ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Wednesday, September 9, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Ranar Malamai Ta Duniya: Yadda Yajin Aikin ASUU Ya Yi Wa Ilimi Katutu A Wuya

Ina Makomar Ilimi A Nijeriya?

by Sadiq
4 years ago
ASUU

Ranar 5 ga watan Oktoban kowace shekara, ita ce ranar da Majalisar Dinkin Duniya ta ware don bikin murnar ranar Malamai ta Duniya.

A yau malamai da dama a sassan duniya na murnar zagayowar wannan rana, amma a Nijeriya abun ba yabo ba fallasa.

  • Gwamnatin Jihar Imo Ta Amince Da Karin Matsayi Da Tallafin Kiwon Lafiya Kyauta Ga Ma’aikatanta
  • Zambar Naira Miliyan 55: ICPC Ta Fara Bin Diddigin Dan Kwangilar Dam Din Jihar Filato

Idan aka yi waiwaye musamman ga ilimin da ya shafi Jami’o’i wanda ya hadar da malamai da dalibai, a iya cewa ‘ba a rabu da Bukar ba an haifi Habu.’

ADVERTISEMENT

ASUU da Gwamnatin Tarayyar Nijeriya sun shafe kimanin watanni bakwai zuwa takwas suna tafka takaddama kan yajin aikin da ya ki ya ki cinye kan wasu alkawura da malaman Jami’o’in suka tilas ne sai an biya musu.

Idan aka yi waiwaye za a fahimci cewar yajin aikin ASUU abu ne da aka shafe kimanin sama da shekaru 30 ana yinsa, a iya cewa kusan kowace gwamnati ta zo sai an yi wannan takaddama ta yajin aiki.

LABARAI MASU NASABA

Karuwar Farin Jinin Gwamna Umaru Bago A Siyasar Jihar Neja

Kyakkyawan Tsarin Laken Asiri Zai Dakile Shirin Magudin Zabe A Nijeriya —Mohammed

Wasu gwamnatocin kan yi kokarin ganin sun biya wasu bukatun da ASUU ke nema sannan ta dauki alkawarin cika wasu, wanda a wasu lokutan hakan ke jefa wata gwamnatin cikin kaka-na-kayi idan ta gaji wata gwamnatin.

A shekarar 2012, gwamnatin shugaba Goodluck Jonathan ta daukar wa ASUU alkawura wanda gwamnatin yanzu kuma ta gada, hakan ya sa ake ta kwan-gaba-kwan-baya.

Sai dai dag bangarenta, ASUU na ganin kamar gwamnatin yanzu na nuna halin ko in kula game da illar da yajin aikin ka iya haifar wa fagen ilimi.

Sannan ta soki lamirin gwamnatin tarayya kan tsarin biya ma’aikata albashi na IPPIS, wanda ta ce akwai lauje cikin nadi game da tsarin, wanda hakan ya sa tun fil-azal taki karbar tsarin.

Idan aka yi duba kuwa game da koma baya da yajin aikin ya haifar, a iya cewa akwai bukatar kowane bangare ya mayar da wukarsa don cimma matsaya tare da bai wa dalibai da su kan su malamai damar gudanar da ayyukansu yadda ya dace.

Yajin aikin ya kawo koma baya ga dalibai da yawa, musamman daliban da ke shirin kammala karatu da kuma wanda suke jiran a kammala duba kundin bincikensu don ba su takardar shaidar kammala Jami’a.

A bangaren malaman kuwa, su ma suna fama da rashin albashi, wanda hakan ya jefa da dama daga cikinsu cikin mayuwancin hali, musamman abin da ya shafi tafi da harkokin gida na yau da kull da kula da karatun yara.

Gashi gwamnatin tarayya ta kafa dokar duk wanda bai yi aiki ba, ba shi da albashi.

Wannan hali da ake ciki, ya sanya mutane da dama yin kiranye-kiranye ga gwamnatin tarayya da ma bangaren ASUU na ganin kowa ya dauki dangana, don ciyar da ilimi gaba da kuma kyankyasar da matasa masu ilimi da su jagoranci Nijeriya a nan gaba.

