ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Thursday, June 4, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Yadda Abokai Da Ƙawaye Ke Tasiri Wajen Canza Halayen Mutane

by Rabi'at Sidi Bala and Sulaiman
6 months ago
Halaye

Shafin TASKIRA shafi ne daya saba zakulo muku batutuwa daban-daban wadanda suka shafi al’umma, ciki sun hadar da zamantakewar aure, rayuwar yau da kullum, rayuwar matasa, soyayya, da dai sauransu. Tsokacinmu na yau zai yi duba ne game da yadda wasu mutanen suke canjawa daga mutanen kirki, masu hakuri da tausayawa, zuwa akasin hakan. Wasu mutanen suna da kirki sosai, da kyawun hali, daga bisani kuma sai a ci karo da su a wasu wuraren tamkar ba su ba, kyawun halinsu da tausayawarsu ya zama tarihi. Musamman idan rayuwarsu ta kara canjawa daga matakin farko zuwa mataki na gaba. Misali; a makarantu, Asibitoci, Kamfanoni da dai sauransu. Wasu na kallon hakan da cewa kawaye ko abokai ne suke canja su, yayin da wasu kuma ke kallon hakan da cewa, daman can halinsu ne hakan waje ne kawai basu samu ba, domin wani baya iya canja wani. Dalilin hakan ya sa shafin TASKIRA jin ta bakin wasu daga cikin mabiya shafin game da wannan batu; “Ko mene ne gaskiyar al’amarin, shin wani ba ya iya canja wani?”

 

Ga dai bayanan nasu kamar haka;

ADVERTISEMENT

Sunana Hafsat Sa’eed, Jihar Neja:

Wasu suna da hakuri juya su kawai ake yi, sai a rika ganin kamar su da kansu suke yi. Musamman a tsarin shugabancin makarantu ko na asibitoci, ko kamfani da sauransu. Wasu dole ake yi musu daga wajen na samansu duk da suna da halin kirki sai a ce sai sun zama marasa kirki (masu zafi) shi ne za su iya kula da waje ko kula dana kasa da su, komai kankantar mukamin da aka basu a wajen. Wasu kuma kawayen da suka hadu da su ne suke ziga su wai kar a raina su, wasu kuma koya suke yi da zarar sun dan taka wani matsayi. Ya kamata mutane su rika aiki da hankali ba wai abin da za a dora su akai mara kyau ba, kai za ka auna da kanka ka ga ya dace ko bai dace ba.

LABARAI MASU NASABA

Sharrin Da Ke Tattare Da Jifan Iyali Da Munanan Kalamai

Ra’ayin Matasa Game Da Auren Kusa Da Na Nesa

 

Sunana Aminu Adamu, Malam Madori, A Jihar Jigawa:

Hakika hakan yana faruwa ka ga mutum ya canja lokaci daya, to amma ba kowa bane wani yake iya canja shi saboda mu’amular yau da kullum sai dai dama idan mutum ba shi da cikakkiyar tarbiyya da kuma ilimin gane abun da ya dace da kuma wanda bai dace ba. To duk mutum mai kyakkyawar dabi’a a cikin al’umma za ka gan shi mutum ne mai tarbiyya, don haka zai yi wuya wani ya canja shi cikin karamin lokaci don haka samun cikakkiyar tarbiyya ita ce hanyar samun kyakkyawar dabi’a.

 

Sunana Hassana Yahaya Iyayi, Jihar Kano:

Gaskiya halayyar jama’a tana canjawa in suka hadu da gurbatattun mutane nan da nan suke saurin dauke dabi’u marasa kyau. Wannan kuma abin dama ba dabi’ace mai kyau ba, Allah ya sa mu dace

 

Sunana Fatima Nura Kila, Jihar Jigawa:

Tabbas Hakan yana faruwa, shi ya sa akodayaushe matukar mutum zai yi abota yayi kokari ya yi da wadda ya fi shi wannnan halin na kirkin da aka san shi, zama yau da kullum shi ne kan janyowa a dauki hali irin na wadancan. Tabbas hakan yakan iya janyo matsaloli a cikin al’umma. Akodayaushe mutum ya rike akidar sa, saboda hakan shi ne ba zai sa ka zama kamar su ba, domin kuwa zama waje daya kuma yau da kullum ta ki wasa.

 

Sunana Lawan Isma’il (Lisary) Rano, A Jihar Kano:

Tabbas zama tare da wasu mutanen sukan canja musu halaye da dabi’u ba wai halinsu ne a haka ba. Misali; za a ga wata matar tana tare da mijinta babu dadin zama har ta kai ga ya auro wata wacce duniya ta yarda ta kirkice, amma idan aka yi rashin sa’a sai uwar gidan ta rinjayeta ita ma ta zama ta banza. Shawarata ita ce mu yi kokari da dadi-babu dadi mu ci gaba da nuna halayenmu na kirki wanda addinimu ya zo mana da shi da kuma wanda aka san malam bahaushe da shi. Ka da mu rika kallon banzan halin da wawayen cikinmu suke aikatawa Allah kasa mu dace amin.

