• Leadership Hausa
Monday, December 4, 2023
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Sana’a Sa’a
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Sana’a Sa’a
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Rayuwar Aure Makaranta Ce Mai Zaman Kanta…

by Rabi'at Sidi Bala
6 months ago
in Taskira
0
Rayuwar Aure Makaranta Ce Mai Zaman Kanta…
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Daukar juna ba a bakin komai ba: Da yawan ma’aurata ganin an kwana biyu tare, an saba da juna sai ya zama kar ta san kar ne, su kan manta da abubuwan da kan kara ma zamantakewarsu armashi.

Zai zamo mace duk abin da mijinta zai yi ba za ta ga bajintar shi ba, tana ganin ai dolen shi ne, dan haka ba ta ga abin yabawa ba.

  • Gwamnatin Abba Kabir Za Ta Inganta Tsarin Makarantun Tsangayu A Kano – Falaki
  • Tattalin Arzikin Sin Zai Ci Gaba Da Zama Injin Farfadowar Tattalin Arzikin Duniya

Haka ta bangaren maza ma, babu wannan yabawar tsakaninsu da matansu. Yana da kyau komin kankantar abu da miji ko mata ta/ya yi, a yaba a kuma gode. Hakan zai kara karfafa wa mutum. Idan girki ta yi, kamata ya yi ka gode ma ta tare da kuranta abincinta, haka bangaren kwalliya ma.

Shi ya sa wasu matan da sun yi aure, duk wata kwalliya sai su zubar, saboda mazajensu ba sa yabawa. Haka ta bangaren hidimar gida, ya kamata mata su rika yabawa mazajensu duk da cewa hakkinsu ne su dauki nauyin iyalansu, amma yana da kyau a gode mu su. Hakan zai kara mu su kwarin gwiwa.

-Dogon buri: Da yawan maza da mata kan shiga gidajen aurensu da dogon buri, suna tunanin babu komai a cikin rayuwar aure face jin dadi. Sun dauka irin rayuwar fina-finai ce da abubuwa na jin dadi da suke gani. Sai dai kash, rayuwa ce mai tattare da kalubale, wata rana zuma wata rana madaci. Dogon burin da ake shiga da shi na daga cikin manyan kura-kurai da ma’aurata ke tafkawa. Sai bayan an shiga a ga akasin abin da ake tsammani, wanda wasu idan an yi sa’a su kan yi hakuri da abin da suka iske, wasu kuwa a lokacin ne fitintinu za su yi ta bullowa.

Labarai Masu Nasaba

Dabi’ar Saba Alkawarin Da Maza Ke Yi Ga Matan Da Za Su Aura

Tsokaci A Kan Yadda Wasu Mata Ke Baje Kolin Hira A Cikin Motocin Haya

Ya zama wajibi ga ma’aurata su cire dogon buri a rayuwar aurensu, su rungumi abin da suka tarar da hannu biyu da yakinin cewa canji na faruwa ne daga kan mutum. Kasancewar aboki ko abokiyar rayuwar da wani nakasu a rayuwa ba shi ke nuna cewa rayuwar zamantakewa ta ruguje ba. Kowane Dan’adam tara yake bai cika goma ba. Haka kowane rayuwar aure bai cika dari bisa dari ba, dole a samu tawaya ta wani bangaren.

-Rashin hakuri: Gaba daya rayuwar aure ‘yar hakuri ce, sannan hakuri shi ne ribar zaman duniya. Muna cikin wani zamani da ma’aurata kamar jiran juna suke, kowane a wuya yake dan uwarsa ya yi abu ya zama abin fada da cece-kuce. Kowane ma’aurata suna samun sabani a tsakanin junansu. Wasu kan yi kokari wajen ganin sun gano bakin zare ta hanyar warware matsalolinsu ta hanyar lumana. Wasu kuwa a lokacin ne zage-zage, buge-buge da bakaken maganganu ke kunno kai. Daga nan sai wutar ta kara ruruwa, har ta kai ga abin da ba a so. Wasu ma’auratan koda sune da laifi ya kan zama abu mai matukar wahala su bude baki su bada hakuri. Daga nan sai gardama ta biyo baya. Ko dan zaman lafiya bada hakuri na kashe wutar fitina.

Daga karshe, za mu iya cewa wadannan suna daga cikin manyan kura-kurai da ma’aurata ke yi. Ba kuma suke nan ba. Idan akwai wasu da kuke ganin ya dace su shiga wannan lisaafi, to sai ku saka su.

