ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Thursday, July 9, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Ranar Lafiyar Ƙwaƙwalwa Ta Duniya: Majalisar Ɗinkin Duniya Ta Horas Da ‘Yan Jarida A Abuja

Akwai 'Yan Nijeriya Miliyan 20 Da Ke Fama Da Matsalar Ƙwakwalwa

by yahuzajere
3 years ago
Dandazon 'yan jaridar da aka horas tare da kwararrun da suka bayar da horo bayan kammala horaswar a ranar Talata

Dandazon 'yan jaridar da aka horas tare da kwararrun da suka bayar da horo bayan kammala horaswar a ranar Talata

Majalisar Ɗinkin Duniya ta shirya horaswa ta musamman ga ‘yan jarida daga ɓangarori daban-daban a kan muhimmancin kula da lafiyar ƙwaƙwalwa domin taimaka wa wayar da kan jama’a game da abubuwan da ke shafar lafiyar ƙwaƙwalwa da yadda za a magance su ko a rage kaifinsu.

A yayin horaswar masana daban-daban sun gabatar da ƙasidu da suka yi bayani game da ‘yancin Ɗan’adam wajen samun kiwon lafiyar ƙwaƙwalwa da muhimmancin abin da matakan riga-kafin kamuwa da cututtukan da suka shafi ƙwaƙwalwa.

  • Majalisar Dinkin Duniya Ta Jaddada ‘Yancin Dan Adam Wajen Samun Kiwon Lafiyar Kwakwalwa
  • Kisan Dan Jarida: ‘Yansandan Sun Kama Wadanda ake Zargi Da Hannu A Zamfara

Bugu da ƙari an horas da ‘yan jaridan a kan alaƙar aikinsu da kiwon lafiyar ƙwaƙwalwa da yadda ya kamata su riƙa bayar da rahotannin da suka shafi kiwon lafiyar ƙwaƙwalwa cikin ƙwarewa da tausayawa.

ADVERTISEMENT

Wakazalika, an aiwatar da wasu tsare-tsare na gwajin lafiyar ƙwaƙwalwar mahalartan domin kowa ya san matsayinsa da irin matakan da suka kamata mutum ya ɗauka domin daidaita rayuwarsa ta yadda ba za ta haifar masa da matsalar ƙwaƙwalwa ba.

ƙwaƙwalwa

LABARAI MASU NASABA

Kotu Ta Tsare Malamin ABU Kan Zargin Gwamnatin Katsina Da Ɗaukar Nauyin Aikin Hajjin ‘Yan Bindiga

Sin Da Tanzania Da Zambia Sun Karrama Jaruman Sinawa A Bikin Cika Shekaru 50 Da Kafa Layin Dogo Na TAZARA

An fara gabatar da bikin ranar kiwon lafiyar ƙwaƙwalwa ne a ranar 10 ga watan Oktobar 1992 ta hannun Ƙungiyar Kula da Lafiyar Ƙwaƙwalwa ta Duniya bisa goyon bayan Hukumar Lafiya ta Duniya da sauransu.

A saƙonsa na bikin ranar ta bana, Sakatare Janar na Majalisar Ɗinkin Duniya, Antonio Guterres ya bayyana cewa, lafiyar ƙwaƙwalwa da tunani mai kyau yana ba Ɗan’adam damar gudanar da rayuwa mai gamsarwa da ba da gudummawa sosai ga al’ummomi.

Ya nuna takaicinta cewa, daya cikin mutane takwas a duniya na fama da matsalar lafiyar ƙwaƙwalwa, wanda hakan ya fi ƙamari cikin ‘yan mata da matasa.

ƙwaƙwalwa

Bugu da ƙari, mutum uku cikin mutane huɗu da ke fama da matsalar ƙwaƙwalwa, ba su samun isasshiyar kulawa ko kuma babu kulawa ma kwata-kwata, sannan da yawa suna fuskantar ƙyama da wariya a cikin al’umma.

“Kiyaye Lafiyar ƙwaƙwalwa ba gata ba ce ta wane da wane, haƙƙi ce ta dukkan Ɗan’adam– ya zama dole a kula da Lafiyar ƙwaƙwalwa a duk cikin al’ummatai da ke cikin faɗin duniyarmu. Dole ne gwamnatoci su ba da kulawa don magani ga masu matsalar ƙwaƙwalwa da kuma kiyaye hakkinsu.

“Dole ne kuma a magance matsalar cin zarafi tare da karya duk wani shingen da ke hana mutane neman tallafi don magance matsalar ƙwaƙwalwa kuma dole ne mu magance matsalar ƙwaƙwalwa tun daga tushe musamman ta fuskar talauci, wariya, tashin hankali da sauransu.

“A wannan rana ta kula da Kiwon Lafiyar Hankali ta Duniya, muna sake jaddada cewa, kiyaye lafiyar ƙwaƙwalwa, hakki ce kuma ‘yancin Ɗan’adam ne ba tare da nuna wata wariya ba, tare za mu gina duniya mafi ƙoshin lafiya inda kowa zai yi alfahari da ita” in ji ji sakataren majalisar.

