ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Thursday, November 13, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Rashin Tsaro: Sanatan APC Ya Nemi Monguno Ya Yi Murabus

by Sadiq
3 years ago
Monguno

Sanata mai wakiltar Neja ta Gabas, Sani Musa, ya ce Babagana Monguno, mai bai wa shugaban kasa shawara kan harkokin tsaro (NSA), ya yi murabus saboda tabarbarewar tsaro a kasar.

Musa ya soki hukumar NSA da cewa ba ita ce ta fara sanar da shugaban kasa Muhammadu Buhari barazanar da ‘yan ta’adda ke yi na sace shi ba.

  • ‘Yan Bindiga Na Kwararowa Jihata – Gwamnan Nasarawa
  • ‘Yan Kannywood Mu Guji Isar Da Sakon Da Bai Dace Ba -Yunusa Gaya

Sanatan yabyi magana ne a ranar Lahadi a wata hira da ya yi da gidan talabijin na Channels.

ADVERTISEMENT

A karshen makon da ya gabata ne wani faifan bidiyo da ‘yan ta’adda suka saki, suka yi barazanar sace Buhari da gwamnan jihar Kaduna, Nasir el-Rufai, ya karade shafukan sada zumunta.

Da yake magana kan lamarin a ranar Laraba, El-Rufai ya ce shugaba Buhari bai san da barazanar sai da ya sanar da shi da kansa.

LABARAI MASU NASABA

Babu Wani Abu Kuskure Ga Sojan Da Ya Yi Sa-in-sa Da Ministan FCT – Matawalle

Majalisar Tarayya Za Ta Binciki Masaƙa Ta Kaduna Da Sauran Gine-ginen Gwamnati 11,000 Da Aka Yi Watsi Da Su

Musa, wani jigo a jam’iyyar APC, ya ce “bisa dukkan alamu” cewa shugaban kasa ba shi da masaniyar lamarin.

“Idan har gaskiya ne, idan aka yi la’akari da maganar gwamna El-Rufai na cewa shugaban kasa bai sani ba, wannan lamari kadai ya isa a kori NSA.

“Ana kashe mutane a kasa, kuma za ka gaya min cewa a matsayina na shugaban kasa don tsara yadda ya kamata tsaronmu ya kasance, ba ka da masaniya kan haka kuma ba za a iya sanar da shugaban kasa ba. Ya kamata a sallami NSA.”

Da yake karin haske kan matsalar rashin tsaro, Sanatan Neja, ya ce da ya yi murabus idan shi ne NSA na shugaban kasa, inda ya kara da cewa jami’an tsaro a ko da yaushe sun kasa yin aiki da rahotannin sirri.

“Dole ne mu kira. Da ni ne mai ba kasa shawara kan harkokin tsaro a kasar nan da zan mika takardar murabus dina saboda na gaza. Ba ku jira sai lokacin da aka kawo muku hari sannan za ku yi aiki ba.

“Wadannan bayanan sirrin da ake rabawa bayanai ne da aka ba ku a wani mataki da masu laifin ba su cumma manufarsu da shirinsu ba kuma za ku kawar da su.

“Don haka a gare ni, na yi imani cewa muna bukatar mu sake tsara dabarunmu duba da yawan al’umma. Idan ka je jihar Neja, yau za ka ga ‘yan gudun hijira da dama, mutane sun bar garuruwansu.”

A baya-bayan nan ne mai bai wa shugaban kasa kan sha’anin tsaro, ya ce ‘yan Nijeriya sun gaji da matsalar tsaro a kasar, inda ta kara da cewa ‘yan kasar na kokarin neman taimakon kai.

