ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Friday, June 5, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Ranar Lafiyar Ƙwaƙwalwa Ta Duniya: Majalisar Ɗinkin Duniya Ta Horas Da ‘Yan Jarida A Abuja

Akwai 'Yan Nijeriya Miliyan 20 Da Ke Fama Da Matsalar Ƙwakwalwa

by yahuzajere
3 years ago
Dandazon 'yan jaridar da aka horas tare da kwararrun da suka bayar da horo bayan kammala horaswar a ranar Talata

Dandazon 'yan jaridar da aka horas tare da kwararrun da suka bayar da horo bayan kammala horaswar a ranar Talata

Majalisar Ɗinkin Duniya ta shirya horaswa ta musamman ga ‘yan jarida daga ɓangarori daban-daban a kan muhimmancin kula da lafiyar ƙwaƙwalwa domin taimaka wa wayar da kan jama’a game da abubuwan da ke shafar lafiyar ƙwaƙwalwa da yadda za a magance su ko a rage kaifinsu.

A yayin horaswar masana daban-daban sun gabatar da ƙasidu da suka yi bayani game da ‘yancin Ɗan’adam wajen samun kiwon lafiyar ƙwaƙwalwa da muhimmancin abin da matakan riga-kafin kamuwa da cututtukan da suka shafi ƙwaƙwalwa.

  • Majalisar Dinkin Duniya Ta Jaddada ‘Yancin Dan Adam Wajen Samun Kiwon Lafiyar Kwakwalwa
  • Kisan Dan Jarida: ‘Yansandan Sun Kama Wadanda ake Zargi Da Hannu A Zamfara

Bugu da ƙari an horas da ‘yan jaridan a kan alaƙar aikinsu da kiwon lafiyar ƙwaƙwalwa da yadda ya kamata su riƙa bayar da rahotannin da suka shafi kiwon lafiyar ƙwaƙwalwa cikin ƙwarewa da tausayawa.

ADVERTISEMENT

Wakazalika, an aiwatar da wasu tsare-tsare na gwajin lafiyar ƙwaƙwalwar mahalartan domin kowa ya san matsayinsa da irin matakan da suka kamata mutum ya ɗauka domin daidaita rayuwarsa ta yadda ba za ta haifar masa da matsalar ƙwaƙwalwa ba.

ƙwaƙwalwa

LABARAI MASU NASABA

Ƴansanda Sun Daƙile Harin Ƴan Bindiga, Sun Kwato Shanu 25 A Sakkwato

Rikicin Manoma Da Makiyaya Ya Kashe Mutane 7, Ya Jikkata 6 A Bauchi

An fara gabatar da bikin ranar kiwon lafiyar ƙwaƙwalwa ne a ranar 10 ga watan Oktobar 1992 ta hannun Ƙungiyar Kula da Lafiyar Ƙwaƙwalwa ta Duniya bisa goyon bayan Hukumar Lafiya ta Duniya da sauransu.

A saƙonsa na bikin ranar ta bana, Sakatare Janar na Majalisar Ɗinkin Duniya, Antonio Guterres ya bayyana cewa, lafiyar ƙwaƙwalwa da tunani mai kyau yana ba Ɗan’adam damar gudanar da rayuwa mai gamsarwa da ba da gudummawa sosai ga al’ummomi.

Ya nuna takaicinta cewa, daya cikin mutane takwas a duniya na fama da matsalar lafiyar ƙwaƙwalwa, wanda hakan ya fi ƙamari cikin ‘yan mata da matasa.

ƙwaƙwalwa

Bugu da ƙari, mutum uku cikin mutane huɗu da ke fama da matsalar ƙwaƙwalwa, ba su samun isasshiyar kulawa ko kuma babu kulawa ma kwata-kwata, sannan da yawa suna fuskantar ƙyama da wariya a cikin al’umma.

“Kiyaye Lafiyar ƙwaƙwalwa ba gata ba ce ta wane da wane, haƙƙi ce ta dukkan Ɗan’adam– ya zama dole a kula da Lafiyar ƙwaƙwalwa a duk cikin al’ummatai da ke cikin faɗin duniyarmu. Dole ne gwamnatoci su ba da kulawa don magani ga masu matsalar ƙwaƙwalwa da kuma kiyaye hakkinsu.

“Dole ne kuma a magance matsalar cin zarafi tare da karya duk wani shingen da ke hana mutane neman tallafi don magance matsalar ƙwaƙwalwa kuma dole ne mu magance matsalar ƙwaƙwalwa tun daga tushe musamman ta fuskar talauci, wariya, tashin hankali da sauransu.

“A wannan rana ta kula da Kiwon Lafiyar Hankali ta Duniya, muna sake jaddada cewa, kiyaye lafiyar ƙwaƙwalwa, hakki ce kuma ‘yancin Ɗan’adam ne ba tare da nuna wata wariya ba, tare za mu gina duniya mafi ƙoshin lafiya inda kowa zai yi alfahari da ita” in ji ji sakataren majalisar.

