ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Wednesday, September 9, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Yadda Mata Ke Daukar Yara Don Taya Su Aikin Gida

by Leadership Hausa and Sulaiman
2 years ago
Mata

A yau canjin yanayin wannan zamanin ya zo wa da mata wani sabon salo da yadda suke daukan ‘yara domin taya su aiki a gida.

Wasu su kan sakar wa mai aiki ragamar aikin gida, har ya kai ga basu koya wa ‘ya’yansu mata girki domin wasu ana yin aurensu basu iya girki ba. Ko me za ku ce akan hakan? Shafin Taskira shafi ne da ya saba zakolo muku batutuwa daban-daban wadanda suka shafi al’umma. Tsokacimmu na yau zai yi doba ne game da yadda ake samu, ana auran yara mata basu iya Girki ba:

 

ADVERTISEMENT

Usman Sani

Gaskiya wannan batu yana da muhimmanci sosai. Yanzu zamanin ya canza, kuma yawancin iyaye suna daukar ma’aikata don su taimaka a ayyukan gida. Wannan ba matsala bace idan dai iyayen suna koyar da ’ya’yansu abubuwan da suka kamata, musamman girki.

LABARAI MASU NASABA

Sharrin Da Ke Tattare Da Jifan Iyali Da Munanan Kalamai

Ra’ayin Matasa Game Da Auren Kusa Da Na Nesa

Amma idan aka bar wa mai’aikata duk aikin gida, kuma iyaye ba su ba wa ’ya’yan nasu lokaci don koya musu girki ba, lamarin zai iya zama matsala. A lokacin aure, wasu matan za su fuskanci kalubale saboda ba su da gogewa.

Ina ganin wajibi ne iyaye su rika koya wa ’ya’yansu mata abubuwan da suka dace, ko da kuwa akwai ma’aikata a gida. Wannan zai taimaka musu su zama masu cikakkiyar basira da iya kula da gida a gaba. Wannan kuma ba zai hana daukar ma’aikata ba, amma ba dole a jingina komai a kansu ba.

 

Khadija Abdullahi

To gaskiya rashin iya girki ga mace ba karamar matsala bace, saboda bai kamata ace tunda aka haifeki har kika taso koka girma ace baki iya girki ba wannan gaskiya abun kunya ne.

Ya kamata ace iyaye su dage, suyi iya kokarinsu danganin sun koyawa yaransu girki, tun yarinya na karama yakamata afara koyamata ahankali ahankali hatta girma, kafin yarinya ta girma sai ki ga ta iya aikinta. Amma da zarar annuna wa yarinya so an bar ta ba a koya mata komai ba haka za ta girma ba ta iya komai ba, kuma ta zo ta wahala daga baya tun da dole sai ta yi, ba za a tattaba ta yi aure ba, sannan ba ka san wanda za ta aura ba ya yanayin halinsa yake, wani komai halinsa ba ya son mai aiki ya fi son matarsa ta yi masa girki da kanta.

Shawara ga iyaye mata mu cire son ‘ya’yanmu, mu koya musu girki kala-kala, duk inda za su shiga ba za su ji kunya ba saboda sun san sun iya komai, amma idan basu iya ba sai ki ga su kansu suna jin kunyar shiga mutane. Ki koya wa ‘ya’yanki aiki wannan shi ne gata. Allah ya sa mu dace.

 

Fa’iza Musa

To ni a ganina gaskiya ka koyawa ‘ya’yanka mata aikin gida shi ne gata, ba wai ka bar su sakaka ba komai a ce mai aiki ce za ta yi gaskiya wannan ba daidai ba ne, ba kuma so bane, ni ina ganin ma cutarsu kake. Ya kamata iyaye su koyawa ‘ya’yansu aikin gida ba wai girki kadai ba komai na gida yadda kyau yarinya mace ta iya kome na gida.

