• English
  • Business News
Thursday, May 15, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Ranar Malamai Ta Duniya: Yadda Yajin Aikin ASUU Ya Yi Wa Ilimi Katutu A Wuya

Ina Makomar Ilimi A Nijeriya?

by Sadiq
3 years ago
in Rahotonni
0
Ranar Malamai Ta Duniya: Yadda Yajin Aikin ASUU Ya Yi Wa Ilimi Katutu A Wuya
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Ranar 5 ga watan Oktoban kowace shekara, ita ce ranar da Majalisar Dinkin Duniya ta ware don bikin murnar ranar Malamai ta Duniya.

A yau malamai da dama a sassan duniya na murnar zagayowar wannan rana, amma a Nijeriya abun ba yabo ba fallasa.

  • Gwamnatin Jihar Imo Ta Amince Da Karin Matsayi Da Tallafin Kiwon Lafiya Kyauta Ga Ma’aikatanta
  • Zambar Naira Miliyan 55: ICPC Ta Fara Bin Diddigin Dan Kwangilar Dam Din Jihar Filato

Idan aka yi waiwaye musamman ga ilimin da ya shafi Jami’o’i wanda ya hadar da malamai da dalibai, a iya cewa ‘ba a rabu da Bukar ba an haifi Habu.’

ASUU da Gwamnatin Tarayyar Nijeriya sun shafe kimanin watanni bakwai zuwa takwas suna tafka takaddama kan yajin aikin da ya ki ya ki cinye kan wasu alkawura da malaman Jami’o’in suka tilas ne sai an biya musu.

Idan aka yi waiwaye za a fahimci cewar yajin aikin ASUU abu ne da aka shafe kimanin sama da shekaru 30 ana yinsa, a iya cewa kusan kowace gwamnati ta zo sai an yi wannan takaddama ta yajin aiki.

Labarai Masu Nasaba

Gwamna Umar Namadi Ya Dauki Matakan Kai Jihar Jigawa Babban Matsayi

Ficewar Kasar Nijar Daga Rundunar Hadin Gwiwa Ta Kasa Da Kasa Barazana Ce Ga Tsaro -Hedikwatar Tsaro

Wasu gwamnatocin kan yi kokarin ganin sun biya wasu bukatun da ASUU ke nema sannan ta dauki alkawarin cika wasu, wanda a wasu lokutan hakan ke jefa wata gwamnatin cikin kaka-na-kayi idan ta gaji wata gwamnatin.

A shekarar 2012, gwamnatin shugaba Goodluck Jonathan ta daukar wa ASUU alkawura wanda gwamnatin yanzu kuma ta gada, hakan ya sa ake ta kwan-gaba-kwan-baya.

Sai dai dag bangarenta, ASUU na ganin kamar gwamnatin yanzu na nuna halin ko in kula game da illar da yajin aikin ka iya haifar wa fagen ilimi.

Sannan ta soki lamirin gwamnatin tarayya kan tsarin biya ma’aikata albashi na IPPIS, wanda ta ce akwai lauje cikin nadi game da tsarin, wanda hakan ya sa tun fil-azal taki karbar tsarin.

Idan aka yi duba kuwa game da koma baya da yajin aikin ya haifar, a iya cewa akwai bukatar kowane bangare ya mayar da wukarsa don cimma matsaya tare da bai wa dalibai da su kan su malamai damar gudanar da ayyukansu yadda ya dace.

Yajin aikin ya kawo koma baya ga dalibai da yawa, musamman daliban da ke shirin kammala karatu da kuma wanda suke jiran a kammala duba kundin bincikensu don ba su takardar shaidar kammala Jami’a.

A bangaren malaman kuwa, su ma suna fama da rashin albashi, wanda hakan ya jefa da dama daga cikinsu cikin mayuwancin hali, musamman abin da ya shafi tafi da harkokin gida na yau da kull da kula da karatun yara.

Gashi gwamnatin tarayya ta kafa dokar duk wanda bai yi aiki ba, ba shi da albashi.

Wannan hali da ake ciki, ya sanya mutane da dama yin kiranye-kiranye ga gwamnatin tarayya da ma bangaren ASUU na ganin kowa ya dauki dangana, don ciyar da ilimi gaba da kuma kyankyasar da matasa masu ilimi da su jagoranci Nijeriya a nan gaba.

