• English
  • Business News
Tuesday, November 4, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Rashin Tsaro: Garuruwa Sama Da 30 Sun Gudanar Da Zanga-zanga A Zamfara

by Rabi'u Ali Indabawa
3 months ago
Tsaro

Tsoro ya haifar da rarrabuwar kawuna a kananan hukumomin Tureta da Dange/Shuni na Jihar Sokoto, yayin da hare-haren ‘yan bindiga ke ci gaba da addabar al’umma, lamarin da ya tilasta wa daruruwan iyalai tserewa daga gidajensu cikin halin kunci.

Tsawon watanni, mazauna yankin – musamman mata da yara – sun yi gudun hijira a cikin dare, suna neman mafaka a buɗaɗɗen wurare, dazuzzuka, da karkashin bishiyoyi, ba su iya kwana a cikin gida saboda ci gaba da barazanar tashin hankali.

  • Hukumar NABDA Ta Bukaci Musulmi Su Cire Fargabar Amfani Da Fasahar Alkinta Halittu
  • Muhimman Batutuwan Da Za Mu Yi La’akari Da Su Kafin Amincewa Da Bukatun Kirkirar Sabbin Jihohi — Majalisar Dattawa

“Ban shiga gidana ba cikin wata uku,” in ji Halima, wata uwa mai ‘ya’ya hudu daga Tureta.

“Kowane dare, muna kwana a karkashin bishiya, muna rayuwa cikin tsoro, tare da fargabar duk sautin da muka ii ‘yan fashi.”

Zanga-zanga a Zamfara

LABARAI MASU NASABA

Jami’an Tsaro Sun Kwato Wayoyi 45 Daga Hannun Wata Kungiyar Barayi

‘Yansanda Sun Kama Mutum Hudu Da Ake Zargi Da Aikata Muggan Laifuka A Yobe

A halin da ake ciki, mazauna kauyuka sama da 30 na gundumar Dan-Isa da Kagara a Karamar Hukumar Kaura-Namoda ta Jihar Zamfara sun gudanar da zanga-zangar lumana a Gusau babban birnin Jihar a ranar Alhamis.

Sun yi kira da gwamnati ta sa baki cikin gaggawa domin magance matsalar rashin tsaro da ke kara kamari a cikin al’ummominsu.

Masu zanga-zangar wadanda galibinsu mata da yara ne suka yi tattaki a kan titunan Gusau, rike da kwalaye masu dauke da saonni kamar haka: “Muna Bukatar Zaman Lafiya a Kauyukan Kaura-Namoda,” “Ya Kamata Gwamna Dauda Lawal da Matawalle Su Cece Mu,” “Ana Kashe Jama’ar Mu Kullum.

Da yake jawabi ga manema labarai a gaban gidan gwamnati da ke Gusau, daya daga cikin shugabannin al’ummar yankin, Lawal Kamilu daga Dan-Isa, ya bayyana zanga-zangar a matsayin kukan neman taimako bayan shafe shekaru ana kai hare-haren ‘yan fashi, da sace-sace da kashe-kashe.

“Mun fito ne daga kauyuka kusan 30. Mafi yawanmu a nan mata ne da kananan yara saboda yawancin mazajenmu ko dai an kashe su ko kuma ‘yan bindiga sun yi garkuwa da su,” in ji Kamilu.

 

Martanin gwamnati

martanin da ya mayar, Kanar Ahmed Usman (mai ritaya), mai bai wa gwamnan Jihar Sokoto shawara kan harkokin tsaro, ya amince da zanga-zangar amma ya ce gwamnati na daukar matakan dawo da zaman lafiya.

“Jihar tana ci gaba da gudanar da ayyuka tare da hadin gwiwar jami’an tsaro, wanda aka samu gagarumar nasara,” in ji Kanar Usman.

“Saboda irin namijin kokarin da jami’an tsaronmu na yau da kullum da masu gadin al’umma suke yi, muna hada gwiwa da shugabannin al’umma domin dawo da zaman lafiya.

ShareTweetSendShare

MASU ALAKA

Jami’an Tsaro Sun Kwato Wayoyi 45 Daga Hannun Wata Kungiyar Barayi
Kotu Da Ɗansanda

Jami’an Tsaro Sun Kwato Wayoyi 45 Daga Hannun Wata Kungiyar Barayi

October 4, 2025
‘Yansanda Sun Ceto Mutum 21 Da Aka Sace, Sun Kwato N4.8m Kuɗin Fansa
Kotu Da Ɗansanda

‘Yansanda Sun Kama Mutum Hudu Da Ake Zargi Da Aikata Muggan Laifuka A Yobe

October 4, 2025
Yaki Da Miyagun Kwayoyi: Kamfanin LEADERSHIP Da NDLEA Sun Kulla Kawance
Kotu Da Ɗansanda

NDLEA Ta Farmaki Masu Safarar Muggan Kwayoyi A Sassan Nijeriya

September 27, 2025
Next Post
An Sake Daure Dan Nijeriya Shekara Biyar A Birtaniya Kan Laifin Fyade

An Sake Daure Dan Nijeriya Shekara Biyar A Birtaniya Kan Laifin Fyade

LABARAI MASU NASABA

Jami’an Tsaro Sun Dawo Da Fasfo Ɗin Sanata Natasha Bayan Ƙwace Shi A Abuja

Natasha Ta Zargi Akpabio Da Sanya Jami’an Tsaro Su Ƙwace Mata Fasfo A Filin Jirgin Saman Abuja 

November 4, 2025
Masu Kashe Mutane A Kudu Maso Gabas Kiristoci Ne – Soludo

Masu Kashe Mutane A Kudu Maso Gabas Kiristoci Ne – Soludo

November 4, 2025
Ribadu Ya Gana Da Hafsoshin Tsaro Biyo Bayan Kalaman Trump 

Ribadu Ya Gana Da Hafsoshin Tsaro Biyo Bayan Kalaman Trump 

November 4, 2025
Sarkin Kasar Spaniya Zai Kawo Ziyara Kasar Sin

Sarkin Kasar Spaniya Zai Kawo Ziyara Kasar Sin

November 3, 2025
Sin Ta Yi Watsi Da Zargin Trump Dangane Da Gwajin Nukiliya A Asirce

Sin Ta Yi Watsi Da Zargin Trump Dangane Da Gwajin Nukiliya A Asirce

November 3, 2025
An Bude Taron Kasuwanci Na Duniya Na 18 A Macau

An Bude Taron Kasuwanci Na Duniya Na 18 A Macau

November 3, 2025
“Ƴan Adawa Sun Wuce Gona da Iri — Wike Ya Soki Masu Goyon Bayan  Trump

“Ƴan Adawa Sun Wuce Gona da Iri — Wike Ya Soki Masu Goyon Bayan  Trump

November 3, 2025
Shugabannin Wasu Kasashe Za Su Halarci Baje Kolin CIIE Karo Na Takwas A Birnin Shanghai

Shugabannin Wasu Kasashe Za Su Halarci Baje Kolin CIIE Karo Na Takwas A Birnin Shanghai

November 3, 2025
Li Qiang Zai Halarci Bikin Bude Taron CIIE Na 8 Da Sauran Ayyuka

Li Qiang Zai Halarci Bikin Bude Taron CIIE Na 8 Da Sauran Ayyuka

November 3, 2025
Likitocin Gwamnati Sun Zargi Gwamnatin Tarayya Da Yaɗa Bayanai Na Karya

Likitocin Gwamnati Sun Zargi Gwamnatin Tarayya Da Yaɗa Bayanai Na Karya

November 3, 2025

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.