• English
  • Business News
Friday, September 19, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Ranar Malamai Ta Duniya: Yadda Yajin Aikin ASUU Ya Yi Wa Ilimi Katutu A Wuya

Ina Makomar Ilimi A Nijeriya?

by Sadiq
3 years ago
in Rahotonni
0
Ranar Malamai Ta Duniya: Yadda Yajin Aikin ASUU Ya Yi Wa Ilimi Katutu A Wuya
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Ranar 5 ga watan Oktoban kowace shekara, ita ce ranar da Majalisar Dinkin Duniya ta ware don bikin murnar ranar Malamai ta Duniya.

A yau malamai da dama a sassan duniya na murnar zagayowar wannan rana, amma a Nijeriya abun ba yabo ba fallasa.

  • Gwamnatin Jihar Imo Ta Amince Da Karin Matsayi Da Tallafin Kiwon Lafiya Kyauta Ga Ma’aikatanta
  • Zambar Naira Miliyan 55: ICPC Ta Fara Bin Diddigin Dan Kwangilar Dam Din Jihar Filato

Idan aka yi waiwaye musamman ga ilimin da ya shafi Jami’o’i wanda ya hadar da malamai da dalibai, a iya cewa ‘ba a rabu da Bukar ba an haifi Habu.’

ASUU da Gwamnatin Tarayyar Nijeriya sun shafe kimanin watanni bakwai zuwa takwas suna tafka takaddama kan yajin aikin da ya ki ya ki cinye kan wasu alkawura da malaman Jami’o’in suka tilas ne sai an biya musu.

Idan aka yi waiwaye za a fahimci cewar yajin aikin ASUU abu ne da aka shafe kimanin sama da shekaru 30 ana yinsa, a iya cewa kusan kowace gwamnati ta zo sai an yi wannan takaddama ta yajin aiki.

Labarai Masu Nasaba

Yadda Ahlul Faidhati Mai Diwani Group Suka Yi Maulidin Cikar Annabi (SAW) Shekara 1,500 Da Haihuwa 

Abin Fargaba Ne Yadda Bashin Nijeriya Ya Haura Tiriliyan 149 – Shugaban Majalisar Wakilai 

Wasu gwamnatocin kan yi kokarin ganin sun biya wasu bukatun da ASUU ke nema sannan ta dauki alkawarin cika wasu, wanda a wasu lokutan hakan ke jefa wata gwamnatin cikin kaka-na-kayi idan ta gaji wata gwamnatin.

A shekarar 2012, gwamnatin shugaba Goodluck Jonathan ta daukar wa ASUU alkawura wanda gwamnatin yanzu kuma ta gada, hakan ya sa ake ta kwan-gaba-kwan-baya.

Sai dai dag bangarenta, ASUU na ganin kamar gwamnatin yanzu na nuna halin ko in kula game da illar da yajin aikin ka iya haifar wa fagen ilimi.

Sannan ta soki lamirin gwamnatin tarayya kan tsarin biya ma’aikata albashi na IPPIS, wanda ta ce akwai lauje cikin nadi game da tsarin, wanda hakan ya sa tun fil-azal taki karbar tsarin.

Idan aka yi duba kuwa game da koma baya da yajin aikin ya haifar, a iya cewa akwai bukatar kowane bangare ya mayar da wukarsa don cimma matsaya tare da bai wa dalibai da su kan su malamai damar gudanar da ayyukansu yadda ya dace.

Yajin aikin ya kawo koma baya ga dalibai da yawa, musamman daliban da ke shirin kammala karatu da kuma wanda suke jiran a kammala duba kundin bincikensu don ba su takardar shaidar kammala Jami’a.

A bangaren malaman kuwa, su ma suna fama da rashin albashi, wanda hakan ya jefa da dama daga cikinsu cikin mayuwancin hali, musamman abin da ya shafi tafi da harkokin gida na yau da kull da kula da karatun yara.

Gashi gwamnatin tarayya ta kafa dokar duk wanda bai yi aiki ba, ba shi da albashi.

Wannan hali da ake ciki, ya sanya mutane da dama yin kiranye-kiranye ga gwamnatin tarayya da ma bangaren ASUU na ganin kowa ya dauki dangana, don ciyar da ilimi gaba da kuma kyankyasar da matasa masu ilimi da su jagoranci Nijeriya a nan gaba.

