ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Tuesday, July 14, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Me Ya Sa Fina-finai Masu dogon Zango A Masana’antar kannywood ke Zama Cin kwan Makauniya?

by Rabilu Sanusi Bena
1 year ago
Zango

A wani rahoto da BBC Hausa ta fitar ya nuna yadda fina-finai masu dogon zango aka kasa kawo karshensu duk da tsawon lokacin da aka kwashe ana yin su, masu kallon fina-finan Hausa na ci gaba da tambayar wai me ya sa ba a kawo karshen fina-finan Hausa masu dogon zango, tambayar da har yanzu ba ta samu cikakkiyar amsa ba.

Daga cikin fina-finan da aka dade ana yi akwai fim din Izzar so mai dogon zango, wanda ya kasance cikin fina-finai masu dogon zango na farko-farko.

Fim din wanda aka fara sakin fitowa ta daya a ranar 12 ga watan Afrilun shekarar 2020, an yi fitowa (episode) har sau 100, sannan aka koma Izzar so sabon salo daga fitowa ta 101, zuwa fitowa ta 150, daga nan kuma sai su ka koma Izzar so takun farko, wanda shi ake yi yanzu, kuma ana fitowa ta 10.

ADVERTISEMENT
  • Gwamnati Za Ta Goyi Bayan Shirin Fim Kan Tarihin Shekaru 25 Na Dimokuraɗiyyar Nijeriya
  • Shirin Fim Kan Cikar Nijeriya Shekaru 25 A Kan Turbar Dimokuradiyya: Tasiri Da Muhimmanci

Sai dai ba fim din Izzar so ne ya fi dadewa ana yi ba, domin akwai fim din dadin kowa na tashar Arewa24, wanda zuwa yanzu an haura shekara 10 ana yi, fim din Gidan Badamasi wanda shi ma ake kallo a tashar Arewa24, a baya an sanar da kammala shi, amma yanzu an dawo an ci gaba.

Haka akwai finafinai da dama masu dogon zango da wasu suke ganin kamar ya dace a ce an dakatar da su, an shiga wasu, a fina-finan Hausa masu dogon, ana tunanin yanzu fim din Watarana a kano na Abubakar Bashir Maishadda, wanda yake da fitowa biyar kacal ne aka nuna shi a manhajar Arewa on demand na Arewa24 aka gama.

LABARAI MASU NASABA

Daraktan Hollywood Carl Rinsch Zai Shafe Watanni 30 A Gidan Gyaran Hali

Zan Iya Auren Namiji Komai Talaucinsa Muddin Muna Son Junanmu -Maryam Labarina

Wannan ya sa murnar da wasu ke yi ta komawa da haska finafinan Hausa masu dogon zango a tashar YouTube ta fara komawa ciki.

Me ya sa ba a gamawa din?

BBC Hausa ta ci gaba da cewa wani faifan bidiyo na wata tattaunawa da jagoran shirin Izzar so, Ahmad Lawan ya yi a tasharsa ta Bakori TV, ya ce masu kallo ne ba su gaji da kallon shirin ba, shi ya sa ba zai daina ba.

Ya ce kasancewar Youtube ya dade kudu, amma bai je arewacin Nijeriya ba ne ya sa su ka gwada domin su koya wa mutanen arewa kallon fim a YouTube, shi kuma wannan fim din ya na ciki, ko in ce shi ne daya tilo da ya koya wa mutane kallo a YouTube, kuma mutane ba su gaji da kallonsa ba,” in ji shi, inda ya kara da cewa, “ka ga babu dalilin da zai sa mu daina.”

Zango

Na biyu kuma shi ne akwai abubuwa na addini da muke kawowa da suke tasiri a zukatan al’umma kamar soyayyar Annabi SAW, sannan akwai abubuwa da dama da an manta su a cikin addini, idan muka nuna sai su zama matashiya, fitaccen jarumin ya kara da cewa a sanadiyar dim din akwai akalla mutum uku da suka karvi addinin musulunci, wanda a cewarsa hakan na cikin abubuwan da suka sa bai daina fim din ba.

