• English
  • Business News
Thursday, May 15, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Rayuwar Aure Makaranta Ce Mai Zaman Kanta…

by Rabi'at Sidi Bala
2 years ago
in Taskira
0
Rayuwar Aure Makaranta Ce Mai Zaman Kanta…
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Daukar juna ba a bakin komai ba: Da yawan ma’aurata ganin an kwana biyu tare, an saba da juna sai ya zama kar ta san kar ne, su kan manta da abubuwan da kan kara ma zamantakewarsu armashi.

Zai zamo mace duk abin da mijinta zai yi ba za ta ga bajintar shi ba, tana ganin ai dolen shi ne, dan haka ba ta ga abin yabawa ba.

  • Gwamnatin Abba Kabir Za Ta Inganta Tsarin Makarantun Tsangayu A Kano – Falaki
  • Tattalin Arzikin Sin Zai Ci Gaba Da Zama Injin Farfadowar Tattalin Arzikin Duniya

Haka ta bangaren maza ma, babu wannan yabawar tsakaninsu da matansu. Yana da kyau komin kankantar abu da miji ko mata ta/ya yi, a yaba a kuma gode. Hakan zai kara karfafa wa mutum. Idan girki ta yi, kamata ya yi ka gode ma ta tare da kuranta abincinta, haka bangaren kwalliya ma.

Shi ya sa wasu matan da sun yi aure, duk wata kwalliya sai su zubar, saboda mazajensu ba sa yabawa. Haka ta bangaren hidimar gida, ya kamata mata su rika yabawa mazajensu duk da cewa hakkinsu ne su dauki nauyin iyalansu, amma yana da kyau a gode mu su. Hakan zai kara mu su kwarin gwiwa.

-Dogon buri: Da yawan maza da mata kan shiga gidajen aurensu da dogon buri, suna tunanin babu komai a cikin rayuwar aure face jin dadi. Sun dauka irin rayuwar fina-finai ce da abubuwa na jin dadi da suke gani. Sai dai kash, rayuwa ce mai tattare da kalubale, wata rana zuma wata rana madaci. Dogon burin da ake shiga da shi na daga cikin manyan kura-kurai da ma’aurata ke tafkawa. Sai bayan an shiga a ga akasin abin da ake tsammani, wanda wasu idan an yi sa’a su kan yi hakuri da abin da suka iske, wasu kuwa a lokacin ne fitintinu za su yi ta bullowa.

Labarai Masu Nasaba

Shirye-shiryen Bukukuwan karamar Sallah

Muhimmancin Karfafa Iyali Wajen Sadaka A Watan Ramadan

Ya zama wajibi ga ma’aurata su cire dogon buri a rayuwar aurensu, su rungumi abin da suka tarar da hannu biyu da yakinin cewa canji na faruwa ne daga kan mutum. Kasancewar aboki ko abokiyar rayuwar da wani nakasu a rayuwa ba shi ke nuna cewa rayuwar zamantakewa ta ruguje ba. Kowane Dan’adam tara yake bai cika goma ba. Haka kowane rayuwar aure bai cika dari bisa dari ba, dole a samu tawaya ta wani bangaren.

-Rashin hakuri: Gaba daya rayuwar aure ‘yar hakuri ce, sannan hakuri shi ne ribar zaman duniya. Muna cikin wani zamani da ma’aurata kamar jiran juna suke, kowane a wuya yake dan uwarsa ya yi abu ya zama abin fada da cece-kuce. Kowane ma’aurata suna samun sabani a tsakanin junansu. Wasu kan yi kokari wajen ganin sun gano bakin zare ta hanyar warware matsalolinsu ta hanyar lumana. Wasu kuwa a lokacin ne zage-zage, buge-buge da bakaken maganganu ke kunno kai. Daga nan sai wutar ta kara ruruwa, har ta kai ga abin da ba a so. Wasu ma’auratan koda sune da laifi ya kan zama abu mai matukar wahala su bude baki su bada hakuri. Daga nan sai gardama ta biyo baya. Ko dan zaman lafiya bada hakuri na kashe wutar fitina.

