• English
  • Business News
Thursday, May 15, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Rashin Tabbas Ya Dabaibaye Dorewar Aikin Noma Da Gwamnatin Buhari Ta Kirkiro

by Abubakar Abba
2 years ago
in Noma Da Kiwo
0
Rashin Tabbas Ya Dabaibaye Dorewar Aikin Noma Da Gwamnatin Buhari Ta Kirkiro
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Shekaru da dama da suka wuce,  fannin aikin noma  a kasar ya fuskanci kalubale da dama da suka hada da rashin zuba kudi a fannin.

Sai dai,  labarin ya canza tun a shekarar 2016 bayan da gwamnatin shugaban kasa  Muhammadu Buhari ta zuba biliyoyin Naira a fanin aikin noma.

  • INEC Ta Raba Muhimman Kayyayakin Zabe Don Kammala Zaben Gwamnan Kebbi
  • Xi Jinping Ya Gana Da Shugaban Kasar Brazil

Gwamnatinsa ta zo da sabbin tsare-tsare da shirye-shirye domin bunkasa aikin naoma da samar da wadacaccen abinci a kasar, musamman domin a Nijeriya ta rage yin dogaro akan shigo da amfanin gona zuwa cikin kasar nan daga ketare, inda hakan ya sa aka samu rage kashe biliyoyin dalar Amurka don shigo da amfanin.

Wasu daga cikin shirye-shiyen da gwamnatin ta kirkiro da su sun hadada, shirin samar da takin zamani na fadar shugaban kasa (PFI), shirin aikin noma na Anchor Borrowers da sauransu.

Sai dai, abin takaici, wasu daga cikin wadannan shirye-shiyen masu kayu, cin hanci da rashawa ya yi masu kakatutu, ko kuma wasu mutanen da ba manoma sun mamaye shirye-shiyen.

Labarai Masu Nasaba

Gwamnatin Tarayya Ta Gabatar Da Wasu Shirye-shirye Na Bunƙasa Kiwon Shanu

Nazari Kan Dabarun Taimaka Wa Masu Kiwon Kifi Domin Jurewa Sauyin Yanayi

Misali shirin aikin noma na Anchor Borrowers gwamnatin Buhari ce ta kirkiro da shi a shekarar 2016, wanda a tun da farko gwmanatin ta kebe Naira biliyan  40, don a tallafawa manoman ta hanyar ba su rancen da bai da kudin ruwa.

Tun a wancan lokacin, sama da Naira tirilyan 1.5 aka rabarwa da manoman a a tsakiyar shekarar 2022 a karkashin shirin.

A cewar rahoton da aka fitar a watan da ya wuce, Asusun bayar da lamuni na dunya IMF, ya dora jimlar kan Naira tiriliyan  1.9 tare da kashi 25 a cikin dari kacal da aka karbo, inda kuma ba a iya karbo  Naira tiriliyan 1.4 ba.

Bugu da kari, CBN ta hanyar mukaddashin Darktan sashen samar da bayanai Dakta AbdulMumin Isa ya karyata wannan ikirarin, inda ya jaddada cewa, Bnkin ya karbo kimain kashi 52 a cikn dari na kudin.

Hakazalika, bayan kaddamar da shirin na Anchor Borrowers a 2016, mutane da ba su da wata nasaba da aikin noma, sun ta kafa kungiyoyi kayan masarufi, don kawai su samu rancen kudin na noma.

Misali, a ranar 16 ga watan Maris na 2023, ofishin hukumar EFFC na shiyyar jihar Legas, ta gurfanar da wani mai suna Uche Chigozie Edwin kan damfarar kungiyar masu noman Masara da sarrafa Naira biliyan 1.4.

Har ila yau, akwai kuma zargin badakalar  baya da rance Naira biliyan 5.6 na shirin noman Alkama da ke a karkashin kulawa hukumar (NIRSAL), inda hakan ya janyo aka kori wasu ma’aikatan hukumar daga aikinsu.

Bugu da kari, akwai kuma zargin harkalla a shirin samar da takin zamani na fadar shugaban kasa.

Shugaba Buhari ya kadamar da shirin na (PFI)  a watan Disambar 2016 bisa yakinin kara karfafa sarrafa takin zamani a cikin kasar nan.

Sai dai, abin takaici cin hanci da rashawa ya bulla a cikin shirin, inda hakan ya haifar da rubuce-rubucen korafi kan zargin wasu jam’ian da ke a cikin shirin kan karkatar da kudaden da aka zuba don samar da takin zamani, da suka kai yawan Naira biliyan 300

Hakan ya tilasta gwamnatin tarayya sake yiwa shirin garambawul.

Kusan shekaru biyu ke nan zuwa yanzu, shirin ya zama tamkar na jeka na yi ka, inda takin zaman ya zamowa maomna kasar nan, musamman kananan manoma tamkar Gwal, ganin cewa farashin Buhu daya ya haura Naira 25,000.