ƙwaƙwalwa

Wata ƙididdiga da wata ƙwararriyar da ta yi lacca a taron horas da ‘yan jaridar, Mrs. Moji Makanjuola ta bayyana, ta nunar da cewa akwai ‘Yan Nijeriya aƙalla miliyan 20 da ke fama da rashin lafiyar ƙwaƙwalwa, sannan du-du-du asibitocin da ke kula da masu matsalar ƙwaƙwalwa na gwamnati ba su wuce guda takwas ba, da na masu zaman kansu guda 30, kana likitocin ƙwaƙwalwa 350 ne kacal ake da su a duk faɗin Nijeriya.

 

 

 

ƙwaƙwalwa
yahuzajere
+ postsBio
  • yahuzajere
    Da Kujerar Mulki Gara Zaman Lafiyar Kano
  • yahuzajere
    Ya Kamata Amurka Ta San Ana Barin Halal Don Kunya
  • yahuzajere
    Buɗaɗɗiyar Wasiƙa Ga Gwamnatin Tarayya A Kan Tozarta Marasa Lafiya Daga Jami’an FIRS A Kano
  • yahuzajere
    Sin Ta Kaddamar Da Gagarumin Bikin Ba Da Lambobin Yabo Na Kasar Sin

MASU ALAKA

Kotu Ta Tsare Malamin ABU Kan Zargin Gwamnatin Katsina Da Ɗaukar Nauyin Aikin Hajjin ‘Yan Bindiga
Manyan Labarai

Kotu Ta Tsare Malamin ABU Kan Zargin Gwamnatin Katsina Da Ɗaukar Nauyin Aikin Hajjin ‘Yan Bindiga

July 8, 2026
Sin Da Tanzania Da Zambia Sun Karrama Jaruman Sinawa A Bikin Cika Shekaru 50 Da Kafa Layin Dogo Na TAZARA
Labarai

Sin Da Tanzania Da Zambia Sun Karrama Jaruman Sinawa A Bikin Cika Shekaru 50 Da Kafa Layin Dogo Na TAZARA

July 8, 2026
Badaƙalar PFIPC: Ban Taɓa Haɗuwa Da Gbajabiamila Ba – Adeyemi
Manyan Labarai

Badaƙalar PFIPC: Ban Taɓa Haɗuwa Da Gbajabiamila Ba – Adeyemi

July 8, 2026
Next Post
Alkalan Wasan Firimiya Sun Dauki Matakan Guje Wa Kuskure Dangane Da Na’urar VAR

Alkalan Wasan Firimiya Sun Dauki Matakan Guje Wa Kuskure Dangane Da Na'urar VAR

LABARAI MASU NASABA

Sin Ta Yi Kira Ga Amurka Da Iran Da Su Aiwatar Da Cikakkiyar Takardar Bayanin Fahimtar Juna Da Aka Cimma

Sin Ta Yi Kira Ga Amurka Da Iran Da Su Aiwatar Da Cikakkiyar Takardar Bayanin Fahimtar Juna Da Aka Cimma

July 8, 2026
Sin Ta Yi Kira Da A Cike Gibin Cin Gajiyar Fasahar AI

Sin Ta Yi Kira Da A Cike Gibin Cin Gajiyar Fasahar AI

July 8, 2026
Kotu Ta Tsare Malamin ABU Kan Zargin Gwamnatin Katsina Da Ɗaukar Nauyin Aikin Hajjin ‘Yan Bindiga

Kotu Ta Tsare Malamin ABU Kan Zargin Gwamnatin Katsina Da Ɗaukar Nauyin Aikin Hajjin ‘Yan Bindiga

July 8, 2026
Ministan Lafiya Na DRC Ya Gode Wa Sin Bisa Tura Kwararrun Likitoci Kasar Don Tallafa Wa Dakile Ebola

Ministan Lafiya Na DRC Ya Gode Wa Sin Bisa Tura Kwararrun Likitoci Kasar Don Tallafa Wa Dakile Ebola

July 8, 2026
Sin Ta Yi Watsi Da Ikirarin Philippine Kan Tekun Kudancinta

Sin Ta Yi Watsi Da Ikirarin Philippine Kan Tekun Kudancinta

July 8, 2026
Sin Da Tanzania Da Zambia Sun Karrama Jaruman Sinawa A Bikin Cika Shekaru 50 Da Kafa Layin Dogo Na TAZARA

Sin Da Tanzania Da Zambia Sun Karrama Jaruman Sinawa A Bikin Cika Shekaru 50 Da Kafa Layin Dogo Na TAZARA

July 8, 2026
Zaɓen 2027: NNPP Ta Fara Shigar Da Sunayen ’Yan Takara, Ta Nemi INEC Ta Ƙara Mata Lokaci

Zaɓen 2027: NNPP Ta Fara Shigar Da Sunayen ’Yan Takara, Ta Nemi INEC Ta Ƙara Mata Lokaci

July 8, 2026
Damar Fita Daga Kangin Dalar Amurka Ta Sake Samuwa Ga Kasashen Afirka

Damar Fita Daga Kangin Dalar Amurka Ta Sake Samuwa Ga Kasashen Afirka

July 8, 2026
Badaƙalar PFIPC: Ban Taɓa Haɗuwa Da Gbajabiamila Ba – Adeyemi

Badaƙalar PFIPC: Ban Taɓa Haɗuwa Da Gbajabiamila Ba – Adeyemi

July 8, 2026
NNGF Ta Kaddamar Da Kwamitin Amintattu Na Gidauniyar Asusun Tsaro Ta Yankin

NNGF Ta Kaddamar Da Kwamitin Amintattu Na Gidauniyar Asusun Tsaro Ta Yankin

July 8, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.