• English
  • Business News
Monday, November 3, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Rawar Da Masu Sa Ido Ke Takawa Wajen Magudin Zabe A Nijeriya

by Yusuf Shuaibu
1 year ago
Rawar

Ana nuna damuwa kan sahihancin rahotannin kungiyoyin masu sa ido kan zabe, saboda mafi yawancinsu suna nuna son ransu wajen bayar da rahotanni, yayin da wasu kuma ake ke hada kai da su wajen tafka magudin zabe ko su yi biyayya ga iyayen gidansu ko kuma wadanda suke ra’ayinsu.

Zabuka a Nijeriya na cike da masu sa ido da kungiyoyi daban-daban ke turawa. Domin sa ido a babban zaben 2023, an tura masu sa ido na cikin gida da na kasashen waje 146,913. Sannan kimanin 1,000 daga cikinsu ake sa ran za su saka ido zaben gwamnan Jihar Edo.

  • Dakta Gadan-ƙaya Ya Bada Haƙuri Kan Zargin Auren Jinsi Da Ya Yi A Bauchi
  • Yawan Mutanen Da Suka Shiga Da Fita Daga Kasar Sin A Hutun Bikin Tsakiyar Kaka Ya Zarce Miliyan 5.25

Yayin da akasarin kungiyoyin masu sa ido ba sa gabatar da rahotanni a karshen zabukan, kamar yadda shugaban hukumar zabe mai zaman kanta ta kasa (INEC), Farfesa Mahmood Yakubu ya bayyana cewa wasu da suka mika rahoton ana tambayar su kan sahihincin rahotannin.

Yayin da yake jawabi ga kungiyoyin farar hula, Yakubu ya ce, “Da yawa daga cikinku da suka gabatar da rahotonsu, har yanzu wasu masu sa ido da aka amince da su ba su yi haka ba a zabukan da ya gabata da zabukan cike gibi da kuma zaben fitar da gwani.

“Don haka zan iya yin amfani da wannan damar don tunatar da wadanda har yanzu ba su gabatar da rahoton bincikensu ba cewa ya zama dole su bayar idan suna so a kara ba su damar sa ido a zaben da za a yi nan gaba.”

LABARAI MASU NASABA

Manyan Kalubalen Da Sabon Shugaban INEC Zai Fuskanta

2027: Peter Obi Ya Shiga Rudani Kan Jam’iyyar Da Zai Tsaya Takara

Da yake zantawa da LEADERSHIP, ko’odinetan gidauniyar samar da ci gaba mai dorewa, Jude Uzoma, ya yarda cewa rahotannin da wasu kungiyoyin sa ido kan zabuka na hada kai da ‘yan siyasa wajen bayar da rahotonnin da ba su dace ba.

Uzoma ya ce, kamar yadda cin hanci da rashawa ya mamaye dukkan bangarori na rayuwar al’ummar Nijeriya, haka ma yake tasiri wajen sa ido a harkokin zabe.

“Kamar yadda mutane ke cewa, cin hanci da rashawa yana dukkanin bangarorin rayuwarmu, tun daga addini, tattalin arziki, siyasa, kasuwanci da duk wani abu.

“Babu wanda ya kubuta daga cin hanci da rashawa, ciki har da kungiyoyin farar hula da ke aiki da hukumar zabe mai zaman kanta ta kasa (INEC) a matsayin masu sa ido na kasashen waje ko kuma masu sa ido na cikin gida. Wasu kungiyoyin sa ido suna goyi bayan jam’iyyar PDP, yayin da wasu ke goyon bayan APC a lokacin zabe,” in ji shi.

Masana sun tabbatar da cewa masu saka ido a zabe suna da matukar tasiri wajen gudanar da sahihin zabe a Nijeriya, wanda suke bayar da rahotanni inda aka yi dai-dai da inda ba a yi ba.

ShareTweetSendShare

MASU ALAKA

Manyan Kalubalen Da Sabon Shugaban INEC Zai Fuskanta
Tambarin Dimokuradiyya

Manyan Kalubalen Da Sabon Shugaban INEC Zai Fuskanta

October 17, 2025
peter
Tambarin Dimokuradiyya

2027: Peter Obi Ya Shiga Rudani Kan Jam’iyyar Da Zai Tsaya Takara

October 17, 2025
peter
Tambarin Dimokuradiyya

Peter Obi Ya Bukaci INEC Ta Tabbatar Da Shaidar Karatun Dan Takara Kafin Shiga Zabe

October 10, 2025
Next Post
Sin Ta Yi Kira Ga Isra’ila Da Ta Dakatar Da Danyen Aikin Dake Barazanar Jefa Yankin Cikin Wani Bala’i

Sin Ta Yi Kira Ga Isra’ila Da Ta Dakatar Da Danyen Aikin Dake Barazanar Jefa Yankin Cikin Wani Bala’i

LABARAI MASU NASABA

Sojoji Sun Kashe Ƴan Bindiga 19, Sun Ƙwato Makamai A Kano

Sojoji Sun Kashe Ƴan Bindiga 19, Sun Ƙwato Makamai A Kano

November 3, 2025
Zamfara Ta Tashi Daga Matsayi Na 36 Zuwa Na 17 A Shekara Biyu Ƙarƙashin Gwamna Lawal — Rahoton BudgIT

Zamfara Ta Tashi Daga Matsayi Na 36 Zuwa Na 17 A Shekara Biyu Ƙarƙashin Gwamna Lawal — Rahoton BudgIT

November 3, 2025
Sabon Muƙaddashin Shugaban PDP Ya Sha Alwashin Maido Da Martabar Jam’iyyar Kafin 2027

Sabon Muƙaddashin Shugaban PDP Ya Sha Alwashin Maido Da Martabar Jam’iyyar Kafin 2027

November 3, 2025
2023: Gwarazan Jam’iyyu A Karon Battar Zaben Shugaban Kasa

Mayar Da Martani Kan Barazanar Amurka Ga Nijeriya: Fadar Shugaban Ƙasa Ta Yaba Wa Kwankwaso 

November 3, 2025
Likitoci

NARD Ta Yi Fatali Da Iƙirarin Gwamnatin Tarayya Na Ba Ta ₦43bn, Kuma Yajin Aiki Na Nan

November 3, 2025
Kano

Kano Ta Amince Da Naira Biliyan 8.2 Don Ayyukan ilimi, Samar Da Ruwa, Da Makamashi

November 3, 2025
Kwankwaso Ya Gargaɗi Trump Kan Barazana Ga Nijeriya

Kwankwaso Ya Gargaɗi Trump Kan Barazana Ga Nijeriya

November 2, 2025
Gumi Ya Nemi Nijeriya Ta Katse Hulɗa Da Amurka Idan Trump Bai Janye Barazanar Sa Ba

Gumi Ya Nemi Nijeriya Ta Katse Hulɗa Da Amurka Idan Trump Bai Janye Barazanar Sa Ba

November 2, 2025
Shugaba Xi Ya Mika Sakon Taya Murnar Bude Babban Gidan Tarihi Na Kasar Masar

Shugaba Xi Ya Mika Sakon Taya Murnar Bude Babban Gidan Tarihi Na Kasar Masar

November 2, 2025
Ƙasashen Da Ba Su Yanke Hukuncin Kisa A Duniya Ba

Ƙasashen Da Ba Su Yanke Hukuncin Kisa A Duniya Ba

November 2, 2025

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.