• English
  • Business News
Monday, July 14, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Ranar Malamai Ta Duniya: Yadda Yajin Aikin ASUU Ya Yi Wa Ilimi Katutu A Wuya

Ina Makomar Ilimi A Nijeriya?

by Sadiq
3 years ago
in Rahotonni
0
Ranar Malamai Ta Duniya: Yadda Yajin Aikin ASUU Ya Yi Wa Ilimi Katutu A Wuya
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Ranar 5 ga watan Oktoban kowace shekara, ita ce ranar da Majalisar Dinkin Duniya ta ware don bikin murnar ranar Malamai ta Duniya.

A yau malamai da dama a sassan duniya na murnar zagayowar wannan rana, amma a Nijeriya abun ba yabo ba fallasa.

  • Gwamnatin Jihar Imo Ta Amince Da Karin Matsayi Da Tallafin Kiwon Lafiya Kyauta Ga Ma’aikatanta
  • Zambar Naira Miliyan 55: ICPC Ta Fara Bin Diddigin Dan Kwangilar Dam Din Jihar Filato

Idan aka yi waiwaye musamman ga ilimin da ya shafi Jami’o’i wanda ya hadar da malamai da dalibai, a iya cewa ‘ba a rabu da Bukar ba an haifi Habu.’

ASUU da Gwamnatin Tarayyar Nijeriya sun shafe kimanin watanni bakwai zuwa takwas suna tafka takaddama kan yajin aikin da ya ki ya ki cinye kan wasu alkawura da malaman Jami’o’in suka tilas ne sai an biya musu.

Idan aka yi waiwaye za a fahimci cewar yajin aikin ASUU abu ne da aka shafe kimanin sama da shekaru 30 ana yinsa, a iya cewa kusan kowace gwamnati ta zo sai an yi wannan takaddama ta yajin aiki.

Labarai Masu Nasaba

Na Shiga Aikin Soja Domin Gujewa Yin Auren Fari Da Ƙuruciya — Buhari

Muhimman Abubuwa 10 Da Kowa Zai So Ya Sani Game Da Marigayi Shugaban Ƙasa Buhari

Wasu gwamnatocin kan yi kokarin ganin sun biya wasu bukatun da ASUU ke nema sannan ta dauki alkawarin cika wasu, wanda a wasu lokutan hakan ke jefa wata gwamnatin cikin kaka-na-kayi idan ta gaji wata gwamnatin.

A shekarar 2012, gwamnatin shugaba Goodluck Jonathan ta daukar wa ASUU alkawura wanda gwamnatin yanzu kuma ta gada, hakan ya sa ake ta kwan-gaba-kwan-baya.

Sai dai dag bangarenta, ASUU na ganin kamar gwamnatin yanzu na nuna halin ko in kula game da illar da yajin aikin ka iya haifar wa fagen ilimi.

Sannan ta soki lamirin gwamnatin tarayya kan tsarin biya ma’aikata albashi na IPPIS, wanda ta ce akwai lauje cikin nadi game da tsarin, wanda hakan ya sa tun fil-azal taki karbar tsarin.

Idan aka yi duba kuwa game da koma baya da yajin aikin ya haifar, a iya cewa akwai bukatar kowane bangare ya mayar da wukarsa don cimma matsaya tare da bai wa dalibai da su kan su malamai damar gudanar da ayyukansu yadda ya dace.

Yajin aikin ya kawo koma baya ga dalibai da yawa, musamman daliban da ke shirin kammala karatu da kuma wanda suke jiran a kammala duba kundin bincikensu don ba su takardar shaidar kammala Jami’a.

A bangaren malaman kuwa, su ma suna fama da rashin albashi, wanda hakan ya jefa da dama daga cikinsu cikin mayuwancin hali, musamman abin da ya shafi tafi da harkokin gida na yau da kull da kula da karatun yara.

Gashi gwamnatin tarayya ta kafa dokar duk wanda bai yi aiki ba, ba shi da albashi.

Wannan hali da ake ciki, ya sanya mutane da dama yin kiranye-kiranye ga gwamnatin tarayya da ma bangaren ASUU na ganin kowa ya dauki dangana, don ciyar da ilimi gaba da kuma kyankyasar da matasa masu ilimi da su jagoranci Nijeriya a nan gaba.

