• English
  • Business News
Tuesday, August 26, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Rashin Hadin Kai Ke Dakile Ci Gaban Masana’antar Kannywood -Ayatullahi Tage

by Rabi'at Sidi Bala
4 months ago
in Nishadi
0
Rashin Hadin Kai Ke Dakile Ci Gaban Masana’antar Kannywood -Ayatullahi Tage
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Atatullahi Tage daya daga cikin jarumai a masana’antar shirya fina-finan Hausa ta Kannywood a wata hira da yayi da jaridar DCL Hausa a cikin shirinsu na sirrin daukaka ya tabo batutuwa da dama da suka shafi masana’antar ciki har da abin da ya kira shamaki ga ci gaban wannan babbar masana’anta da dubban al’umma ke neman abinci a cikinta.

Ni dai an haife ni a jihar Jigawa wanda cikin ikon Allah zama ya dawo dani nan Kano, sakamakon mahaifina da yake zaune a nan tsawon lokaci, abubuwa da dama sun sa ban yi zurfi a karatun zamani ba domin kuwa ko makarantar Sakandire ban kammala ba ko da na bar zuwa makaranta in ji Ayatullahi.

  • Me Ya Sa Fina-finai Masu dogon Zango A Masana’antar kannywood ke Zama Cin kwan Makauniya?
  • Kallo Daya Mutum Za Yi Min Ya Gane Masana’antar Kannywood Ta Canza Rayuwata -Farida Abdullahi

A lokacin da na zo Kano na yi sana’oi da dama kafin in zama abin da na zama a yanzu kama daga tallar kaset a baro, inda nike zuba kaset-kaset a baro ina zagayawa ina sayarwa, daga wannan sana’a ce na dawo harkar fim gadan-gadan, a wancan lokacin ban gamu da wani cikas yayin shigata harkar fim ba kamar yadda nike ji wasu na fadin matsalolin da suka fuskanata yayin shigiwa.

Dalili kuwa shi ne ko da na fara wannan harka ta fim bani da wani wanda ke tsawatar mani sakamakon iyayena da suka rasu, a wancan lokacin ma ba kowa ne ya damu da abin da na samu ko ya sameni ba, wasu mutane ma kallon wani mutum marar amfani suke yi mani, da haka dai na ci gaba da dagewa har Allah ya kawo ni inda nike yanzu ya kara da cewa.

Da yake amsa tambaya akan minene sirrin samun daukakarshi Tage ya ce ba komai ba ne sirrin samun daukaka illa Hakuri, Biyayya da kuma aiki tukuru, domin kuwa idan ka saka wadanann a zuciyarka to komai zai zo maka a cikin sauki ba tare da ka wahala ba, yanzu sau da dama mutane sun fi son su samu abu cikin sauki kuma cikin lokaci ba tare da sun wahala ba.

Labarai Masu Nasaba

Babban Burina A Harkar Fim Shi Ne Ganin Habakar Harshe Da Al’adun Hausa—Murtala Abdullah

Na Hadu Da Azzalumai Da Mayaudara Farkon Shigata Kannywood – Dan’duniya

Sai kaga mutum daga ya samu wata yar dama to do yake ace ya samu wata hanyar wulakanta wannan wanda yayi masa rana kokuma ya wuce shi a matsayi ko wani abin Duniya ba tareda la’akari da cewar wannna wanda ya koya maka to ya fika sanin komai a wannan harkar musamman ma a nan masana’antar Kannywood.

Don haka kamata ya yi ce mutane sun fahimci cewar babu ta yadda za a yi ka ci gaba matukar ka na da wata niyyar cin amanar wanda ya taimake ka ka kai wani matsayi na rayuwa, ni yanzu a matsayina na Ayatullahi Tage na yi biyayya ga maigidana Alhaji Tage wanda ya nuna mani hanya, ya rike ni kamar dan da ya haifa, kuma yake fatan duk wani alheri na Duniya ya same ni.

Ga shi yanzu ina ganin amfanin biyayyar domin kuwa duk wani abin da ake fatan samu na alheri a wannan masana’antar Allah ya nufe ni da samu kama daga mutunci, daukaka da kuma abin Duniya, don haka nike shawartar ‘yan uwa abokan sana’ara da ma sauran mutane da su kasance masu biyayya a duk inda suka samu kansu a rayuwa kuma kada su zamo masu girman kai ko nuna kyashi ga abin da wani ya samu domin kuwa  Allah mai iko ne akan kowa da komai zai iya baiwa wanda bai da shi, ya kuma amshe ga wanda ke da shi idan yaga dama.

Dangane da matsaloli ko kalubale da masana’antar Kannywood ke fuskanta Tage ya ce, ba komai ya janyo hakan ba illa rashin hadin kai a tsakanin masana’antar, duk al’ummar da aka ce babu hadin kai a tsakaninsu to lallai za ka samu wannan al’umma babu wani cigaba da suka samu, to amma matukar muka hada kanmu ya zamana mun zamo tsintsiya madaurinki daya babu wata baraka da za ta iya shigowa a cikinmu ya tabbatar.

Muddin aka ce akwai hassada ko kyashi a tsakaninmu to zai yi wuya mu dinga bai wa junanmu shawarwarin da za su ciyar da masana’antar gaba, sakamakon haka kuwa ba karamar illa zai janyo mana ba, don haka nike kira ga mahukunta da sauran al’umma da ke cikin Kannywood da mu daure mu hada kanmu domin mu kai wannan masana’antar inda ya kamata ta kasance.

