Leadership Hausa Newspapers
No Result
View All Result
  • LABARAI
  • WASANNI
  • RAHOTANNI
  • SIYASA
  • KASUWANCI
  • ADABI
  • RA’AYINMU
  • TATTAUNAWA
  • BIDIYO
  • MAKALAR YAU
  • LABARAI
  • WASANNI
  • RAHOTANNI
  • SIYASA
  • KASUWANCI
  • ADABI
  • RA’AYINMU
  • TATTAUNAWA
  • BIDIYO
  • MAKALAR YAU
No Result
View All Result
Leadership Hausa Newspapers
No Result
View All Result
Home RIGAR 'YANCI

Ranar Yaki Da Kanjamau: Hisbah Ta Kama Masu Yada Kanjamau Sama Da Guda 40

by Muhammad
December 2, 2020
in RIGAR 'YANCI
2 min read
Kanjamau
WhatsAppShare on FacebookShare on TwitterShare on Telegram

Daga Abdullahi Muhammad Sheka

 

samndaads

A yayin da a ke bikin ranar yaki cutar kanjamau ta duniya a ranar Talatar data gabata, Hukumar Hisbah ta Jihar Kano ta kama maza da mata kimanin 40, wadanda ke dauke da cutar Kanjamau kuma suke yada ta ga sauran jama’a a jihar.

Kwamandan Hisbah na jihar Kano, Malam Muhammad Harun Ibn Sina, ne ya bayyana haka, inda ya ce sun kama mata guda 32, sai kuma maza guda 10. Hukumar ta kama mutanen ne a kasuwar saida kayan gwari ta garin Badume da ke karamar Hukumar Bichi a jihar ta Kano.

Ya ce, mutum bakwai daga cikin matan sun san su na dauke da cutar, yayin da kuma ragowar matan sun fahimci hakan ne bayan sakamakon gwajin da a ka yi mu su ya fito. Ya ce, bayan da a ka bayyana mu su hakan ne, sai kuma su ka barke da kuka sakamakon rashin sanin cewa, su na dauke da cutar ta Kanjamau.

Ya cigaba da cewa, wasu daga cikin wadanda a ka kama din ba ’yan asalin Jihar Kano ba ne, sun zo ne daga makwabtan jihohi.

Majalisar Dinkin Duniya dai ta ware ranar daya ga watan Disambar kowace shekara a matsayin ranar cutar kanjamau ta duniya, don nuna goyan baya ga mutanen dake dauke da cutar da kuma tuna wadanda suka rigamu gidan gaskiya a sanadiyyar cutar ta kanjamau.

A cewar Hukumar lafiya ta duniya mutan miliyan 38 ne ke dauke da cutar ta kanjamau a fadin duniya. Haka kuma fiye da kaso sittin na wadannan mutane sun fito ne daga najiyar afrika.

 

SendShareTweetShare
Previous Post

Mun Amince Ka Karbo Wa Kano Bashin Biliyan N20 – Majalisa Ga Ganduje

Next Post

Majalisar Dattawa Ta Tabbatar Da Tazarcen Yakubu A Matsayin Shugaban INEC

RelatedPosts

’Yan Sandan Italiya

’Yan Sandan Italiya Sun Kama ’Yan Nijeriya 16 Masu Sana’ar Miyagun Kwayoyi

by Sulaiman Ibrahim
3 days ago
0

Rahotanni daga Kasar Italiya sun zo da ingacin cewa a...

miyagun kwayoyi

NDLEA Sun Cafke Mutum Uku Da Hodar Iblis A Legas

by Sulaiman Ibrahim
3 days ago
0

Hukumar hana sha da fataucin miyagun kwayoyi ta kasa (NDLEA),...

’Yan Fashi

’Yan Sanda Sun Tabbatar Da Kisan Dan Uwan Akanta Janar Na ​​Imo

by Sulaiman Ibrahim
3 days ago
0

’Yan sanda sun tabbatar da kisan dan uwan ​Akanta Janar...

Next Post
Tazarcen

Majalisar Dattawa Ta Tabbatar Da Tazarcen Yakubu A Matsayin Shugaban INEC

Domin sanya talla ko karin bayani a tuntube wannan numbar +2348126152609.

Leadership Epaper
ADVERTISEMENT
  • LABARAI
  • WASANNI
  • RAHOTANNI
  • SIYASA
  • KASUWANCI
  • ADABI
  • RA’AYINMU
  • TATTAUNAWA
  • BIDIYO
  • MAKALAR YAU
Advertise with us

© 2020 Leadership Group .

No Result
View All Result
  • LABARAI
  • WASANNI
  • RAHOTANNI
  • SIYASA
  • KASUWANCI
  • ADABI
  • RA’AYINMU
  • TATTAUNAWA
  • BIDIYO
  • MAKALAR YAU

© 2020 Leadership Group .

Go to mobile version