ƙwaƙwalwa

Wata ƙididdiga da wata ƙwararriyar da ta yi lacca a taron horas da ‘yan jaridar, Mrs. Moji Makanjuola ta bayyana, ta nunar da cewa akwai ‘Yan Nijeriya aƙalla miliyan 20 da ke fama da rashin lafiyar ƙwaƙwalwa, sannan du-du-du asibitocin da ke kula da masu matsalar ƙwaƙwalwa na gwamnati ba su wuce guda takwas ba, da na masu zaman kansu guda 30, kana likitocin ƙwaƙwalwa 350 ne kacal ake da su a duk faɗin Nijeriya.

 

 

 

ƙwaƙwalwa
yahuzajere
+ postsBio
  • yahuzajere
    Da Kujerar Mulki Gara Zaman Lafiyar Kano
  • yahuzajere
    Ya Kamata Amurka Ta San Ana Barin Halal Don Kunya
  • yahuzajere
    Buɗaɗɗiyar Wasiƙa Ga Gwamnatin Tarayya A Kan Tozarta Marasa Lafiya Daga Jami’an FIRS A Kano
  • yahuzajere
    Sin Ta Kaddamar Da Gagarumin Bikin Ba Da Lambobin Yabo Na Kasar Sin

MASU ALAKA

Ƴansanda Sun Daƙile Harin Ƴan Bindiga, Sun Kwato Shanu 25 A Sakkwato
Tsaro

Ƴansanda Sun Daƙile Harin Ƴan Bindiga, Sun Kwato Shanu 25 A Sakkwato

June 4, 2026
Rikicin Manoma Da Makiyaya Ya Kashe Mutane 7, Ya Jikkata 6 A Bauchi
Labarai

Rikicin Manoma Da Makiyaya Ya Kashe Mutane 7, Ya Jikkata 6 A Bauchi

June 4, 2026
Rikicin Manoma Da Makiyaya Ya Yi Sanadin Mutuwar Mutane 7 A Bauchi
Manyan Labarai

Rikicin Manoma Da Makiyaya Ya Yi Sanadin Mutuwar Mutane 7 A Bauchi

June 4, 2026
Next Post
Alkalan Wasan Firimiya Sun Dauki Matakan Guje Wa Kuskure Dangane Da Na’urar VAR

Alkalan Wasan Firimiya Sun Dauki Matakan Guje Wa Kuskure Dangane Da Na'urar VAR

LABARAI MASU NASABA

Matatar Dangote Ta Ƙara Yawan Man Da Take Tacewa Zuwa Ganga 700,000

Matatar Dangote Ta Ƙara Yawan Man Da Take Tacewa Zuwa Ganga 700,000

June 4, 2026
Ƴansanda Sun Daƙile Harin Ƴan Bindiga, Sun Kwato Shanu 25 A Sakkwato

Ƴansanda Sun Daƙile Harin Ƴan Bindiga, Sun Kwato Shanu 25 A Sakkwato

June 4, 2026
Takunkumin Amurka Ya Haifar Da Mummunan Tasiri Ga Tsarin Samar Da Kayan Latironi Na Duniya

Takunkumin Amurka Ya Haifar Da Mummunan Tasiri Ga Tsarin Samar Da Kayan Latironi Na Duniya

June 4, 2026
Rikicin Manoma Da Makiyaya Ya Kashe Mutane 7, Ya Jikkata 6 A Bauchi

Rikicin Manoma Da Makiyaya Ya Kashe Mutane 7, Ya Jikkata 6 A Bauchi

June 4, 2026
Rikicin Manoma Da Makiyaya Ya Yi Sanadin Mutuwar Mutane 7 A Bauchi

Rikicin Manoma Da Makiyaya Ya Yi Sanadin Mutuwar Mutane 7 A Bauchi

June 4, 2026
Mun Kaɗu Matuƙa Kan Labarin Mutuwar ‘Yan Mauludi A Hanyar Saminaka – Gwamnan Kaduna

Gwamna Sani Ya Kashe Sama Da Naira Biliyan Ɗaya Kan Tallafin Ɗalibai A Kaduna – Kwamishina

June 4, 2026
Sin Ta Ware Kudi Har Yuan Biliyan 99.9 Domin Tallafawa Kula Da Lafiyar Yara A 2026

Sin Ta Ware Kudi Har Yuan Biliyan 99.9 Domin Tallafawa Kula Da Lafiyar Yara A 2026

June 4, 2026
Tasirin Nasarar Da Kasar Sin Ta Cimma A Fannin Kakkabe Matsanancin Talauci

Tasirin Nasarar Da Kasar Sin Ta Cimma A Fannin Kakkabe Matsanancin Talauci

June 4, 2026
Sabbin Ra’ayoyin Ci Gaba: Manufofin Zamani Na Zamanantarwa

Sabbin Ra’ayoyin Ci Gaba: Manufofin Zamani Na Zamanantarwa

June 4, 2026
Fargabar Satar Mutane Ya Sa An Rufe Makarantu A Abuja Da Mararaba

Fargabar Satar Mutane Ya Sa An Rufe Makarantu A Abuja Da Mararaba

June 4, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.