Daga karshe ya bukaci mutane da ke furta kalaman tsinuwa ga jaruman fim da suji tsoron Allah su bari, idan kuma ba haka ba to su sani cewa su kansu basu san wadanda za su haifa ba, mai yiwuwa su haifi yaron da zai ji ya na sha’awar  harkar fim kuma ya shigo harkar a dama dashi, to idan haka ta faru wannan tsinuwar da sukayi wa jaruman fim za ta shafi yayansu da suma suka shiga cikin harkar fim din.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: KannywoodTage
ShareTweetSendShare
Previous Post

Barin Liverpool Ita Ce Shawara Mafi Wahala Da Na Taɓa Yankewa A Rayuwata -Alexander 

Next Post

Tsohon Dan Takarar Gwamna A NNPP A Jihar Ondo Ya Yi Murabus Daga Jam’iyyar

Related

Babban Burina A Harkar Fim Shi Ne Ganin Habakar Harshe Da Al’adun Hausa—Murtala Abdullah
Nishadi

Babban Burina A Harkar Fim Shi Ne Ganin Habakar Harshe Da Al’adun Hausa—Murtala Abdullah

2 days ago
Na Hadu Da Azzalumai Da Mayaudara Farkon Shigata Kannywood – Dan’duniya
Nishadi

Na Hadu Da Azzalumai Da Mayaudara Farkon Shigata Kannywood – Dan’duniya

1 week ago
Ko Maƙiyina Ba Na Yi Masa Fatan Tsintar Kansa A Halin Da Na Samu Kaina – Ummi Nuhu
Nishadi

Ko Maƙiyina Ba Na Yi Masa Fatan Tsintar Kansa A Halin Da Na Samu Kaina – Ummi Nuhu

2 weeks ago
Na Yi Lokacin Da Idan Aka Gan Ni Ake Gudu A Masana’antar Kannywood – Mai Dawayya
Nishadi

Na Yi Lokacin Da Idan Aka Gan Ni Ake Gudu A Masana’antar Kannywood – Mai Dawayya

2 weeks ago
An Ɗaura Auren Rahma Sadau A Kaduna
Nishadi

An Ɗaura Auren Rahma Sadau A Kaduna

2 weeks ago
Samun Kuɗi Ya Fi Samun Ɗaukaka Wahala A Kannywood -Baba Sadiƙ
Nishadi

Samun Kuɗi Ya Fi Samun Ɗaukaka Wahala A Kannywood -Baba Sadiƙ

3 weeks ago
Next Post
Tsohon Dan Takarar Gwamna A NNPP A Jihar Ondo Ya Yi Murabus Daga Jam’iyyar

Tsohon Dan Takarar Gwamna A NNPP A Jihar Ondo Ya Yi Murabus Daga Jam’iyyar

LABARAI MASU NASABA

An Yi Bikin Mu’ammalar Al’Adu Na SCO Na 2025 A Beijing

An Yi Bikin Mu’ammalar Al’Adu Na SCO Na 2025 A Beijing

August 25, 2025
Kuri’ar Jin Ra’ayin Jama’a Ta CGTN: Sin Ta Yi Rawar Gani A Fannin Bunkasa SCO

Kuri’ar Jin Ra’ayin Jama’a Ta CGTN: Sin Ta Yi Rawar Gani A Fannin Bunkasa SCO

August 25, 2025
CGTN Poll: Ba Da Kariya Shi Ne Tuna Baya—-Shekaru 80 Bayan Yakin Duniya Na II

CGTN Poll: Ba Da Kariya Shi Ne Tuna Baya—-Shekaru 80 Bayan Yakin Duniya Na II

August 25, 2025
Gwamnatin Tarayya Ta Yi Hasashen Ambaliyar Ruwa A Jihohin Arewa 15

Gwamnatin Tarayya Ta Sake Gargadin Jihohin Arewa 9 Kan Afkuwar Ambaliya 

August 25, 2025
Sojoji Sun Kashe ‘Yan Bindiga 3 Da Kubutar Da Mutum 16 Da Aka Sace A Kaduna

ECOWAS Za Ta Kaddamar Da Rundunar Yaki Da Ta’addanci Mai Jami’ai 260,000

August 25, 2025
Za A Watsa Shirin “Sha’awar Xi Jinping Ga Al’adu” a Manyan Kafofin Watsa Labarai Na Kasashen SCO

Za A Watsa Shirin “Sha’awar Xi Jinping Ga Al’adu” a Manyan Kafofin Watsa Labarai Na Kasashen SCO

August 25, 2025
Mauludi: Gwamnatin Kano Ta Sake Ɗage Ranar Komawa Makarantu

Zargin Babban Hadimin Gwamnan Kano Ya Karkatar Da Kuɗaɗen Jama’a Ba Gaskiya Ba Ne

August 25, 2025
Wani Rahoton Kasar Sin Ya Kalubalanci Halaccin Ayyukan Amurka Bisa Dogaro Da “’Yancin Zirga-zirga”

Wani Rahoton Kasar Sin Ya Kalubalanci Halaccin Ayyukan Amurka Bisa Dogaro Da “’Yancin Zirga-zirga”

August 25, 2025
Burkina Faso Da Mali Sun Yi Watsi Da Taron Sojojin Afirka A Nijeriya

Burkina Faso Da Mali Sun Yi Watsi Da Taron Sojojin Afirka A Nijeriya

August 25, 2025
Beijing Zai Bunkasa Amfani Da Fasahohin Zamani A Wuraren Adana Kayan Tarihi

Beijing Zai Bunkasa Amfani Da Fasahohin Zamani A Wuraren Adana Kayan Tarihi

August 25, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.