• English
  • Business News
Wednesday, September 17, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Rawar Da Masu Sa Ido Ke Takawa Wajen Magudin Zabe A Nijeriya

by Yusuf Shuaibu
12 months ago
in Tambarin Dimokuradiyya
0
Rawar Da Masu Sa Ido Ke Takawa Wajen Magudin Zabe A Nijeriya
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Ana nuna damuwa kan sahihancin rahotannin kungiyoyin masu sa ido kan zabe, saboda mafi yawancinsu suna nuna son ransu wajen bayar da rahotanni, yayin da wasu kuma ake ke hada kai da su wajen tafka magudin zabe ko su yi biyayya ga iyayen gidansu ko kuma wadanda suke ra’ayinsu.

Zabuka a Nijeriya na cike da masu sa ido da kungiyoyi daban-daban ke turawa. Domin sa ido a babban zaben 2023, an tura masu sa ido na cikin gida da na kasashen waje 146,913. Sannan kimanin 1,000 daga cikinsu ake sa ran za su saka ido zaben gwamnan Jihar Edo.

  • Dakta Gadan-ƙaya Ya Bada Haƙuri Kan Zargin Auren Jinsi Da Ya Yi A Bauchi
  • Yawan Mutanen Da Suka Shiga Da Fita Daga Kasar Sin A Hutun Bikin Tsakiyar Kaka Ya Zarce Miliyan 5.25

Yayin da akasarin kungiyoyin masu sa ido ba sa gabatar da rahotanni a karshen zabukan, kamar yadda shugaban hukumar zabe mai zaman kanta ta kasa (INEC), Farfesa Mahmood Yakubu ya bayyana cewa wasu da suka mika rahoton ana tambayar su kan sahihincin rahotannin.

Yayin da yake jawabi ga kungiyoyin farar hula, Yakubu ya ce, “Da yawa daga cikinku da suka gabatar da rahotonsu, har yanzu wasu masu sa ido da aka amince da su ba su yi haka ba a zabukan da ya gabata da zabukan cike gibi da kuma zaben fitar da gwani.

“Don haka zan iya yin amfani da wannan damar don tunatar da wadanda har yanzu ba su gabatar da rahoton bincikensu ba cewa ya zama dole su bayar idan suna so a kara ba su damar sa ido a zaben da za a yi nan gaba.”

Labarai Masu Nasaba

Rudani Ya Kunno Kai Yayin Da INEC Ta Ki Amincewa Da Shugabancin ADC

‘Yan Nijeriya Suna Shan Wahala A Lokacin Da Gwamnatin Tinubu Ta Fi Damuwa Da Aljihunta – Sule Lamido

Da yake zantawa da LEADERSHIP, ko’odinetan gidauniyar samar da ci gaba mai dorewa, Jude Uzoma, ya yarda cewa rahotannin da wasu kungiyoyin sa ido kan zabuka na hada kai da ‘yan siyasa wajen bayar da rahotonnin da ba su dace ba.

Uzoma ya ce, kamar yadda cin hanci da rashawa ya mamaye dukkan bangarori na rayuwar al’ummar Nijeriya, haka ma yake tasiri wajen sa ido a harkokin zabe.

“Kamar yadda mutane ke cewa, cin hanci da rashawa yana dukkanin bangarorin rayuwarmu, tun daga addini, tattalin arziki, siyasa, kasuwanci da duk wani abu.

“Babu wanda ya kubuta daga cin hanci da rashawa, ciki har da kungiyoyin farar hula da ke aiki da hukumar zabe mai zaman kanta ta kasa (INEC) a matsayin masu sa ido na kasashen waje ko kuma masu sa ido na cikin gida. Wasu kungiyoyin sa ido suna goyi bayan jam’iyyar PDP, yayin da wasu ke goyon bayan APC a lokacin zabe,” in ji shi.

Masana sun tabbatar da cewa masu saka ido a zabe suna da matukar tasiri wajen gudanar da sahihin zabe a Nijeriya, wanda suke bayar da rahotanni inda aka yi dai-dai da inda ba a yi ba.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: DamuwaEdoSanya IdoZabe
ShareTweetSendShare
Previous Post

2027: Majar Atiku Da Obi Da Kwankwaso Ta Fada Shakku

Next Post

Sin Ta Yi Kira Ga Isra’ila Da Ta Dakatar Da Danyen Aikin Dake Barazanar Jefa Yankin Cikin Wani Bala’i

Related

Fursunoni Ba Za Su Samu Damar Kada Kuri’a Ba A Zaben 2023 – INEC
Tambarin Dimokuradiyya

