• English
  • Business News
Wednesday, September 10, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Rashin Tsaro: Garuruwa Sama Da 30 Sun Gudanar Da Zanga-zanga A Zamfara

by Rabi'u Ali Indabawa
4 weeks ago
in Kotu Da Ɗansanda
0
Rashin Tsaro: Garuruwa Sama Da 30 Sun Gudanar Da Zanga-zanga A Zamfara
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Tsoro ya haifar da rarrabuwar kawuna a kananan hukumomin Tureta da Dange/Shuni na Jihar Sokoto, yayin da hare-haren ‘yan bindiga ke ci gaba da addabar al’umma, lamarin da ya tilasta wa daruruwan iyalai tserewa daga gidajensu cikin halin kunci.

Tsawon watanni, mazauna yankin – musamman mata da yara – sun yi gudun hijira a cikin dare, suna neman mafaka a buɗaɗɗen wurare, dazuzzuka, da karkashin bishiyoyi, ba su iya kwana a cikin gida saboda ci gaba da barazanar tashin hankali.

  • Hukumar NABDA Ta Bukaci Musulmi Su Cire Fargabar Amfani Da Fasahar Alkinta Halittu
  • Muhimman Batutuwan Da Za Mu Yi La’akari Da Su Kafin Amincewa Da Bukatun Kirkirar Sabbin Jihohi — Majalisar Dattawa

“Ban shiga gidana ba cikin wata uku,” in ji Halima, wata uwa mai ‘ya’ya hudu daga Tureta.

“Kowane dare, muna kwana a karkashin bishiya, muna rayuwa cikin tsoro, tare da fargabar duk sautin da muka ii ‘yan fashi.”

Zanga-zanga a Zamfara

Labarai Masu Nasaba

Zargin Shan Guba: ’Yan Nijeriya Biyu Sun Mutu A Libya

Yadda Wani Mai Unguwa Ya Yi Wa ‘Yar Shekara 12 Fyade A Gombe

A halin da ake ciki, mazauna kauyuka sama da 30 na gundumar Dan-Isa da Kagara a Karamar Hukumar Kaura-Namoda ta Jihar Zamfara sun gudanar da zanga-zangar lumana a Gusau babban birnin Jihar a ranar Alhamis.

Sun yi kira da gwamnati ta sa baki cikin gaggawa domin magance matsalar rashin tsaro da ke kara kamari a cikin al’ummominsu.

Masu zanga-zangar wadanda galibinsu mata da yara ne suka yi tattaki a kan titunan Gusau, rike da kwalaye masu dauke da saonni kamar haka: “Muna Bukatar Zaman Lafiya a Kauyukan Kaura-Namoda,” “Ya Kamata Gwamna Dauda Lawal da Matawalle Su Cece Mu,” “Ana Kashe Jama’ar Mu Kullum.

Da yake jawabi ga manema labarai a gaban gidan gwamnati da ke Gusau, daya daga cikin shugabannin al’ummar yankin, Lawal Kamilu daga Dan-Isa, ya bayyana zanga-zangar a matsayin kukan neman taimako bayan shafe shekaru ana kai hare-haren ‘yan fashi, da sace-sace da kashe-kashe.

“Mun fito ne daga kauyuka kusan 30. Mafi yawanmu a nan mata ne da kananan yara saboda yawancin mazajenmu ko dai an kashe su ko kuma ‘yan bindiga sun yi garkuwa da su,” in ji Kamilu.

 

Martanin gwamnati

martanin da ya mayar, Kanar Ahmed Usman (mai ritaya), mai bai wa gwamnan Jihar Sokoto shawara kan harkokin tsaro, ya amince da zanga-zangar amma ya ce gwamnati na daukar matakan dawo da zaman lafiya.

“Jihar tana ci gaba da gudanar da ayyuka tare da hadin gwiwar jami’an tsaro, wanda aka samu gagarumar nasara,” in ji Kanar Usman.

“Saboda irin namijin kokarin da jami’an tsaronmu na yau da kullum da masu gadin al’umma suke yi, muna hada gwiwa da shugabannin al’umma domin dawo da zaman lafiya.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: Tsaro
ShareTweetSendShare
Previous Post

An Kama Wakilin Jam’iyya Da Miliyan ₦29 Zai Sayi Ƙuri’a A Kaduna

Next Post

An Sake Daure Dan Nijeriya Shekara Biyar A Birtaniya Kan Laifin Fyade

Related

Zargin Shan Guba: ’Yan Nijeriya Biyu Sun Mutu A Libya
Kotu Da Ɗansanda

Zargin Shan Guba: ’Yan Nijeriya Biyu Sun Mutu A Libya

3 weeks ago
‘Yansanda Sun Kama Ɗan Bindiga Da Kuɗin Fansa Naira Miliyan 5 A Delta
Kotu Da Ɗansanda

