• English
  • Business News
Saturday, October 4, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Rashin Tsaro: Garuruwa Sama Da 30 Sun Gudanar Da Zanga-zanga A Zamfara

by Rabi'u Ali Indabawa
2 months ago
in Kotu Da Ɗansanda
0
Rashin Tsaro: Garuruwa Sama Da 30 Sun Gudanar Da Zanga-zanga A Zamfara
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Tsoro ya haifar da rarrabuwar kawuna a kananan hukumomin Tureta da Dange/Shuni na Jihar Sokoto, yayin da hare-haren ‘yan bindiga ke ci gaba da addabar al’umma, lamarin da ya tilasta wa daruruwan iyalai tserewa daga gidajensu cikin halin kunci.

Tsawon watanni, mazauna yankin – musamman mata da yara – sun yi gudun hijira a cikin dare, suna neman mafaka a buɗaɗɗen wurare, dazuzzuka, da karkashin bishiyoyi, ba su iya kwana a cikin gida saboda ci gaba da barazanar tashin hankali.

  • Hukumar NABDA Ta Bukaci Musulmi Su Cire Fargabar Amfani Da Fasahar Alkinta Halittu
  • Muhimman Batutuwan Da Za Mu Yi La’akari Da Su Kafin Amincewa Da Bukatun Kirkirar Sabbin Jihohi — Majalisar Dattawa

“Ban shiga gidana ba cikin wata uku,” in ji Halima, wata uwa mai ‘ya’ya hudu daga Tureta.

“Kowane dare, muna kwana a karkashin bishiya, muna rayuwa cikin tsoro, tare da fargabar duk sautin da muka ii ‘yan fashi.”

Zanga-zanga a Zamfara

Labarai Masu Nasaba

Jami’an Tsaro Sun Kwato Wayoyi 45 Daga Hannun Wata Kungiyar Barayi

‘Yansanda Sun Kama Mutum Hudu Da Ake Zargi Da Aikata Muggan Laifuka A Yobe

A halin da ake ciki, mazauna kauyuka sama da 30 na gundumar Dan-Isa da Kagara a Karamar Hukumar Kaura-Namoda ta Jihar Zamfara sun gudanar da zanga-zangar lumana a Gusau babban birnin Jihar a ranar Alhamis.

Sun yi kira da gwamnati ta sa baki cikin gaggawa domin magance matsalar rashin tsaro da ke kara kamari a cikin al’ummominsu.

Masu zanga-zangar wadanda galibinsu mata da yara ne suka yi tattaki a kan titunan Gusau, rike da kwalaye masu dauke da saonni kamar haka: “Muna Bukatar Zaman Lafiya a Kauyukan Kaura-Namoda,” “Ya Kamata Gwamna Dauda Lawal da Matawalle Su Cece Mu,” “Ana Kashe Jama’ar Mu Kullum.

Da yake jawabi ga manema labarai a gaban gidan gwamnati da ke Gusau, daya daga cikin shugabannin al’ummar yankin, Lawal Kamilu daga Dan-Isa, ya bayyana zanga-zangar a matsayin kukan neman taimako bayan shafe shekaru ana kai hare-haren ‘yan fashi, da sace-sace da kashe-kashe.

“Mun fito ne daga kauyuka kusan 30. Mafi yawanmu a nan mata ne da kananan yara saboda yawancin mazajenmu ko dai an kashe su ko kuma ‘yan bindiga sun yi garkuwa da su,” in ji Kamilu.

 

Martanin gwamnati

martanin da ya mayar, Kanar Ahmed Usman (mai ritaya), mai bai wa gwamnan Jihar Sokoto shawara kan harkokin tsaro, ya amince da zanga-zangar amma ya ce gwamnati na daukar matakan dawo da zaman lafiya.

“Jihar tana ci gaba da gudanar da ayyuka tare da hadin gwiwar jami’an tsaro, wanda aka samu gagarumar nasara,” in ji Kanar Usman.