Rudani Ya Kunno Kai Yayin Da INEC Ta Ki Amincewa Da Shugabancin ADC

2 weeks ago
‘Yan Nijeriya Suna Shan Wahala A Lokacin Da Gwamnatin Tinubu Ta Fi Damuwa Da Aljihunta – Sule Lamido
Tambarin Dimokuradiyya

‘Yan Nijeriya Suna Shan Wahala A Lokacin Da Gwamnatin Tinubu Ta Fi Damuwa Da Aljihunta – Sule Lamido

2 weeks ago
Daraktoci Da Jami’an FCT 7 Na Fuskantar Tuhume-tuhume Kan Badakar Fili
Tambarin Dimokuradiyya

2027: Idan Kana Son Tarwatsa PDP, To Ka Dawo Da Peter Obi – Wike

2 weeks ago
ADC Ta Bukaci Tinubu Ya Kafa Dokar Ta Baci A Katsina Da Zamfara Kan Rashin Tsaro
Tambarin Dimokuradiyya

ADC Ta Bukaci Tinubu Ya Kafa Dokar Ta Baci A Katsina Da Zamfara Kan Rashin Tsaro

3 weeks ago
katin zabe
Tambarin Dimokuradiyya

INEC Ta Bayyana Damuwarta Kan Katunan Zabe 360,000 Da Ba A Karba Ba A Kano

3 weeks ago
Jam’iyyar PDP Ta Janye Daga Shiga Zaɓen Ƙananan Hukumomi A Kebbi
Tambarin Dimokuradiyya

Shugabannin PDP Sun Shiga Dimuwa Yayin Da APC Ke Zawarcin Wasu Gwamnoninsu

3 weeks ago
Next Post
Sin Ta Yi Kira Ga Isra’ila Da Ta Dakatar Da Danyen Aikin Dake Barazanar Jefa Yankin Cikin Wani Bala’i

Sin Ta Yi Kira Ga Isra’ila Da Ta Dakatar Da Danyen Aikin Dake Barazanar Jefa Yankin Cikin Wani Bala’i

LABARAI MASU NASABA

Saudiyya Ta Saki ‘Yan Nijeriya 3 Da Ta Kama Bisa Kuskuren Safarar Ƙwayoyi

Saudiyya Ta Saki ‘Yan Nijeriya 3 Da Ta Kama Bisa Kuskuren Safarar Ƙwayoyi

September 17, 2025
Babban Jirgin Ruwan Kasar Sin Ya Nufi Yankin Tekun Kudancin Kasar Domin Gwaji Da Samar Da Horo

Babban Jirgin Ruwan Kasar Sin Ya Nufi Yankin Tekun Kudancin Kasar Domin Gwaji Da Samar Da Horo

September 16, 2025
Shawarwarin Sin: Ingantattun Hanyoyi Masu Sauki Na Warware Sabani

Shawarwarin Sin: Ingantattun Hanyoyi Masu Sauki Na Warware Sabani

September 16, 2025
Sauye-sauyen Manufofin Gwamnati Na Iya Hana Masu HND Zuwa NYSC

An Yi Garkuwa Da Wani Mai Hidimar Ƙasa Da Ɗalibi A Jos

September 16, 2025
Sin Da Amurka Sun Yi Tattaunawar Keke-da-keke Kan Batutuwan Cinikayya Da Manhajar TikTok

Sin Da Amurka Sun Yi Tattaunawar Keke-da-keke Kan Batutuwan Cinikayya Da Manhajar TikTok

September 16, 2025
Da Ɗumi-ɗumi: Tinubu Ya Dawo Abuja Bayan Hutun Sati 2 A Ƙasar Faransa

Da Ɗumi-ɗumi: Tinubu Ya Dawo Abuja Bayan Hutun Sati 2 A Ƙasar Faransa

September 16, 2025
Sin Da Ghana Na Fadada Hadin Gwiwa A Bangaren Ciniki Da Zuba Jari

Sin Da Ghana Na Fadada Hadin Gwiwa A Bangaren Ciniki Da Zuba Jari

September 16, 2025
Sojoji

Sojoji Sun Harbe Wasu ‘Yan Ta’adda 2 A Taraba

September 16, 2025
Yawan Hatsin Da Aka Girbe A Kasar Sin Tsakanin Shekarar 2021-2025 Ya Kai Wani Sabon Matsayi

Yawan Hatsin Da Aka Girbe A Kasar Sin Tsakanin Shekarar 2021-2025 Ya Kai Wani Sabon Matsayi

September 16, 2025
Buhari Ya Taya Amusan Murnar Lashe Zinari A Gasar Tsere Ta Duniya

Tinubu Ya Taya Amusan Da Gumel Murnar Samun Nasarori A Ɓangarori Daban-daban

September 16, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.