ShareTweetSendShare

MASU ALAKA

Babu Wani Abu Kuskure Ga Sojan Da Ya Yi Sa-in-sa Da Ministan FCT – Matawalle
Labarai

Babu Wani Abu Kuskure Ga Sojan Da Ya Yi Sa-in-sa Da Ministan FCT – Matawalle

November 13, 2025
Majalisar Tarayya Za Ta Binciki Masaƙa Ta Kaduna Da Sauran Gine-ginen Gwamnati 11,000 Da Aka Yi Watsi Da Su
Manyan Labarai

Majalisar Tarayya Za Ta Binciki Masaƙa Ta Kaduna Da Sauran Gine-ginen Gwamnati 11,000 Da Aka Yi Watsi Da Su

November 13, 2025
Lambar Yabo Da LEADERSHIP Ta Ba Mu, Ta Ƙara Zaburar Da Mu – Gwamna Sule
Manyan Labarai

Lambar Yabo Da LEADERSHIP Ta Ba Mu, Ta Ƙara Zaburar Da Mu – Gwamna Sule

November 13, 2025
Next Post
DSS Ta Kama Kwamandan Boko Haram a Ogun

DSS Ta Kama Kwamandan Boko Haram a Ogun

LABARAI MASU NASABA

Sau Ɗaya Na Taɓa Da-nasanin Fitowa A Cikin Fim – Tanimu Akawu

Sau Ɗaya Na Taɓa Da-nasanin Fitowa A Cikin Fim – Tanimu Akawu

November 13, 2025
Nijeriya Za Ta Buga Gasar Kofin Duniya Na Shekarar 2026 – Gusau

Nijeriya Za Ta Buga Gasar Kofin Duniya Na Shekarar 2026 – Gusau

November 13, 2025
‘Yan Wasan Ƙwallon Ƙafa 10 Da Za Su Iya Buga Gasar Cin Kofin Duniya Ta Ƙarshe A 2026

‘Yan Wasan Ƙwallon Ƙafa 10 Da Za Su Iya Buga Gasar Cin Kofin Duniya Ta Ƙarshe A 2026

November 13, 2025
Babu Wani Abu Kuskure Ga Sojan Da Ya Yi Sa-in-sa Da Ministan FCT – Matawalle

Babu Wani Abu Kuskure Ga Sojan Da Ya Yi Sa-in-sa Da Ministan FCT – Matawalle

November 13, 2025
Majalisar Tarayya Za Ta Binciki Masaƙa Ta Kaduna Da Sauran Gine-ginen Gwamnati 11,000 Da Aka Yi Watsi Da Su

Majalisar Tarayya Za Ta Binciki Masaƙa Ta Kaduna Da Sauran Gine-ginen Gwamnati 11,000 Da Aka Yi Watsi Da Su

November 13, 2025
Lambar Yabo Da LEADERSHIP Ta Ba Mu, Ta Ƙara Zaburar Da Mu – Gwamna Sule

Lambar Yabo Da LEADERSHIP Ta Ba Mu, Ta Ƙara Zaburar Da Mu – Gwamna Sule

November 13, 2025
Zaɓen 2027: Jam’iyyar ADC ta Ƙaddamar Da Kwamitin Sake Fasalinta A Kaduna

Zaɓen 2027: Jam’iyyar ADC ta Ƙaddamar Da Kwamitin Sake Fasalinta A Kaduna

November 12, 2025
Sin Ta Bukaci Japan Ta Daina Yi Wa Masu Fafutukar “‘Yancin Kan Taiwan” Ingiza Mai Kantu Ruwa

Sin Ta Bukaci Japan Ta Daina Yi Wa Masu Fafutukar “‘Yancin Kan Taiwan” Ingiza Mai Kantu Ruwa

November 12, 2025
Gwamnati Ta Janye Buƙatar Amfani Da Harshen Gida Wurin Koyarwa A Makarantu 

Gwamnati Ta Janye Buƙatar Amfani Da Harshen Gida Wurin Koyarwa A Makarantu 

November 12, 2025
Peng Liyuan Da Sarauniya Letizia Ta Spain Sun Ziyarci Cibiyar Kula Da Nakasassu A Beijing

Peng Liyuan Da Sarauniya Letizia Ta Spain Sun Ziyarci Cibiyar Kula Da Nakasassu A Beijing

November 12, 2025

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.