwaƙwalwa da yadda ya kamata su riƙa bayar da rahotannin da suka shafi kiwon lafiyar ƙwaƙwalwa cikin ƙwarewa da tausayawa.

Wakazalika, an aiwatar da wasu tsare-tsare na gwajin lafiyar ƙwaƙwalwar mahalartan domin kowa ya san matsayinsa da irin matakan da suka kamata mutum ya ɗauka domin daidaita rayuwarsa ta yadda ba za ta haifar masa da matsalar ƙwaƙwalwa ba.

ƙwaƙwalwa

Labarai Masu Nasaba

‘Yan Adawa Sun Dunkule A ADC Don Tunkarar Tinubu A 2027

Ku Manta Da 2027, Tinubu Zai Ci Gaba Da Mulki Har 2031 — Fadar Shugaban Ƙasa Ga ADC

An fara gabatar da bikin ranar kiwon lafiyar ƙwaƙwalwa ne a ranar 10 ga watan Oktobar 1992 ta hannun Ƙungiyar Kula da Lafiyar Ƙwaƙwalwa ta Duniya bisa goyon bayan Hukumar Lafiya ta Duniya da sauransu.

A saƙonsa na bikin ranar ta bana, Sakatare Janar na Majalisar Ɗinkin Duniya, Antonio Guterres ya bayyana cewa, lafiyar ƙwaƙwalwa da tunani mai kyau yana ba Ɗan’adam damar gudanar da rayuwa mai gamsarwa da ba da gudummawa sosai ga al’ummomi.

Ya nuna takaicinta cewa, daya cikin mutane takwas a duniya na fama da matsalar lafiyar ƙwaƙwalwa, wanda hakan ya fi ƙamari cikin ‘yan mata da matasa.

ƙwaƙwalwa

Bugu da ƙari, mutum uku cikin mutane huɗu da ke fama da matsalar ƙwaƙwalwa, ba su samun isasshiyar kulawa ko kuma babu kulawa ma kwata-kwata, sannan da yawa suna fuskantar ƙyama da wariya a cikin al’umma.

“Kiyaye Lafiyar ƙwaƙwalwa ba gata ba ce ta wane da wane, haƙƙi ce ta dukkan Ɗan’adam– ya zama dole a kula da Lafiyar ƙwaƙwalwa a duk cikin al’ummatai da ke cikin faɗin duniyarmu. Dole ne gwamnatoci su ba da kulawa don magani ga masu matsalar ƙwaƙwalwa da kuma kiyaye hakkinsu.

“Dole ne kuma a magance matsalar cin zarafi tare da karya duk wani shingen da ke hana mutane neman tallafi don magance matsalar ƙwaƙwalwa kuma dole ne mu magance matsalar ƙwaƙwalwa tun daga tushe musamman ta fuskar talauci, wariya, tashin hankali da sauransu.

“A wannan rana ta kula da Kiwon Lafiyar Hankali ta Duniya, muna sake jaddada cewa, kiyaye lafiyar ƙwaƙwalwa, hakki ce kuma ‘yancin Ɗan’adam ne ba tare da nuna wata wariya ba, tare za mu gina duniya mafi ƙoshin lafiya inda kowa zai yi alfahari da ita” in ji ji sakataren majalisar.

ƙwaƙwalwa

Wata ƙididdiga da wata ƙwararriyar da ta yi lacca a taron horas da ‘yan jaridar, Mrs. Moji Makanjuola ta bayyana, ta nunar da cewa akwai ‘Yan Nijeriya aƙalla miliyan 20 da ke fama da rashin lafiyar ƙwaƙwalwa, sannan du-du-du asibitocin da ke kula da masu matsalar ƙwaƙwalwa na gwamnati ba su wuce guda takwas ba, da na masu zaman kansu guda 30, kana likitocin ƙwaƙwalwa 350 ne kacal ake da su a duk faɗin Nijeriya.

 

 

 


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: 'Yan JaridaBikihoraswaRanar kiwon lafiyar kwakwalwaTaro
ShareTweetSendShare
Previous Post

Rikicin Sudan: Gwamna Lawal Ya Samar Da Agajin Ggaggawa Ga Daliban Zamfara 66

Next Post

Alkalan Wasan Firimiya Sun Dauki Matakan Guje Wa Kuskure Dangane Da Na’urar VAR

Related

‘Yan Adawa Sun Dunkule A ADC Don Tunkarar Tinubu A 2027
Labarai

‘Yan Adawa Sun Dunkule A ADC Don Tunkarar Tinubu A 2027

4 hours ago
Ku Manta Da 2027, Tinubu Zai Ci Gaba Da Mulki Har 2031 — Fadar Shugaban Ƙasa Ga ADC
Manyan Labarai

Ku Manta Da 2027, Tinubu Zai Ci Gaba Da Mulki Har 2031 — Fadar Shugaban Ƙasa Ga ADC