Da fatan kowane bangare zai duba na tsanaki, da bai wa zuciyarsa ruwan sanyi don daina tafasa kan wannan yajin aiki da ya ki ci ya ki cinyewa.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: Gwamnatin TarayyaJami'o'iMajalisar Dinkin DuniyaMalamaiRanar Malamai ta DuniyaTakaddamaTsawaita Yajin Aikin
ShareTweetSendShare
Previous Post

Zargin Badakalar Kudade: Kotu Ta Wanke Magu

Next Post

Dalibai Sun Yi Zanga-Zanga Kan Korarsu Daga Cibiyar Koyar Da Sana’o’i Ta Dangote A Kano

Related

Ahlul Faidhati Mai Diwani Group
Rahotonni

Yadda Ahlul Faidhati Mai Diwani Group Suka Yi Maulidin Cikar Annabi (SAW) Shekara 1,500 Da Haihuwa 

7 days ago
Majalisa Ta Nemi Jami’an Tsaro Su Ceto Daliban Jami’ar Gusau 30 Da Aka Sace
Rahotonni

Abin Fargaba Ne Yadda Bashin Nijeriya Ya Haura Tiriliyan 149 – Shugaban Majalisar Wakilai 

1 week ago
Arewa
Rahotonni

Matsalar Tsaro: Gwamnonin Arewa Sun Bullo Da Sabbin Matakan Yaki Da Ta’addanci

2 weeks ago
'Yan Bindiga
Rahotonni

Sulhu Da ‘Yan Bindiga Ya Fara Haifar Da Da Mai Ido A Katsina

2 weeks ago
Gidauniyar ‘Ya’yan Sarakunan Arewa Sun Marawa Sarkin Musulmi A Matsayin Shugaban Majalisar Sarakuna
Rahotonni

Babban Taron Lauyoyi Na Kasa: Sarkin Musulmi Ya Gargadi Alkalai Kan Tabbatar Da Adalci

3 weeks ago
Sin Ta Fara Amfani Da Tauraron Dan Adam Wajen Duba Manyan Hanyoyin Wutar Lantarki A Karo Na Farko
Rahotonni

Cire Tallafin Wutar Lantarki Zai Kara Kuntata Rayuwar ‘Yan Nijeriya – Kungiyar Kwadago

3 weeks ago
Next Post
Dalibai Sun Yi Zanga-Zanga Kan Korarsu Daga Cibiyar Koyar Da Sana’o’i Ta Dangote A Kano

Dalibai Sun Yi Zanga-Zanga Kan Korarsu Daga Cibiyar Koyar Da Sana'o'i Ta Dangote A Kano

LABARAI MASU NASABA

An Yi Bikin Tunawa Da Ranar Kaddamar Da Yakin Kin Mamayar Dakarun Japan A Birnin Shenyang

An Yi Bikin Tunawa Da Ranar Kaddamar Da Yakin Kin Mamayar Dakarun Japan A Birnin Shenyang

September 18, 2025
Likitocin Sin Dake Aikin Agajin Kiwon Lafiya A Nijar Sun Gudanar Da Tiyatar ALT A Karon Farko A Yammacin Afirka

Likitocin Sin Dake Aikin Agajin Kiwon Lafiya A Nijar Sun Gudanar Da Tiyatar ALT A Karon Farko A Yammacin Afirka

September 18, 2025
Fim Mai Taken 731 Na Tunatar Da Jama’a Muhimmancin Kiyaye Zaman Lafiya

Fim Mai Taken 731 Na Tunatar Da Jama’a Muhimmancin Kiyaye Zaman Lafiya

September 18, 2025
Kotun Sojin Nijeriya Ta Yanke Hukuncin Kisa Kan Wani Soja Da Ya Kashe ÆŠan Adaidaita

Kotun Sojin Nijeriya Ta Yanke Hukuncin Kisa Kan Wani Soja Da Ya Kashe ÆŠan Adaidaita

September 18, 2025
Sashen Raya Kimiyya Da Fasaha Na Sin Ya Kai Babban Matsayi Yayin Shirin Raya Kasa Na Shekaru Biyar-biyar Karo Na 14

Sashen Raya Kimiyya Da Fasaha Na Sin Ya Kai Babban Matsayi Yayin Shirin Raya Kasa Na Shekaru Biyar-biyar Karo Na 14

September 18, 2025
Jose Mourinho Ya Zama Sabon Kocin Benfica

Jose Mourinho Ya Zama Sabon Kocin Benfica

September 18, 2025
An Bude Taron Dandalin Tattauna Batun Tsaro Na Xiangshan Karo Na 12 A Birnin Beijing

An Bude Taron Dandalin Tattauna Batun Tsaro Na Xiangshan Karo Na 12 A Birnin Beijing

September 18, 2025
NNPP

Gwamna Yusuf Ya Nuna Jin DaÉ—insa Kan Yadda Kano Ta Zarce Legas, Oyo A Sakamakon NECO Na 2025

September 18, 2025
Shugaban Guinea-Bissau Ya Goyi Bayan Shawarar Tsarin Shugabancin Duniya Da Sin Ta Gabatar

Shugaban Guinea-Bissau Ya Goyi Bayan Shawarar Tsarin Shugabancin Duniya Da Sin Ta Gabatar

September 18, 2025
An Damke Basarake Da Wasu Mutum 10 Bisa Zargin Hada Baki Da ‘Yan Bindiga A Kudancin Kaduna

Sojoji Sun Tarwatsa Wata Haramtacciyar Masana’antar Ƙera Makamai A Filato

September 18, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.