Mafitar akan wannan matslar kamar yadda shugaban manoma na gasakiya na kasa Architect Kabiru Ibrahim, dole ne gwamnati tarayya mai zuwa ta yi dukkan mai yuwa don ganin shirye-shiryen sun ci gaba da daorewa

Ibrahim ya kuma shawarci zababben shugaban  kaar mai jiran Gado Boal Tinubu da ya nada minitan aikin gona da raya karkara bisa cancanta wanda kuma ya san yadda daukacin hukomomin aikin noma za su iya gudanar da yyukan su yadda ya kamata.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: BuhariKiwoNoma
ShareTweetSendShare
Previous Post

Sin Na Adawa Da Matakin Amurka Na Sanya Kamfanonin Kasar Cikin Jerin Sunayen Kamfanonin Da Ta Sanya Musu Takunkumi

Next Post

Ridi, Citta, Zoborodo Na Kan Gaba A Jerin Amfanin Gonan Da Ake Fitar Wa A Tashar Apapa

Related

Gwamnatin Tarayya Ta Gabatar Da Wasu Shirye-shirye Na Bunƙasa Kiwon Shanu
Noma Da Kiwo

Gwamnatin Tarayya Ta Gabatar Da Wasu Shirye-shirye Na Bunƙasa Kiwon Shanu

4 days ago
Nazari Kan Dabarun Taimaka Wa Masu Kiwon Kifi Domin Jurewa Sauyin Yanayi
Noma Da Kiwo

Nazari Kan Dabarun Taimaka Wa Masu Kiwon Kifi Domin Jurewa Sauyin Yanayi

5 days ago
Noman 2025: Dole Ne Manoma Su Kiyaye Hasashen Hukumar NiMet
Noma Da Kiwo

Noman 2025: Dole Ne Manoma Su Kiyaye Hasashen Hukumar NiMet

5 days ago
Masana Sun Bayyana Ingancin TELA Maize Ga Rayuwar Al’umma
Noma Da Kiwo

Masana Sun Bayyana Ingancin TELA Maize Ga Rayuwar Al’umma

6 days ago
Nazari Kan Dabarun Gargajiya Domin Jawo Hankalin Zuma
Noma Da Kiwo

Nazari Kan Dabarun Gargajiya Domin Jawo Hankalin Zuma

2 weeks ago
Ambaliya: Yankunan Da Ba Za Su Yi Noma A Kakar Bana Ba A Jihar Neja
Noma Da Kiwo

Ambaliya: Yankunan Da Ba Za Su Yi Noma A Kakar Bana Ba A Jihar Neja

2 weeks ago
Next Post
Ridi, Citta, Zoborodo Na Kan Gaba A Jerin Amfanin Gonan Da Ake Fitar Wa A Tashar Apapa

Ridi, Citta, Zoborodo Na Kan Gaba A Jerin Amfanin Gonan Da Ake Fitar Wa A Tashar Apapa

LABARAI MASU NASABA

Shawarwarin Raya Tattalin Arziki Da Cinikayya Tsakanin Sin Da Amurka Sun Haifar Da Managarcin Sakamako

Shawarwarin Raya Tattalin Arziki Da Cinikayya Tsakanin Sin Da Amurka Sun Haifar Da Managarcin Sakamako

May 15, 2025
‘Yan Bindiga Sun Sace Sarki Mai Daraja Ta Ɗaya A Kogi

‘Yan Bindiga Sun Sace Sarki Mai Daraja Ta Ɗaya A Kogi

May 15, 2025
Shugaba Xi Ya Amsa Wasikar Da Jagoran Da Ya Kafa Majalisar Cinikayya Ta Denmark A Sin Ya Aike Masa

Shugaba Xi Ya Amsa Wasikar Da Jagoran Da Ya Kafa Majalisar Cinikayya Ta Denmark A Sin Ya Aike Masa

May 15, 2025
An Bayar Da ₦95m Ga Iyalan Maharba Da Mutanen Da ‘Yan Ta’adda Suka Kashe A Bauchi

An Bayar Da ₦95m Ga Iyalan Maharba Da Mutanen Da ‘Yan Ta’adda Suka Kashe A Bauchi

May 15, 2025
NNPP Ta Tafka Asara, Ƴan Majalisa 2 Daga Kano Sun Koma APC

NNPP Ta Tafka Asara, Ƴan Majalisa 2 Daga Kano Sun Koma APC

May 15, 2025
Ya Kamata A Kori Ministan Ilimi – Aisha Yesufu

Ya Kamata A Kori Ministan Ilimi – Aisha Yesufu

May 15, 2025
Lassa Da Shawara Sun Kashe Mutum 183 A Jihohi 36 Da Abuja

Lassa: Mutane 138 Sun Rasu, 717 Sun Kamu A Jihohi 18 – NCDC

May 15, 2025
Wa Suka Fi Cancanta A Nada Ministocin Tinubu?

Tinubu Ya Ƙaddamar Da Dakarun Da Za Suke Tsaron Daji Don Yaƙar ‘Yan Ta’adda

May 15, 2025
ECOWAS Na Fuskantar Matsala Saboda Rashin Kyakkyawan Shugabanci – Bala Mohammed 

ECOWAS Na Fuskantar Matsala Saboda Rashin Kyakkyawan Shugabanci – Bala Mohammed 

May 15, 2025
‘Yansanda Sun Musanta Zargin Kai Wa ‘Yan Bindiga Abinci Ta Jirgin Sama A Kogi

‘Yansanda Sun Musanta Zargin Kai Wa ‘Yan Bindiga Abinci Ta Jirgin Sama A Kogi

May 15, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.