Da fatan kowane bangare zai duba na tsanaki, da bai wa zuciyarsa ruwan sanyi don daina tafasa kan wannan yajin aiki da ya ki ci ya ki cinyewa.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: Gwamnatin TarayyaJami'o'iMajalisar Dinkin DuniyaMalamaiRanar Malamai ta DuniyaTakaddamaTsawaita Yajin Aikin
ShareTweetSendShare
Previous Post

Zargin Badakalar Kudade: Kotu Ta Wanke Magu

Next Post

Dalibai Sun Yi Zanga-Zanga Kan Korarsu Daga Cibiyar Koyar Da Sana’o’i Ta Dangote A Kano

Related

Gwamna Umar Namadi Ya Dauki Matakan Kai Jihar Jigawa Babban Matsayi
Rahotonni

Gwamna Umar Namadi Ya Dauki Matakan Kai Jihar Jigawa Babban Matsayi

4 weeks ago
Janar Tiani Ya Fara Sabon Mulkin Shekaru Biyar A Nijar
Rahotonni

Ficewar Kasar Nijar Daga Rundunar Hadin Gwiwa Ta Kasa Da Kasa Barazana Ce Ga Tsaro -Hedikwatar Tsaro

1 month ago
An Gudanar Da Taron Zaman Lafiya Tsakanin Manoma Da Makiyaya
Rahotonni

An Gudanar Da Taron Zaman Lafiya Tsakanin Manoma Da Makiyaya

1 month ago
Donald Trump Zai Gurfana A Gaban Kotu Kan Tuhumar Da Ake Masa
Rahotonni

Amurka Ta Sayi Kayayyakin Nijeriya Na Dala Miliyan 643 A Wata 2 – Rahoto

1 month ago
Gwamnoni 20 Na Fuskantar Matsin Lambar NULGE Kan Rashin Aiwatar Da Mafi Karanci Albashi
Rahotonni

Gwamnoni 20 Na Fuskantar Matsin Lambar NULGE Kan Rashin Aiwatar Da Mafi Karanci Albashi

1 month ago
Tinubu
Manyan Labarai

Yadda Tinubu Ya Shirya Wa Kansa Mafitar Siyasa Kafin Zaben 2027

2 months ago
Next Post
Dalibai Sun Yi Zanga-Zanga Kan Korarsu Daga Cibiyar Koyar Da Sana’o’i Ta Dangote A Kano

Dalibai Sun Yi Zanga-Zanga Kan Korarsu Daga Cibiyar Koyar Da Sana'o'i Ta Dangote A Kano

LABARAI MASU NASABA

UTME

ASUU Ta Yi Barazanar Maka JAMB A Kotu Biyo Bayan Samun Mummunan Sakamako A UTME

May 14, 2025
Xi Jinping Ya Gana Da Takwarorinsa Na Kasashen Colombia Da Chile

Xi Jinping Ya Gana Da Takwarorinsa Na Kasashen Colombia Da Chile

May 14, 2025
Gwamnatin Tarayya Da Majalisar Dokoki Za Su Haɗa  Gwiwa Kan Sake Duba Dokar Laifukan Intanet — Minista

Gwamnatin Tarayya Da Majalisar Dokoki Za Su Haɗa  Gwiwa Kan Sake Duba Dokar Laifukan Intanet — Minista

May 14, 2025
Yadda Kasar Sin Ke Kokarin Gina Tashar Bincike A Sama Da Tubalin Kasar Duniyar Wata

Yadda Kasar Sin Ke Kokarin Gina Tashar Bincike A Sama Da Tubalin Kasar Duniyar Wata

May 14, 2025
gaza

Kasafin Kudi Na Naira Tiriliyan 1.78 Na Abuja Ya Tsallake Karatu Na Biyu A Majalisa

May 14, 2025
Kasar Sin Za Ta Inganta Cikakken Tsarin Fitar Da Ma’adanai Zuwa Ketare Don Kiyaye Tsaron Kasa

Kasar Sin Za Ta Inganta Cikakken Tsarin Fitar Da Ma’adanai Zuwa Ketare Don Kiyaye Tsaron Kasa

May 14, 2025
Tinubu Ya Yaba Wa Sule Lamiɗo A Taron Ƙaddamar Da Littafin Tarihin Rayuwasa

Tinubu Ya Yaba Wa Sule Lamiɗo A Taron Ƙaddamar Da Littafin Tarihin Rayuwasa

May 14, 2025
Manyan Ayyuka Guda Biyar Za Su Raya Makomar Al’ummomin Kasar Sin Da kasashen Latin Amurka Da Caribbean Ta Bai Daya

Manyan Ayyuka Guda Biyar Za Su Raya Makomar Al’ummomin Kasar Sin Da kasashen Latin Amurka Da Caribbean Ta Bai Daya

May 14, 2025
Yadda Aka Gina Ofishin ‘Yansanda Na Zamani A Abuja

Yadda Aka Gina Ofishin ‘Yansanda Na Zamani A Abuja

May 14, 2025
JAMB Ta Amince Da Maki 140 Da 100 Mafi Karancin Maki Na Shiga Manyan Makarantu

JAMB: TangarÉ—ar Na’ura Ne Ya Haifar Da Gagarumar Koma Baya A Sakamakon UTME Na 2025

May 14, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.