Daga karshe, za mu iya cewa wadannan suna daga cikin manyan kura-kurai da ma’aurata ke yi. Ba kuma suke nan ba. Idan akwai wasu da kuke ganin ya dace su shiga wannan lisaafi, to sai ku saka su.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: AureDarasiMakarantaRayuwaTsokaci
ShareTweetSendShare
Previous Post

An Bude Bikin Fina-Finai Na Kasa Da Kasa A Shanghai

Next Post

ANA Ta Bukaci Hadin Kan Kasa A Batun Shugabancin Majalisa Ta 10

Related

‘Yansanda Sun Hana Hawan Sallah A Kano Saboda Tsaro
Taskira

Shirye-shiryen Bukukuwan karamar Sallah

2 months ago
Muhimmancin Karfafa Iyali Wajen Sadaka A Watan Ramadan
Taskira

Muhimmancin Karfafa Iyali Wajen Sadaka A Watan Ramadan

2 months ago
Me Ke Kawo Saurin Talaucewa Bayan Kammala Aikin Gwamnati?
Taskira

Me Ke Kawo Saurin Talaucewa Bayan Kammala Aikin Gwamnati?

3 months ago
Maganin Zubewar Mama Da Yadda Ake Gyara Shi 
Taskira

Yadda Mata Ke Daukar Yara Don Taya Su Aikin Gida

5 months ago
Yawaitar Ambaliyar Ruwa: Ina Mafita?
Taskira

Yawaitar Ambaliyar Ruwa: Ina Mafita?

8 months ago
Me Ya Fi Ci Wa Samari Da ‘Yan Mata Tuwo A Kwarya Game Da ‘Ramadan Basket’?
Taskira

Me Ya Fi Ci Wa Samari Da ‘Yan Mata Tuwo A Kwarya Game Da ‘Ramadan Basket’?

1 year ago
Next Post
ANA Ta Bukaci Hadin Kan Kasa A Batun Shugabancin Majalisa Ta 10

ANA Ta Bukaci Hadin Kan Kasa A Batun Shugabancin Majalisa Ta 10

LABARAI MASU NASABA

UTME

ASUU Ta Yi Barazanar Maka JAMB A Kotu Biyo Bayan Samun Mummunan Sakamako A UTME

May 14, 2025
Xi Jinping Ya Gana Da Takwarorinsa Na Kasashen Colombia Da Chile

Xi Jinping Ya Gana Da Takwarorinsa Na Kasashen Colombia Da Chile

May 14, 2025
Gwamnatin Tarayya Da Majalisar Dokoki Za Su Haɗa  Gwiwa Kan Sake Duba Dokar Laifukan Intanet — Minista

Gwamnatin Tarayya Da Majalisar Dokoki Za Su Haɗa  Gwiwa Kan Sake Duba Dokar Laifukan Intanet — Minista

May 14, 2025
Yadda Kasar Sin Ke Kokarin Gina Tashar Bincike A Sama Da Tubalin Kasar Duniyar Wata

Yadda Kasar Sin Ke Kokarin Gina Tashar Bincike A Sama Da Tubalin Kasar Duniyar Wata

May 14, 2025
gaza

Kasafin Kudi Na Naira Tiriliyan 1.78 Na Abuja Ya Tsallake Karatu Na Biyu A Majalisa

May 14, 2025
Kasar Sin Za Ta Inganta Cikakken Tsarin Fitar Da Ma’adanai Zuwa Ketare Don Kiyaye Tsaron Kasa

Kasar Sin Za Ta Inganta Cikakken Tsarin Fitar Da Ma’adanai Zuwa Ketare Don Kiyaye Tsaron Kasa

May 14, 2025
Tinubu Ya Yaba Wa Sule Lamiɗo A Taron Ƙaddamar Da Littafin Tarihin Rayuwasa

Tinubu Ya Yaba Wa Sule Lamiɗo A Taron Ƙaddamar Da Littafin Tarihin Rayuwasa

May 14, 2025
Manyan Ayyuka Guda Biyar Za Su Raya Makomar Al’ummomin Kasar Sin Da kasashen Latin Amurka Da Caribbean Ta Bai Daya

Manyan Ayyuka Guda Biyar Za Su Raya Makomar Al’ummomin Kasar Sin Da kasashen Latin Amurka Da Caribbean Ta Bai Daya

May 14, 2025
Yadda Aka Gina Ofishin ‘Yansanda Na Zamani A Abuja

Yadda Aka Gina Ofishin ‘Yansanda Na Zamani A Abuja

May 14, 2025
JAMB Ta Amince Da Maki 140 Da 100 Mafi Karancin Maki Na Shiga Manyan Makarantu

JAMB: Tangarɗar Na’ura Ne Ya Haifar Da Gagarumar Koma Baya A Sakamakon UTME Na 2025

May 14, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.