Tags: AureDarasiMakarantaRayuwaTsokaci
ShareTweetSendShare
Previous Post

An Bude Bikin Fina-Finai Na Kasa Da Kasa A Shanghai

Next Post

ANA Ta Bukaci Hadin Kan Kasa A Batun Shugabancin Majalisa Ta 10

Related

Dabi’ar Saba Alkawarin Da Maza Ke Yi Ga Matan Da Za Su Aura
Taskira

Dabi’ar Saba Alkawarin Da Maza Ke Yi Ga Matan Da Za Su Aura

1 month ago
Tsokaci A Kan Yadda Wasu Mata Ke Baje Kolin Hira A Cikin Motocin Haya
Taskira

Tsokaci A Kan Yadda Wasu Mata Ke Baje Kolin Hira A Cikin Motocin Haya

2 months ago
Abubuwan Da Ke Janyo Hankalin Namiji Ga Matarsa
Taskira

Abubuwan Da Ke Janyo Hankalin Namiji Ga Matarsa

5 months ago
Ta Ya Za A Magance Rashin Tsaftar Yara Mata Masu Tasowa?
Taskira

Ta Ya Za A Magance Rashin Tsaftar Yara Mata Masu Tasowa?

5 months ago
Rashin Kula Da Kananan Bukatun ‘Ya’ya Mata Da Halin Da Suke Shiga
Taskira

Sharhi A Kan Mata Marasa Wadatar Zuci

6 months ago
Kwaliyyar Da Samari Da ‘Yanmata Suka Tsara Don Burgewa A Wannan Sallar
Taskira

Kwaliyyar Da Samari Da ‘Yanmata Suka Tsara Don Burgewa A Wannan Sallar

8 months ago
Next Post
ANA Ta Bukaci Hadin Kan Kasa A Batun Shugabancin Majalisa Ta 10

ANA Ta Bukaci Hadin Kan Kasa A Batun Shugabancin Majalisa Ta 10

LABARAI MASU NASABA

Gwamnatin Tinubu Za Ta Sake Inganta NTA Da FRCN – Minista

Gwamnatin Tinubu Za Ta Sake Inganta NTA Da FRCN – Minista

December 4, 2023
Neman Bisa: Ofishin Jakadancin Amurka Ya Tantance ‘Yan Nijeriya Fiye Da 150,000 A 2023

Neman Bisa: Ofishin Jakadancin Amurka Ya Tantance ‘Yan Nijeriya Fiye Da 150,000 A 2023

December 4, 2023
Abin Da Ya Haddasa Gobara A Gidan Rediyo Nijeriya Kaduna – ‘Yan Kwana-kwana

Abin Da Ya Haddasa Gobara A Gidan Rediyo Nijeriya Kaduna – ‘Yan Kwana-kwana

December 4, 2023
Atiku Ya Musanta Amfana Da Maido Da Lasisin Kamfanin Intels Da Gwamnati Ta Yi

Atiku Ya Musanta Amfana Da Maido Da Lasisin Kamfanin Intels Da Gwamnati Ta Yi

December 4, 2023
Yadda Na Hana ‘Yan Boko Haram Mayar Da Jihar Neja Hedikwatarsu – Tsohon Gwamnan Jihar 

Yadda Na Hana ‘Yan Boko Haram Mayar Da Jihar Neja Hedikwatarsu – Tsohon Gwamnan Jihar 

December 4, 2023
Dan Kwallon Kano Pillars Ya Zazzaga Kwallaye Biyar A Ragar Gombe United 

Dan Kwallon Kano Pillars Ya Zazzaga Kwallaye Biyar A Ragar Gombe United 

December 3, 2023
Shahararren Masanin Kasar Sin: Rasuwar Kissinger Ta Karfafa Gwiwar Bude Sabon Babi Ga Alakar Kasa Da Kasa

Shahararren Masanin Kasar Sin: Rasuwar Kissinger Ta Karfafa Gwiwar Bude Sabon Babi Ga Alakar Kasa Da Kasa

December 3, 2023
Yadda Matakin Raya Kauyuka Da Sin Ta Dauka Ke Taimakawa Kawar Da Talauci Da Ma Yayata Aladun Kasar

Yadda Matakin Raya Kauyuka Da Sin Ta Dauka Ke Taimakawa Kawar Da Talauci Da Ma Yayata Aladun Kasar

December 3, 2023
Manchester City Ta Koma Ta Uku A Teburin Firimiya Bayan Buga Canjaras Da Tottenham

Manchester City Ta Koma Ta Uku A Teburin Firimiya Bayan Buga Canjaras Da Tottenham

December 3, 2023
Ding Xuexiang Ya Halarci Taron Koli Kan Sauyin Yanayi Tsakanin Shugabannin Kasashen G77 Da Kasar Sin

Ding Xuexiang Ya Halarci Taron Koli Kan Sauyin Yanayi Tsakanin Shugabannin Kasashen G77 Da Kasar Sin

December 3, 2023
Advertise with us

© 2022 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2022 Leadership Media Group - All Right Reserved.