• English
  • Business News
Sunday, August 3, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Rashin Tabbas Ya Dabaibaye Dorewar Aikin Noma Da Gwamnatin Buhari Ta Kirkiro

by Abubakar Abba
2 years ago
in Noma Da Kiwo
0
Rashin Tabbas Ya Dabaibaye Dorewar Aikin Noma Da Gwamnatin Buhari Ta Kirkiro
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Shekaru da dama da suka wuce,  fannin aikin noma  a kasar ya fuskanci kalubale da dama da suka hada da rashin zuba kudi a fannin.

Sai dai,  labarin ya canza tun a shekarar 2016 bayan da gwamnatin shugaban kasa  Muhammadu Buhari ta zuba biliyoyin Naira a fanin aikin noma.

  • INEC Ta Raba Muhimman Kayyayakin Zabe Don Kammala Zaben Gwamnan Kebbi
  • Xi Jinping Ya Gana Da Shugaban Kasar Brazil

Gwamnatinsa ta zo da sabbin tsare-tsare da shirye-shirye domin bunkasa aikin naoma da samar da wadacaccen abinci a kasar, musamman domin a Nijeriya ta rage yin dogaro akan shigo da amfanin gona zuwa cikin kasar nan daga ketare, inda hakan ya sa aka samu rage kashe biliyoyin dalar Amurka don shigo da amfanin.

Wasu daga cikin shirye-shiyen da gwamnatin ta kirkiro da su sun hadada, shirin samar da takin zamani na fadar shugaban kasa (PFI), shirin aikin noma na Anchor Borrowers da sauransu.

Sai dai, abin takaici, wasu daga cikin wadannan shirye-shiyen masu kayu, cin hanci da rashawa ya yi masu kakatutu, ko kuma wasu mutanen da ba manoma sun mamaye shirye-shiyen.

Labarai Masu Nasaba

Manyan Ƙalubale Takwas Da Ke Shafar Farashin Tumatir

Asusun NADF, OCP Da Gwamnatin Katsina Sun Kaddamar Da Noman Hekta 50

Misali shirin aikin noma na Anchor Borrowers gwamnatin Buhari ce ta kirkiro da shi a shekarar 2016, wanda a tun da farko gwmanatin ta kebe Naira biliyan  40, don a tallafawa manoman ta hanyar ba su rancen da bai da kudin ruwa.

Tun a wancan lokacin, sama da Naira tirilyan 1.5 aka rabarwa da manoman a a tsakiyar shekarar 2022 a karkashin shirin.

A cewar rahoton da aka fitar a watan da ya wuce, Asusun bayar da lamuni na dunya IMF, ya dora jimlar kan Naira tiriliyan  1.9 tare da kashi 25 a cikin dari kacal da aka karbo, inda kuma ba a iya karbo  Naira tiriliyan 1.4 ba.

Bugu da kari, CBN ta hanyar mukaddashin Darktan sashen samar da bayanai Dakta AbdulMumin Isa ya karyata wannan ikirarin, inda ya jaddada cewa, Bnkin ya karbo kimain kashi 52 a cikn dari na kudin.

Hakazalika, bayan kaddamar da shirin na Anchor Borrowers a 2016, mutane da ba su da wata nasaba da aikin noma, sun ta kafa kungiyoyi kayan masarufi, don kawai su samu rancen kudin na noma.

Misali, a ranar 16 ga watan Maris na 2023, ofishin hukumar EFFC na shiyyar jihar Legas, ta gurfanar da wani mai suna Uche Chigozie Edwin kan damfarar kungiyar masu noman Masara da sarrafa Naira biliyan 1.4.

Har ila yau, akwai kuma zargin badakalar  baya da rance Naira biliyan 5.6 na shirin noman Alkama da ke a karkashin kulawa hukumar (NIRSAL), inda hakan ya janyo aka kori wasu ma’aikatan hukumar daga aikinsu.

Bugu da kari, akwai kuma zargin harkalla a shirin samar da takin zamani na fadar shugaban kasa.

Shugaba Buhari ya kadamar da shirin na (PFI)  a watan Disambar 2016 bisa yakinin kara karfafa sarrafa takin zamani a cikin kasar nan.

Sai dai, abin takaici cin hanci da rashawa ya bulla a cikin shirin, inda hakan ya haifar da rubuce-rubucen korafi kan zargin wasu jam’ian da ke a cikin shirin kan karkatar da kudaden da aka zuba don samar da takin zamani, da suka kai yawan Naira biliyan 300

Hakan ya tilasta gwamnatin tarayya sake yiwa shirin garambawul.

Kusan shekaru biyu ke nan zuwa yanzu, shirin ya zama tamkar na jeka na yi ka, inda takin zaman ya zamowa maomna kasar nan, musamman kananan manoma tamkar Gwal, ganin cewa farashin Buhu daya ya haura Naira 25,000.