Hakazalika fitaccen marubuci kuma furodusa, Nazir Adam Salihi, wanda yake cikin marubuta shirin dadin kowa mai dogon zango, kuma forudusan shirin Gidan Badamasi, ya ce nan gaba kadan za a fara kammala wasu shirye-shirye.

Ya ce “mu ne muka fara fina-finan nan masu dogon zango, kuma sama da shekara 10 ne da suke wuce ne muka fara zuwa yanzu, a Turai irin su Ingila kuma akwai finafinai masu dogon zango da aka yi shekara 65 ana yi ba a gama ba, ka ga ba za a yi gaggawar cewa ba a gama na Hausa mu da muka fara sama da shekara 10 da suka wuce.”

Sai dai ya ce akwai wasu fina-finai da aka gama daukarsu, “nan gaba kadan zuwa shekara mai zuwa za a kammala wasu fina-finan, a shiga wasu daban, a game da ko ana karancin labaran ne, marubucin ya ce Hausawa na da labarai masu kyau da inganci.

A karshe Salihi ya ba marubuta shawarar su dage da karatu da bincike da kuma natsuwa wajen rubuta labaransu, da yake jawabi kan lamarin, dokta Muhsin Ibrahim, malami a Jami’ar Cologne da ke Jamus ya ce wannan matsala ce ga masana’antar, wadda ba za ta haifa da mai ido ba.

A cewarsa, abin da yake faruwa shi ne masu shirya fina-finan su na fargabar idan suka daina fim din ba dole ba ne wanda za su fara din ya samu karvuwa kamar shi, sai dai ya ce wannan matsala ce babba saboda “babu labarin da ba shi da karshe kuma duk hakurin mai kallo ana iya kure shi.”

Ya ci gaba da cewa duk masana’antun fim na duniya da suka ci gaba a duk labarin da suka tsara, akwai farkonsa da tsakiya da karshe, shi ya sa nake ganin wannan rashin dabara ce saboda yan kallon da suke tunani dai dole sai sun kubuce musu, musamman idan sun samu wani fim da ya fi wannan.

Zango

Muhsin ya kara da cewa ya kamata a ce duk wani fim da za a fara, a san cewa za a iya fara wani wanda ya fi shi ko kuma ya gaza shi, misali shirin Labarina mai dogon zango, duk da cewa Aminu Saira ya rike sunan, ai na biyu ya fi na farko karvuwa, shi fim din kamfanin Uk Entertainment ai Garwashi ya fi Fatake karvuwa,” in ji shi.

Ya ce rashin gama fim yana rage wa masu kallo karsashin ci gaba da kallon saboda fargabar ko sun fara kallo, suna tunanin ba za a gama ba.

Zango
Rabilu Sanusi Bena
+ postsBio
  • Rabilu Sanusi Bena
    https://hausa.leadership.ng/author/rabilu-sanusi-bena/
    FIFA Na Nazarin Faɗaɗa Gasar Kofin Duniya Zuwa Ƙasashe 64
  • Rabilu Sanusi Bena
    https://hausa.leadership.ng/author/rabilu-sanusi-bena/
    Harry Kane: Lashe Kofin Duniya Ya Fi Mini Muhimmanci Fiye da Takalmin Zinare
  • Rabilu Sanusi Bena
    https://hausa.leadership.ng/author/rabilu-sanusi-bena/
    Kofin Duniya: Na fi Son Faransa Ta Kara Da Argentina A Wasan Ƙarshe A Kan Ingila — Vieira
  • Rabilu Sanusi Bena
    https://hausa.leadership.ng/author/rabilu-sanusi-bena/
    Argentina Ta Kai Zagayen Kwata Fainal Bayan Nunawa Egypt Ƙwanji

