ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Thursday, July 16, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Rikicin Sudan: Gwamna Lawal Ya Samar Da Agajin Ggaggawa Ga Daliban Zamfara 66

by Leadership Hausa
3 years ago
Zamfara

Gwamnan Jihar Zamfara, Dauda Lawal ya samar da hanyar jin-kai ga dalibai 66 ‘yan asalin Jihar da aka dawo da su gida daga Sudan.

Gwamnatin Jihar Zamfara ce ta tura Dalibai 66 karatu Sudan, wadanda kuma ba su kammala karatunsu ba aka dawo da su sakamakon yakin da ya kaure.

  • Dan Majalisar Wakilan APC Ya Rasu
  • Jamaica Na Neman Greenwood Ya Koma Wakiltarta A Kwallon Kasa

A wata sanarwar manema labarai da mai magana da yawun gwamnan, Sulaiman Bala Idris ya fitar, ta bayyana cewa Kwamishinan Ilimi ne ya yi karin haske ga Majalisar Zartaswar Jihar a zamanta na ranar Litinin.

ADVERTISEMENT

Ya kara da cewa, dalibai 14 cikin 66 da aka dawo da su daga Kasar ta Sudan suna gab da rubuta jarabawar karshe a fannin Jinya, kafin farawar yakin.

Sanarwar ta ci gaba da cewa: “A watan da ya gabata ne Gwamna Dauda Lawal ya bayar da umarni ga Ma’aikatar Ilimi, Kimiyya da Fasaha ta Zamfara da ta kulla yarjejeniya da hukumar gudanarwar Jami’ar Sudan domin ganin dalibai 14 ‘yan salin Zamfara sun iya rubuta jarabawarsu ta karshe a Nijeriya. Wanda a tsarin jami’ar ta Sudan, Nijeriya ba ta daga cikin cibiyoyin da za a iya yin wannan jarabawa a fadin duniya. Amma bisa jajircewa irin ta gwamnatin Zamfara ya sa suka aminta.

LABARAI MASU NASABA

Ganduje Ya Buƙaci A Yi Siyasar Aƙida Domin Inganta Dimokuraɗiyya A Nijeriya

Gwamna Dauda Lawal Zai Gabatar Da Jawabi A Taron Ƙasa Da Ƙasa Na Jami’ar FUE Zariya

“Haka kuma Gwamnatin ta Zamfara ta roki Jami’ar Usman Dan Fodio da ke Sakkwato da ta bada Asibitin Kwararru na Jami’ar domin a gudanar da wannan jarabawa. Wanda kuma Jami’ar ta Dan Fodio ta amince.

“Cikin tausayawa da jin kai irin na Gwamna Dauda Lawal ne ya dauke nauyin kudin jirgi, masauki da duk wata dawainiya ta malamai uku da suka zo Nijeriya daga Sudan don gudanar da wannan jarabawa. Wannan kuwa duk na daga cikin irin kishin da gwamnan yake da shi ga harkar ilimi ne.

“An gudanar da wannan jarabawar ne ga daliban Zamfara 14 daga ranar 23 ga watan Satumba zuwa 30 ga watan Satumbar 2023.

“Gwamnatin ta Zamfara tana ci gaba da bin duk matakan da suka dace don ganin an kammala samar da guraben karatu ga ragowar ɗalibai 52 da suka dawo.

“Tuni Ma’aikatar Ilimi ta Zamfara ta kammala daukar bayanan dalibai 32 cikin 52 da suka rage, wadanda suka kammala duk wata tantancewa da Ma’aikatar Ilimi ta Tarayya dake Abuja.

“Da zaran Ma’aikatar Ilimi ta Tarayya ta kammala tantance daliban, za a samar musu da guraben karatu a mabambantan jami’o’i.”

Zamfara
Leadership Hausa
Website |  + postsBio
  • Leadership Hausa
    Tallafa Wa Yara Masu Buƙatu Na Musamman Shi Ne Burina
  • Leadership Hausa
    Dole Mata Su Rungumi Sana’o’i Domin Tsira Daga Takaicin Zamani —Ramatu Bello
  • Leadership Hausa
    Batun Dakile Shan Taba Sigari A Tsakanin Yara A Nijeriya
  • Leadership Hausa
    Har Yanzu Akwai Sauran Rina A Kaba Game Da Makomar Yara A Nijeriya