Da fatan kowane bangare zai duba na tsanaki, da bai wa zuciyarsa ruwan sanyi don daina tafasa kan wannan yajin aiki da ya ki ci ya ki cinyewa.

MASU ALAKA

Gwamnatin Neja Ta Bayar Da Umarnin Kawo Karshen Matsalar Tsaro
Rahotonni

Karuwar Farin Jinin Gwamna Umaru Bago A Siyasar Jihar Neja

September 5, 2026
Kyakkyawan Tsarin Laken Asiri Zai Dakile Shirin Magudin Zabe A Nijeriya —Mohammed
Rahotonni

Kyakkyawan Tsarin Laken Asiri Zai Dakile Shirin Magudin Zabe A Nijeriya —Mohammed

September 5, 2026
Jihar Katsina Da UNICEF Sun Ceto Rayuwar Yara Ta Hanyar Samar Da Abinci Mai Gina Jiki
Rahotonni

Jihar Katsina Da UNICEF Sun Ceto Rayuwar Yara Ta Hanyar Samar Da Abinci Mai Gina Jiki

September 5, 2026
Next Post
Dalibai Sun Yi Zanga-Zanga Kan Korarsu Daga Cibiyar Koyar Da Sana’o’i Ta Dangote A Kano

Dalibai Sun Yi Zanga-Zanga Kan Korarsu Daga Cibiyar Koyar Da Sana'o'i Ta Dangote A Kano

LABARAI MASU NASABA

Taron PDP Na Ƙasa: Ɓangaren Wike Ya Kafa Sabon NWC A Abuja

PDP Ta Musanta Mara Wa APM Baya A Bauchi

September 9, 2026
Sojoji

Sojoji Sun Dakile Hare-Hare, Sun Ceto Mutane 12 A Zamfara

September 9, 2026
Batun AI Zai Fi Daukar Hankali A Bikin Baje Kolin Fasahar Zamani Ta Duniya Karo Na 5

Batun AI Zai Fi Daukar Hankali A Bikin Baje Kolin Fasahar Zamani Ta Duniya Karo Na 5

September 8, 2026
Gwamna Radda Ya Samu Goyon Bayan APC A Katsina Gabanin Zaɓen 2027

Gwamna Radda Ya Samu Goyon Bayan APC A Katsina Gabanin Zaɓen 2027

September 8, 2026
Cinikin Wajen Sin Ya Ci Gaba Da Samun Bunkasa Cikin Sauri A Watanni Takwas Na Farkon Bana

Cinikin Wajen Sin Ya Ci Gaba Da Samun Bunkasa Cikin Sauri A Watanni Takwas Na Farkon Bana

September 8, 2026
'Yan Bindiga

‘Yan Bindiga Sun Kashe 2, Sun Yi Garkuwa Da 26 A Kaduna

September 8, 2026
Binciken CGTN Ya Nuna Gamsuwa Da Yadda Baje Kolin CIFTIS Ke Shaida Karfin Gwiwar Sin A Fannin Kara Fadada Bude Kofa Bisa Babban Matsayi

Binciken CGTN Ya Nuna Gamsuwa Da Yadda Baje Kolin CIFTIS Ke Shaida Karfin Gwiwar Sin A Fannin Kara Fadada Bude Kofa Bisa Babban Matsayi

September 8, 2026
Yadda Taron Tattalin Arziki Da Zuba Jari Na Kwana Biyu Ya Gudana A Katsina

Gwamna Radda Ya Gabatar Da Kasafin N828.6bn Na 2027

September 8, 2026
Sin Za Ta Yi Aiki Tare Da Sassa Daban Daban Domin Mayar Da Fasahar AI Wata Dama Ta Cin Gajiya Mai Dorewa

Sin Za Ta Yi Aiki Tare Da Sassa Daban Daban Domin Mayar Da Fasahar AI Wata Dama Ta Cin Gajiya Mai Dorewa

September 8, 2026
Gwamnan Kebbi Ya Bayyana Shirin Sake Duba Albashin Malaman Firamare

Gwamna Idris Ya Rushe Majalisar Shugabannin Hukumar Zaɓe Ta Kebbi

September 8, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.