“Saboda irin namijin kokarin da jami’an tsaronmu na yau da kullum da masu gadin al’umma suke yi, muna hada gwiwa da shugabannin al’umma domin dawo da zaman lafiya.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: Tsaro
ShareTweetSendShare
Previous Post

An Kama Wakilin Jam’iyya Da Miliyan ₦29 Zai Sayi Ƙuri’a A Kaduna

Next Post

An Sake Daure Dan Nijeriya Shekara Biyar A Birtaniya Kan Laifin Fyade

Related

Jami’an Tsaro Sun Kwato Wayoyi 45 Daga Hannun Wata Kungiyar Barayi
Kotu Da Ɗansanda

Jami’an Tsaro Sun Kwato Wayoyi 45 Daga Hannun Wata Kungiyar Barayi

7 hours ago
‘Yansanda Sun Ceto Mutum 21 Da Aka Sace, Sun Kwato N4.8m Kuɗin Fansa
Kotu Da Ɗansanda

‘Yansanda Sun Kama Mutum Hudu Da Ake Zargi Da Aikata Muggan Laifuka A Yobe

8 hours ago
Yaki Da Miyagun Kwayoyi: Kamfanin LEADERSHIP Da NDLEA Sun Kulla Kawance
Kotu Da Ɗansanda

NDLEA Ta Farmaki Masu Safarar Muggan Kwayoyi A Sassan Nijeriya

1 week ago
‘Yansanda Sun Cafke Mutum Hudu Kan Satar Taransifoma A Makaranatar Kebbi
Kotu Da Ɗansanda

‘Yansanda Sun Cafke Mutum Hudu Kan Satar Taransifoma A Makaranatar Kebbi

1 week ago
Zargin Shan Guba: ’Yan Nijeriya Biyu Sun Mutu A Libya
Kotu Da Ɗansanda

Zargin Shan Guba: ’Yan Nijeriya Biyu Sun Mutu A Libya

1 month ago
‘Yansanda Sun Kama Ɗan Bindiga Da Kuɗin Fansa Naira Miliyan 5 A Delta
Kotu Da Ɗansanda

Yadda Wani Mai Unguwa Ya Yi Wa ‘Yar Shekara 12 Fyade A Gombe

1 month ago
Next Post
An Sake Daure Dan Nijeriya Shekara Biyar A Birtaniya Kan Laifin Fyade

An Sake Daure Dan Nijeriya Shekara Biyar A Birtaniya Kan Laifin Fyade

LABARAI MASU NASABA

Ƴar Wasan Gaban Nijeriya, Ifeoma Onumonu Ta Yi Ritaya

Ƴar Wasan Gaban Nijeriya, Ifeoma Onumonu Ta Yi Ritaya

October 4, 2025
Yadda Ake Lemon Tsamiya (Tamarin Juice)

Yadda Ake Lemon Tsamiya (Tamarin Juice)

October 4, 2025
Sojoji Sun Kama Ƴan Ta’adda 450, Sun Ceto Mutane 180 A Satumba — DHQ

Sojoji Sun Kama Ƴan Ta’adda 450, Sun Ceto Mutane 180 A Satumba — DHQ

October 4, 2025
Yadda Za A Magance Amosanin Baki

Yadda Za A Magance Amosanin Baki

October 4, 2025
Gwamnatin Jigawa Ta Bai Wa  Mahaddata Ƙur’ani 200 Tallafin Karatu

Gwamnatin Jigawa Ta Bai Wa  Mahaddata Ƙur’ani 200 Tallafin Karatu

October 4, 2025
Ruwan Sama Ya Lalata Gadoji Da Hanyoyi A Taraba, Kebbi Da Filato

Ruwan Sama Ya Lalata Gadoji Da Hanyoyi A Taraba, Kebbi Da Filato

October 4, 2025
Jami’ar Ibadan Ta Bude Sashen Karatu A Gida Ta Intanet

Jami’ar Ibadan Ta Bude Sashen Karatu A Gida Ta Intanet

October 4, 2025
Nijeriya A 65: ACF Da Afenifere Sun Yi Hannun Riga Kan Makomar Nijeriya

Nijeriya A 65: ACF Da Afenifere Sun Yi Hannun Riga Kan Makomar Nijeriya

October 4, 2025
Jami’an Tsaro Sun Kwato Wayoyi 45 Daga Hannun Wata Kungiyar Barayi

Jami’an Tsaro Sun Kwato Wayoyi 45 Daga Hannun Wata Kungiyar Barayi

October 4, 2025
‘Yansanda Sun Ceto Mutum 21 Da Aka Sace, Sun Kwato N4.8m Kuɗin Fansa

‘Yansanda Sun Kama Mutum Hudu Da Ake Zargi Da Aikata Muggan Laifuka A Yobe

October 4, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.