 

Sunana Hassana Sulaiman, Hadejia ,A Jihar Jigawa:

Eh, gaskiyar lamarin hakan na faruwa lokaci zuwa lokaci, za mu iya cewa kasantuwar dabi’a da hali na mutum na sauyawa. Kuma hakan zamu iya cewa na haifar da rashin jituwa tare da raguwar mutanen dake tare da kai duk ta sanadiyyar sauya halin nan naka da kayi tashi guda. Hanyar da ya kamata mutane su himmatu a kanta wajan dawo da dabi’unsu na kirki wanda za ta zama abin kwatance ga sauran mutane ko da bayanan, ya zamana mutum na danne wasu dabi’un nasa a fili, musamman ma marasa kyau da kuma na fushi ga jama’ar da suke kewaye da shi.

 

Sunana Sadi Dauda Baturiya, Kirikasamma, Jihar Jigawa:

Babu shakka akwai mutane da dama da suka canza halayensu daga mai kyau zuwa maras kyau biyo bayan dalilai mabanbanta, ciki kuwa akwai tasirin abokin zama ko tarayya, batun cewa zama da madaukin kanwa ba ya kawo farin kai ba gaskiya bane, domin kuwa ita rayuwa kowa da kaddararsa, abin da ya dace da kowanne dan’Adam dai shi ne ya ji tsoron Allah a duk inda yake kamar yadda Manzon Allah sallallahu alaihi wasallam ya fada, fatanmu a kullum ya tsaremu daga mummunar kaddara, kuma ya azurtamu da kyakkyawan karshe amin.

 

Sunana Hadiza Ibrahim D. Auta, kaura-Namoda, Jihar Zamfara:

Har kullum Hausawa suna fadin sai hali ya zo daya ake yin abota. Sannan kuma ana yin kamshi idan aka kusanci mai sayar da turare. To kamar haka ne a bangaren hali ko na ce halayya. Sau da yawa mutum zai kasance da halin kirki, amma zama da wani kara-gurbi ya sa shi ma ya koyi wasu abubuwan daga cikin dabi’unsa ba tare da ma ya sani ba. Shi ya sa wasu iyaye masu hikima suke kokarin sanin wane ne abokin dansu, kuma ya ya halayensa suke, idan da matsala suna yin gaggawar yi wa abotar iyaka. Saboda tsoron kusancin nasu ya lalata musu tarbiyyar da suke kokarin ginawa, gudun suna tufka a koma yi musu warawara.

 

Sunana Mohammed Isah, Zareku Miga, A Jihar Jigawa:

Eh a zahiri ana samun irin wadannan mutane da farko ka gansu ba wata matsala, kalau dasu, amma kuma daga baya sai ka ga sun canza. To dama wadansu halinsu ne kawai guri ne basu samu ba. Amma kuma wadannan su abokaine suke canzasu. Matsolilin da hakan ke haifarwa shi ne, rashin kyauwun hali ya kan haifar da rashin tausayin na kasa da kai, taimakon juna da sauran su. Amma kuma idan mutum ya tsinci kansa a irin wannan abokan ya kamata yayi taka-tsam-tsan da kar ya koyi mummunar dabi’a.

 

Sunana Aisha T. Bello, Jihar Kaduna:

Gaskiya in ka ga kana tare da mutun lokaci daya ya canza yana da ra’ayin canza wanne, ko wasu matanen suna bari wasu su yi ‘control’ din rayuwarsu sai abun da suka ce. Shawarata ga masu irin wanan hali shi ne ka da su bawa wani dama ya canza masu rayuwa, idan ma shawara ce suke nema to su nema wajen iyayensu, in kuma ba iyaye Allah na nan shi ne gatan maraya, Allah ya sa mu dace.

Halaye
Rabi'at Sidi Bala
+ posts Bio
  • Rabi'at Sidi Bala
    https://hausa.leadership.ng/author/rabiat-sidi-bala/
    Ban Taɓa Fitowa A Fim Na Yi Da-na-sani Ba —Habibu Yaro
  • Rabi'at Sidi Bala
    https://hausa.leadership.ng/author/rabiat-sidi-bala/
    Yadda Al’umma Suka Gudanar Da Bukukuwan Sallah Duk Da Matsin Tattalin Arziki
  • Rabi'at Sidi Bala
    https://hausa.leadership.ng/author/rabiat-sidi-bala/
    GORON JUMA’A 29-05-2027
  • Rabi'at Sidi Bala
    https://hausa.leadership.ng/author/rabiat-sidi-bala/
    Yadda Za Ku Tattala Kuɗaɗen Da Ke Shigowa Hannu Domin Ci Gaban Rayuwa
Halaye
Sulaiman
+ posts Bio
  • Sulaiman
    Sarki Sanusi II Ya Tuɓe Rawanin Mai Unguwar Rikadawa Kan Badaƙalar Fili
  • Sulaiman
    Tawagar Masanan Dakile Yaduwar Cututtuka Ta Sin Ta Isa DR Congo
  • Sulaiman
    Uba Sani Ya Sanya Hannu Kan Sabbin Dokoki A Bangaren Sauya Fannin Wuta, Noma, Da Muhalli
  • Sulaiman
    Han Zheng Zai Halarci Taron SPIEF Karo Na 29 A Rasha Tare Da Gudanar Da Ziyarar Aiki A Belarus