MASU ALAKA

Tinubu Yana Zuba Kyawawan Ayyuka A Nijeriya – Ganduje
Manyan Labarai

Ganduje Ya Buƙaci A Yi Siyasar Aƙida Domin Inganta Dimokuraɗiyya A Nijeriya

July 16, 2026
Gwamna Dauda Lawal Zai Gabatar Da Jawabi A Taron Ƙasa Da Ƙasa Na Jami’ar FUE Zariya
Labarai

Gwamna Dauda Lawal Zai Gabatar Da Jawabi A Taron Ƙasa Da Ƙasa Na Jami’ar FUE Zariya

July 15, 2026
Sabbin Ministoci
Labarai

Rashin Tsaro: Majalisar Dattawa Ta Bukaci A Tura Ƙarin Sojoji da ’Yansanda Zuwa Benuwe

July 15, 2026
Next Post
Ranar Lafiyar Ƙwaƙwalwa Ta Duniya: Majalisar Ɗinkin Duniya Ta Horas Da ‘Yan Jarida A Abuja

Ranar Lafiyar Ƙwaƙwalwa Ta Duniya: Majalisar Ɗinkin Duniya Ta Horas Da ‘Yan Jarida A Abuja

LABARAI MASU NASABA

Tinubu Yana Zuba Kyawawan Ayyuka A Nijeriya – Ganduje

Ganduje Ya Buƙaci A Yi Siyasar Aƙida Domin Inganta Dimokuraɗiyya A Nijeriya

July 16, 2026
Binciken CGTN: Amfanar Da Kowa Da Kowa Shi Ne Ainihin Alherin Da Fasahohin Kwaikwayon Tunanin Bil Adama Suka Kawo

Binciken CGTN: Amfanar Da Kowa Da Kowa Shi Ne Ainihin Alherin Da Fasahohin Kwaikwayon Tunanin Bil Adama Suka Kawo

July 15, 2026
Sin Ta Yi Kira Da A Kafa Tsarin Jagorantar Muhimman Ma’adinai Ga Sauyawa Zuwa Amfani Da Makamashi Mai Tsafta

Sin Ta Yi Kira Da A Kafa Tsarin Jagorantar Muhimman Ma’adinai Ga Sauyawa Zuwa Amfani Da Makamashi Mai Tsafta

July 15, 2026
Gwamna Dauda Lawal Zai Gabatar Da Jawabi A Taron Ƙasa Da Ƙasa Na Jami’ar FUE Zariya

Gwamna Dauda Lawal Zai Gabatar Da Jawabi A Taron Ƙasa Da Ƙasa Na Jami’ar FUE Zariya

July 15, 2026
Neman Raba-Gari Da Sauran Kasashe Zai Kawo Mummuann Tasiri Ga Bangarorin Da Abin Ya Shafa

Neman Raba-Gari Da Sauran Kasashe Zai Kawo Mummuann Tasiri Ga Bangarorin Da Abin Ya Shafa

July 15, 2026
Kevin Kelly: AI Na Iya Taimakawa Wajen Cimma Burin “Koyar Da Dalibai Da Kwazonsu”

Kevin Kelly: AI Na Iya Taimakawa Wajen Cimma Burin “Koyar Da Dalibai Da Kwazonsu”

July 15, 2026
Gwamna Yusuf Ya Bai Wa Masu Kula Da Akwatinan Zaɓe Na APC Filaye 1,540 Da Tallafin Miliyan 100

Gwamna Yusuf Ya Bai Wa Masu Kula Da Akwatinan Zaɓe Na APC Filaye 1,540 Da Tallafin Miliyan 100

July 15, 2026
Sabbin Ministoci

Rashin Tsaro: Majalisar Dattawa Ta Bukaci A Tura Ƙarin Sojoji da ’Yansanda Zuwa Benuwe

July 15, 2026
GDPn Sin A Rabin Farko Na Shekarar 2026 Ya Karu Da Kashi 4.7% Idan Aka Kwatanta Da Na Kwatankwacin Lokacin Bara

GDPn Sin A Rabin Farko Na Shekarar 2026 Ya Karu Da Kashi 4.7% Idan Aka Kwatanta Da Na Kwatankwacin Lokacin Bara

July 15, 2026
‘Yansanda Sun Tsaurara Tsaron Iyakokin Kano Bayan Hare-haren ‘Yan Bindiga 

Atiku Ya Nuna Damuwa Kan Kasafin Naira Biliyan 6.44 Don Gasar Cin Kofin Duniya ta 2026

July 15, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.