Da fatan kowane bangare zai duba na tsanaki, da bai wa zuciyarsa ruwan sanyi don daina tafasa kan wannan yajin aiki da ya ki ci ya ki cinyewa.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: Gwamnatin TarayyaJami'o'iMajalisar Dinkin DuniyaMalamaiRanar Malamai ta DuniyaTakaddamaTsawaita Yajin Aikin
ShareTweetSendShare
Previous Post

Zargin Badakalar Kudade: Kotu Ta Wanke Magu

Next Post

Dalibai Sun Yi Zanga-Zanga Kan Korarsu Daga Cibiyar Koyar Da Sana’o’i Ta Dangote A Kano

Related

Majalisar Dokokin Nijeriya Ta Sanar Da Dakatar Da Ayyukanta Saboda Alhinin Rasuwar Buhari
Labarai

Na Shiga Aikin Soja Domin Gujewa Yin Auren Fari Da Ƙuruciya — Buhari

13 hours ago
Ko Yanzu Tinubu Ya Yi Rawar Gani, Kuma Yana Ƙoƙari Sosai – Buhari
Rahotonni

Muhimman Abubuwa 10 Da Kowa Zai So Ya Sani Game Da Marigayi Shugaban Ƙasa Buhari

1 day ago
2027: Shugabannin Hamayya Sun Bazama Neman Goyon Baya A Yankunansu
Manyan Labarai

2027: Shugabannin Hamayya Sun Bazama Neman Goyon Baya A Yankunansu

2 days ago
2027: Masu Ruwa Da Tsaki Sun Bukaci A Kawo Karshen Matsalar Sayen Kuri’a
Rahotonni

2027: Masu Ruwa Da Tsaki Sun Bukaci A Kawo Karshen Matsalar Sayen Kuri’a

3 days ago
jam'iyyu
Rahotonni

Sarkakiyar Da Ke Tattare Da Zaben 2027 Da Yadda Za Ta Kaya

1 month ago
ASUU
Rahotonni

2027: An Yi Kira Ga Masu Mulki Da Su Rungumi Tafarkin Inganta Rayuwar Al’umma

1 month ago
Next Post
Dalibai Sun Yi Zanga-Zanga Kan Korarsu Daga Cibiyar Koyar Da Sana’o’i Ta Dangote A Kano

Dalibai Sun Yi Zanga-Zanga Kan Korarsu Daga Cibiyar Koyar Da Sana'o'i Ta Dangote A Kano

LABARAI MASU NASABA

Ministan Wajen Kasar Sin Ya Gana Da Takwaransa Na Rasha 

Ministan Wajen Kasar Sin Ya Gana Da Takwaransa Na Rasha 

July 14, 2025
Dangote Na Neman Izinin Gina Babbar Tashar Jiragen Ruwa Mafi Zurfi A Nijeriya

Dangote Na Neman Izinin Gina Babbar Tashar Jiragen Ruwa Mafi Zurfi A Nijeriya

July 14, 2025
Sin Da Amurka Na Kokarin Tabbatar Da Ci Gaban Da Aka Samu Na Yarjejeniyar London

Sin Da Amurka Na Kokarin Tabbatar Da Ci Gaban Da Aka Samu Na Yarjejeniyar London

July 14, 2025
Sarkin Maroko Ya Aike Da Ta’aziyya Ga Nijeriya Bisa Rasuwar Buhari

Sarkin Maroko Ya Aike Da Ta’aziyya Ga Nijeriya Bisa Rasuwar Buhari

July 14, 2025
Sin Na Maraba Da ’Yan Jaridar Duniya Da Su Halarci Bikin Cika Shekaru 80 Da Cimma Nasarar Yakin Kin Harin Japan Da Na Tafarkin Murdiya 

Sin Na Maraba Da ’Yan Jaridar Duniya Da Su Halarci Bikin Cika Shekaru 80 Da Cimma Nasarar Yakin Kin Harin Japan Da Na Tafarkin Murdiya 

July 14, 2025
Osimhen Na Dab Da Komawa Galatasaray Na Dindindin

Osimhen Na Dab Da Komawa Galatasaray Na Dindindin

July 14, 2025
Gwamnan Zamfara Ya Yi Ta’aziyyar Rasuwar Muhammadu Buhari

Gwamnan Zamfara Ya Yi Ta’aziyyar Rasuwar Muhammadu Buhari

July 14, 2025
Za A Iya Yarda Da Buhari Kan Kowace Irin Amana A Duniya — Abdulsalami

Za A Iya Yarda Da Buhari Kan Kowace Irin Amana A Duniya — Abdulsalami

July 14, 2025
Cinikayyar Shige Da Fice Ta Sin Ta Karu Da Kaso 2.9 Bisa Dari A Watanni Shida Na Farkon Bana

Cinikayyar Shige Da Fice Ta Sin Ta Karu Da Kaso 2.9 Bisa Dari A Watanni Shida Na Farkon Bana

July 14, 2025
Ƴan Bindiga Sun Kashe Mutane 1,111, Sun Yi Garkuwa Da 276 A Nijeriya Cikin Watan Yuni

Ƴan Bindiga Sun Kashe Mutane 1,111, Sun Yi Garkuwa Da 276 A Nijeriya Cikin Watan Yuni

July 14, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.