4 hours ago
ALGON Ta Taya Gwamnan Sani Murnar Samun Lambar Yabo Ta Kasa
Labarai

ALGON Ta Taya Gwamnan Sani Murnar Samun Lambar Yabo Ta Kasa

12 hours ago
Kwankwaso Ba Zai Sake Yi Mana Takarar Shugabancin Ƙasa Ba A Zaɓen 2027 Ba – NNPP
Manyan Labarai

Kwankwaso Ba Zai Sake Yi Mana Takarar Shugabancin Ƙasa Ba A Zaɓen 2027 Ba – NNPP

12 hours ago
An Yi Wa ‘Yar Shekara 18 Fyade Har Lahira A Taraba
Kotu Da Ɗansanda

An Kama Matashin Da Ya Yi Garkuwa Da Abokinsa Tare Da Karbar Kudin Fansa

15 hours ago
Gwamna Ademola Adeleke Ya Ƙaryata Jita-Jitar Sauya Sheƙa Daga PDP Zuwa APC
Manyan Labarai

Gwamna Ademola Adeleke Ya Ƙaryata Jita-Jitar Sauya Sheƙa Daga PDP Zuwa APC

15 hours ago
Next Post
Alkalan Wasan Firimiya Sun Dauki Matakan Guje Wa Kuskure Dangane Da Na’urar VAR

Alkalan Wasan Firimiya Sun Dauki Matakan Guje Wa Kuskure Dangane Da Na'urar VAR

LABARAI MASU NASABA

Wang Yi: Amfani Da Karfin Soji Ba Bisa Ka’ida Ba Na Ingiza Karuwar Tashin Hankali

Wang Yi: Amfani Da Karfin Soji Ba Bisa Ka’ida Ba Na Ingiza Karuwar Tashin Hankali

July 5, 2025
Shawarar Ziri Daya Da Hanya Daya Na Cike Da Hangen Nesa Da Burikan Samar Da Ci Gaba In Ji Firaministan Kasar Senegal

Shawarar Ziri Daya Da Hanya Daya Na Cike Da Hangen Nesa Da Burikan Samar Da Ci Gaba In Ji Firaministan Kasar Senegal

July 5, 2025
‘Yan Adawa Sun Dunkule A ADC Don Tunkarar Tinubu A 2027

‘Yan Adawa Sun Dunkule A ADC Don Tunkarar Tinubu A 2027

July 5, 2025
Wakilin Sin Ya Yi Jawabi Game Da Raya Hidimomi Ga Nakasassu Ta Hanyar Fasahar AI A Madadin Wakilan Kasashe Fiye Da 70

Wakilin Sin Ya Yi Jawabi Game Da Raya Hidimomi Ga Nakasassu Ta Hanyar Fasahar AI A Madadin Wakilan Kasashe Fiye Da 70

July 5, 2025
Ku Manta Da 2027, Tinubu Zai Ci Gaba Da Mulki Har 2031 — Fadar Shugaban Ƙasa Ga ADC

Ku Manta Da 2027, Tinubu Zai Ci Gaba Da Mulki Har 2031 — Fadar Shugaban Ƙasa Ga ADC

July 5, 2025
Zan Dade Ban Manta Da Mahaifinmu Ba -Abba Sadau

Zan Dade Ban Manta Da Mahaifinmu Ba -Abba Sadau

July 5, 2025
Kuri’ar Jin Ra’ayin Jama’a Ta CGTN Ta Nuna Goyon Baya Ga Fadadar Kungiyar BRICS A Matsayin Hanyar Bunkasa Hadin Gwiwa

Kuri’ar Jin Ra’ayin Jama’a Ta CGTN Ta Nuna Goyon Baya Ga Fadadar Kungiyar BRICS A Matsayin Hanyar Bunkasa Hadin Gwiwa

July 5, 2025
Gidajen Gala Ne Kadai Mafita Ga Masana’antar Kannywood – Falalu Dorayi

Gidajen Gala Ne Kadai Mafita Ga Masana’antar Kannywood – Falalu Dorayi

July 5, 2025
Wang Yi Da Takwaransa Na Ghana Sun Aikewa Juna Sakon Murnar Cika Shekaru 65 Da Kulla Dangantakar Diplomasiyya A Tsakanin Kasashensu

Wang Yi Da Takwaransa Na Ghana Sun Aikewa Juna Sakon Murnar Cika Shekaru 65 Da Kulla Dangantakar Diplomasiyya A Tsakanin Kasashensu

July 5, 2025
Sin Da Faransa Sun Amince Da Ingiza Cudanyar Mabanbantan Sassa Tare Da Samar Da Karin Tabbaci Ga Duniya

Sin Da Faransa Sun Amince Da Ingiza Cudanyar Mabanbantan Sassa Tare Da Samar Da Karin Tabbaci Ga Duniya

July 5, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.