Mafitar akan wannan matslar kamar yadda shugaban manoma na gasakiya na kasa Architect Kabiru Ibrahim, dole ne gwamnati tarayya mai zuwa ta yi dukkan mai yuwa don ganin shirye-shiryen sun ci gaba da daorewa

Ibrahim ya kuma shawarci zababben shugaban  kaar mai jiran Gado Boal Tinubu da ya nada minitan aikin gona da raya karkara bisa cancanta wanda kuma ya san yadda daukacin hukomomin aikin noma za su iya gudanar da yyukan su yadda ya kamata.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: BuhariKiwoNoma
ShareTweetSendShare
Previous Post

Sin Na Adawa Da Matakin Amurka Na Sanya Kamfanonin Kasar Cikin Jerin Sunayen Kamfanonin Da Ta Sanya Musu Takunkumi

Next Post

Ridi, Citta, Zoborodo Na Kan Gaba A Jerin Amfanin Gonan Da Ake Fitar Wa A Tashar Apapa

Related

Manyan Ƙalubale Takwas Da Ke Shafar Farashin Tumatir
Noma Da Kiwo

Manyan Ƙalubale Takwas Da Ke Shafar Farashin Tumatir

1 day ago
Sin Ta Gaggauta Aikin Gyara Da Kyautata Ababen Aikin Gona
Noma Da Kiwo

Asusun NADF, OCP Da Gwamnatin Katsina Sun Kaddamar Da Noman Hekta 50

1 week ago
Gwamnatin Tarayya Na Shirin Dakatar Da Shigo Da Kifi Daga Ketare
Noma Da Kiwo

Gwamnatin Tarayya Na Shirin Dakatar Da Shigo Da Kifi Daga Ketare

1 week ago
Abinci
Noma Da Kiwo

Dalilin Gwamnatin Tarayya Na Yin Hadaka Da Jihar Nasarawa Don Bunkasa Noma

2 weeks ago
Shettima
Noma Da Kiwo

Nijeriya Za Ta Rika Samun Naira Tiriliyan Uku A Aikin Tatsar Rogo Duk Shekara – Kashim

2 weeks ago
Wa’adin Da Tinubu Ya Bai Wa Manoman Da Suka Ci Bashin ‘Anchor Borrowers’ Ya Cika
Noma Da Kiwo

Dalilin Ware Naira Biliyan 19.5 Da Asusun Bunkasa Aikin Noma Ya Yi

3 weeks ago
Next Post
Ridi, Citta, Zoborodo Na Kan Gaba A Jerin Amfanin Gonan Da Ake Fitar Wa A Tashar Apapa

Ridi, Citta, Zoborodo Na Kan Gaba A Jerin Amfanin Gonan Da Ake Fitar Wa A Tashar Apapa

LABARAI MASU NASABA

Ministan Yaɗa Labarai Ya Buƙaci A Kwantar Da Hankali Kan Dakatar Da Gidan Rediyon Badeggi FM

Ministan Yaɗa Labarai Ya Buƙaci A Kwantar Da Hankali Kan Dakatar Da Gidan Rediyon Badeggi FM

August 3, 2025
Hanyoyin Da Za A Bi A Rage Yawan Zawarawa

Hanyoyin Da Za A Bi A Rage Yawan Zawarawa

August 3, 2025
Ban Yi Danasanin Shiga Harkar Fim Ba – Baba Ƙarami

Ban Yi Danasanin Shiga Harkar Fim Ba – Baba Ƙarami

August 3, 2025
Gwamnatin Tarayya Za Ta Aiwatar da Shirin Daƙile Sulalewar Kuɗaɗen Haraji

Gwamnatin Tarayya Za Ta Aiwatar da Shirin Daƙile Sulalewar Kuɗaɗen Haraji

August 3, 2025
Dalilin Da Ya Sa Kashi 50 Na Ƙanana Da Matsakaitan Sana’oi Ke Durƙushewa A Nijeriya– FRC

Dalilin Da Ya Sa Kashi 50 Na Ƙanana Da Matsakaitan Sana’oi Ke Durƙushewa A Nijeriya– FRC

August 3, 2025
Sanata Buba Ya ƙaryata Jita-jitar Cewa Majalisa Ta Amince da ƙirƙiro Sabbin Jihohi 12

Sanata Buba Ya ƙaryata Jita-jitar Cewa Majalisa Ta Amince da ƙirƙiro Sabbin Jihohi 12

August 2, 2025
Menene Sirrin Nasarar Ƴan Wasan Nijeriya Mata A Ƙwallon Ƙafa?

Menene Sirrin Nasarar Ƴan Wasan Nijeriya Mata A Ƙwallon Ƙafa?

August 2, 2025
Kashi 40 Na Ƙananan Yara A Nijeriya Ke Fuskantar Barazanar Yunwa — Rahoto

Etsu Nupe Ya Jaddada Buƙatar Sama Wa Sarakunan Gargajiya Gurbi A Tsarin Mulki

August 2, 2025
Babban Bankin Sin Ya Yi Alkawarin Ba Da Goyon Baya Ga Kirkire-Kirkire Da Sayayya

Babban Bankin Sin Ya Yi Alkawarin Ba Da Goyon Baya Ga Kirkire-Kirkire Da Sayayya

August 2, 2025
Fim Na Kisan Kiyashin Nanjing Ya Mamaye Kasuwar Fina-Finan Sin Bisa Samun Kudin Shiga Yuan Biliyan Daya

Fim Na Kisan Kiyashin Nanjing Ya Mamaye Kasuwar Fina-Finan Sin Bisa Samun Kudin Shiga Yuan Biliyan Daya

August 2, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.