Yadda Wani Mai Unguwa Ya Yi Wa ‘Yar Shekara 12 Fyade A Gombe

3 weeks ago
Garkuwa Da Mutane: Wani Ba’indiye Da Ake Zargi Ya Nemi Shafa Wa ‘Yan Nijeriya Kashin Kaji
Kotu Da Ɗansanda

Garkuwa Da Mutane: Wani Ba’indiye Da Ake Zargi Ya Nemi Shafa Wa ‘Yan Nijeriya Kashin Kaji

3 weeks ago
An Sake Daure Dan Nijeriya Shekara Biyar A Birtaniya Kan Laifin Fyade
Kotu Da Ɗansanda

An Sake Daure Dan Nijeriya Shekara Biyar A Birtaniya Kan Laifin Fyade

4 weeks ago
‘Yansanda Sun Ceto Mutum 21 Da Aka Sace, Sun Kwato N4.8m Kuɗin Fansa
Kotu Da Ɗansanda

‘Yansanda Sun Kama ‘Yan Fashi Tare Da Kwato Makamai A Delta

4 weeks ago
An Yanke Wa Mai Gadi Da Mai Dafa Abinci Hukuncin Kisa Kan Kashe Tsohon Kwamishina A Katsina
Kotu Da Ɗansanda

An Yanke Wa Mai Gadi Da Mai Dafa Abinci Hukuncin Kisa Kan Kashe Tsohon Kwamishina A Katsina

1 month ago
Next Post
An Sake Daure Dan Nijeriya Shekara Biyar A Birtaniya Kan Laifin Fyade

An Sake Daure Dan Nijeriya Shekara Biyar A Birtaniya Kan Laifin Fyade

LABARAI MASU NASABA

Kasar Sin Ta Zama Dandalin Karfafa Cudanya Da Cinikayya Tsakanin Kasa Da Kasa

Kasar Sin Ta Zama Dandalin Karfafa Cudanya Da Cinikayya Tsakanin Kasa Da Kasa

September 9, 2025
IATF 2025: Zamfara A Shirye Ta Ke Wajen Maraba Da Masu Zuba Jari – Gwamna Lawal 

IATF 2025: Zamfara A Shirye Ta Ke Wajen Maraba Da Masu Zuba Jari – Gwamna Lawal 

September 9, 2025
An Kai Jirgin Ceto Na Farko Na Kasar Sin Yankin Tsakiyar Kasar

An Kai Jirgin Ceto Na Farko Na Kasar Sin Yankin Tsakiyar Kasar

September 9, 2025
Sin Ta Samu Karuwar Kaso 9.9 Na Sabbin Kamfanoni Masu Jarin Waje A Bara

Sin Ta Samu Karuwar Kaso 9.9 Na Sabbin Kamfanoni Masu Jarin Waje A Bara

September 9, 2025
Nijeriya Ta Rasa Tikitin Kai Tsaye Na Zuwa Gasar Kofin Duniya 

Nijeriya Ta Rasa Tikitin Kai Tsaye Na Zuwa Gasar Kofin Duniya 

September 9, 2025
Nazarin CGTN: Cin Gajiyar Damarmaki Tare Da Samun Sakamakon Moriyar Juna Ta Hanyar Yin Komai A Bude

Nazarin CGTN: Cin Gajiyar Damarmaki Tare Da Samun Sakamakon Moriyar Juna Ta Hanyar Yin Komai A Bude

September 9, 2025
Kasar Sin Ta Samar Da Kaso 30 Na Jimillar Kason Ci Gaban Masana’antun Duniya A Tsakanin 2021 Zuwa 2025

Kasar Sin Ta Samar Da Kaso 30 Na Jimillar Kason Ci Gaban Masana’antun Duniya A Tsakanin 2021 Zuwa 2025

September 9, 2025
Rundunar ‘Yansanda Ta Kama Mutum 9 Da Harsasai 4,264 Da Muggan Makamai A Nasarawa 

Rundunar ‘Yansanda Ta Kama Mutum 9 Da Harsasai 4,264 Da Muggan Makamai A Nasarawa 

September 9, 2025
NNPCL Ya Rage Farashin Man Fetur Zuwa ₦860 Kan Kowacce Lita – IPMAN

Babu Shirin Gaggawa Wajen Fara Aiwatar Da Harajin Kashi 5 Na Man Fetur – Minista

September 9, 2025
Xi Ya Aike Da Martanin Wasika Ga Wakilan Malamai Na Musamman Don Karfafa Musu Gwiwa

Xi Ya Aike Da Martanin Wasika Ga Wakilan Malamai Na Musamman Don Karfafa Musu Gwiwa

September 9, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.