MASU ALAKA

Halaye
Taskira

Sharrin Da Ke Tattare Da Jifan Iyali Da Munanan Kalamai

May 10, 2026
Ra’ayin Matasa Game Da Auren Kusa Da Na Nesa
Labarai

Ra’ayin Matasa Game Da Auren Kusa Da Na Nesa

April 19, 2026
Buƙatar Taka-tsan-tsan Wajen Koya Wa Yara Ƙanana Azumi
Taskira

Buƙatar Taka-tsan-tsan Wajen Koya Wa Yara Ƙanana Azumi

February 28, 2026
Next Post
Japanawa Sun Fito Kan Tituna Suna Nuna Fushi Da Katobarar Firaminista Takaichi A Kan Taiwan

Japanawa Sun Fito Kan Tituna Suna Nuna Fushi Da Katobarar Firaminista Takaichi A Kan Taiwan

LABARAI MASU NASABA

Sarki Sanusi II Ya Tuɓe Rawanin Mai Unguwar Rikadawa Kan Badaƙalar Fili

Sarki Sanusi II Ya Tuɓe Rawanin Mai Unguwar Rikadawa Kan Badaƙalar Fili

June 4, 2026
Tawagar Masanan Dakile Yaduwar Cututtuka Ta Sin Ta Isa DR Congo

Tawagar Masanan Dakile Yaduwar Cututtuka Ta Sin Ta Isa DR Congo

June 3, 2026
Uba Sani Ya Sanya Hannu Kan Sabbin Dokoki A Bangaren Sauya Fannin Wuta, Noma, Da Muhalli

Uba Sani Ya Sanya Hannu Kan Sabbin Dokoki A Bangaren Sauya Fannin Wuta, Noma, Da Muhalli

June 3, 2026
Han Zheng Zai Halarci Taron SPIEF Karo Na 29 A Rasha Tare Da Gudanar Da Ziyarar Aiki A Belarus

Han Zheng Zai Halarci Taron SPIEF Karo Na 29 A Rasha Tare Da Gudanar Da Ziyarar Aiki A Belarus

June 3, 2026
Majalisa Ta Nemi Tinubu Ya Canza Dabarun Yaƙi Da Ta’addanci Don Kawo Ƙarshen Kashe-kashe

’Yan Majalisar Tarayya 3 Sun Fice Daga APC Zuwa ADC da PRP

June 3, 2026
An Fara Watsa Shirye-Shirye Masu Taken “Sha’awar Xi Jinping Ga Al’adu” Da Sauran Fina-Finan Bayyana Labaran Sin A Kasar Laos

An Fara Watsa Shirye-Shirye Masu Taken “Sha’awar Xi Jinping Ga Al’adu” Da Sauran Fina-Finan Bayyana Labaran Sin A Kasar Laos

June 3, 2026
Tambuwal Ya Jajanta Wa Waɗanda Harin ’Yan Bindiga Ya Shafa A Sokoto, Ya Nemi A Ƙara Tsaro

Tambuwal Ya Jajanta Wa Waɗanda Harin ’Yan Bindiga Ya Shafa A Sokoto, Ya Nemi A Ƙara Tsaro

June 3, 2026
Gwamnatin Beijing Ta Amince Da Kafa Cibiyar Kirkire-Kirkiren Fasahar Lissafi Mai Nasaba Da Sararin Samaniya

Gwamnatin Beijing Ta Amince Da Kafa Cibiyar Kirkire-Kirkiren Fasahar Lissafi Mai Nasaba Da Sararin Samaniya

June 3, 2026
Za A Fara Buga Gasar Kofin Sarkin Gombe Bayan Masu Ruwa Da Tsaki Sun Cimma Matsaya

Za A Fara Buga Gasar Kofin Sarkin Gombe Bayan Masu Ruwa Da Tsaki Sun Cimma Matsaya

June 3, 2026
Hada Kai Da ’Yan Awaren Yankin Taiwan Ba Zai Haifar Da Ɗa Mai Ido Ba

Hada Kai Da ’Yan Awaren Yankin Taiwan Ba Zai Haifar Da Ɗa Mai Ido Ba

June 3, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.