MASU ALAKA

Labarin Farfesoshi Tagwaye Da Suka Yi Karatun Digiri Tare Suna Aiki Tare A Wuri Ɗaya
Labarai

Daraktan Hollywood Carl Rinsch Zai Shafe Watanni 30 A Gidan Gyaran Hali

July 12, 2026
Zan Iya Auren Namiji Komai Talaucinsa Muddin Muna Son Junanmu -Maryam Labarina
Nishadi

Zan Iya Auren Namiji Komai Talaucinsa Muddin Muna Son Junanmu -Maryam Labarina

June 14, 2026
Gidajen Gala Ne Kadai Mafita Ga Masana’antar Kannywood – Falalu Dorayi
Nishadi

Gidajen Gala Ne Kadai Mafita Ga Masana’antar Kannywood – Falalu Dorayi

June 14, 2026
Next Post
Sirrin da ke Tattare da Ganyen Mangwaro Ga Lafiyar Ɗan Adam

Sirrin da ke Tattare da Ganyen Mangwaro Ga Lafiyar Ɗan Adam

LABARAI MASU NASABA

CMG Ya Gudanar Da Babban Taron Masu Kirkirar Manyan Shirye-Shirye Da Fina-Finai

CMG Ya Gudanar Da Babban Taron Masu Kirkirar Manyan Shirye-Shirye Da Fina-Finai

July 14, 2026
Tsohon Sanatan Gombe, Bayero Nafada, Ya Fice Daga PDP Bayan Ganawa da Shugabannin APC

Tsohon Sanatan Gombe, Bayero Nafada, Ya Fice Daga PDP Bayan Ganawa da Shugabannin APC

July 14, 2026
ADC Ta Nemi A Binciki Nafiu Bala Bayan INEC Ta Ƙaryata Iƙirarinsa

ADC Ta Nemi A Binciki Nafiu Bala Bayan INEC Ta Ƙaryata Iƙirarinsa

July 14, 2026
Sojoji Sun Kashe ’Yan Ta’adda 3, Sun Ƙwato Makamai A Sakkwato

Sojoji Sun Daƙile Harin ISWAP A Borno

July 14, 2026
Na Yi Tsayin-daka Domin Cika Alƙawarin Ƙasata Nijeriya

Na Yi Tsayin-daka Domin Cika Alƙawarin Ƙasata Nijeriya

July 14, 2026
Tsaka mai wuyar Infantino da Koma bayan mulkin yamma

Tsaka mai wuyar Infantino da Koma bayan mulkin yamma

July 14, 2026
“Buhari Ya Taɓa tambaya Ta Mutane Nawa Na Kashe Saboda Yawan Azumin Dana Ke Yi”

“Buhari Ya Taɓa tambaya Ta Mutane Nawa Na Kashe Saboda Yawan Azumin Dana Ke Yi”

July 14, 2026
Gwamnatin Tarayya Ta Ce Za A Gurfanar Da Tubabbun ’Yan ta’addan Da Suka Sake Aikata Manyan Laifuka

Gwamnatin Tarayya Ta Ce Za A Gurfanar Da Tubabbun ’Yan ta’addan Da Suka Sake Aikata Manyan Laifuka

July 14, 2026
Tinubu Ya Gana da Gwamnan Kwara Bayan Harin Ta’addanci Da Ya Yi Ajalin Sama Da Mutane 160

Kyawawan Manufofin Buhari Za Su Ci Gaba Da Yi Wa ’Yan Nijeriya Tasiri – Tinubu

July 14, 2026
Abin Da Ake Kira “Hukuncin Tekun Kudancin Sin” Da Aka Yanke Wa Sin Na Kashin Kanta Ba Shi Da Wani Amfani

Abin Da Ake Kira “Hukuncin Tekun Kudancin Sin” Da Aka Yanke Wa Sin Na Kashin Kanta Ba Shi Da Wani Amfani

July 13, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.