Sakarwa mai aiki ragamar gida ba kya koyawa ‘ya’yanki aiki ba wannan gaskiya ba karamin cutar kai bane.

Wai sai ki ga sai za a yi auren yarinya sannan ne za a kai ta wajen koyon girki a biya kudi mai yawa, wai a wannan lokacin ne za ta koyi duk wani girki, ai wannan lokacin ya yi kankanta, sannan kuma ko ta ko ya iyakarta ta yi na doki, ba za ta iya dorewa ba daga baya ta watsar tun da ba ta saba ba, ba lallai ne ta iya dorewa ba, a zo kuma a shiga wani yanayi. Allah ya ganar da mu.

Mata
Leadership Hausa
Website |  + posts Bio
  • Leadership Hausa
    Karuwar Farin Jinin Gwamna Umaru Bago A Siyasar Jihar Neja
  • Leadership Hausa
    Kyakkyawan Tsarin Laken Asiri Zai Dakile Shirin Magudin Zabe A Nijeriya —Mohammed
  • Leadership Hausa
    Batun Dawo Da Tallafin Mai Da Atiku Ya Yi Na Ci Gaba Da Tayar Da Kura
  • Leadership Hausa
    Batun Guguwar Kakar Yakin Neman Zabukan 2027 A Nijeriya
Mata
Sulaiman
+ posts Bio
  • Sulaiman
    Batun AI Zai Fi Daukar Hankali A Bikin Baje Kolin Fasahar Zamani Ta Duniya Karo Na 5
  • Sulaiman
    Cinikin Wajen Sin Ya Ci Gaba Da Samun Bunkasa Cikin Sauri A Watanni Takwas Na Farkon Bana
  • Sulaiman
    ‘Yan Bindiga Sun Kashe 2, Sun Yi Garkuwa Da 26 A Kaduna
  • Sulaiman
    Binciken CGTN Ya Nuna Gamsuwa Da Yadda Baje Kolin CIFTIS Ke Shaida Karfin Gwiwar Sin A Fannin Kara Fadada Bude Kofa Bisa Babban Matsayi

MASU ALAKA

Mata
Taskira

Sharrin Da Ke Tattare Da Jifan Iyali Da Munanan Kalamai

May 10, 2026
Ra’ayin Matasa Game Da Auren Kusa Da Na Nesa
Labarai

Ra’ayin Matasa Game Da Auren Kusa Da Na Nesa

April 19, 2026
Buƙatar Taka-tsan-tsan Wajen Koya Wa Yara Ƙanana Azumi
Taskira

Buƙatar Taka-tsan-tsan Wajen Koya Wa Yara Ƙanana Azumi

February 28, 2026
Next Post
Mata

Bitar Aikin Hajjin 2024

LABARAI MASU NASABA

Batun AI Zai Fi Daukar Hankali A Bikin Baje Kolin Fasahar Zamani Ta Duniya Karo Na 5

Batun AI Zai Fi Daukar Hankali A Bikin Baje Kolin Fasahar Zamani Ta Duniya Karo Na 5

September 8, 2026
Gwamna Radda Ya Samu Goyon Bayan APC A Katsina Gabanin Zaɓen 2027

Gwamna Radda Ya Samu Goyon Bayan APC A Katsina Gabanin Zaɓen 2027

September 8, 2026
Cinikin Wajen Sin Ya Ci Gaba Da Samun Bunkasa Cikin Sauri A Watanni Takwas Na Farkon Bana

Cinikin Wajen Sin Ya Ci Gaba Da Samun Bunkasa Cikin Sauri A Watanni Takwas Na Farkon Bana

September 8, 2026
'Yan Bindiga

‘Yan Bindiga Sun Kashe 2, Sun Yi Garkuwa Da 26 A Kaduna

September 8, 2026
Binciken CGTN Ya Nuna Gamsuwa Da Yadda Baje Kolin CIFTIS Ke Shaida Karfin Gwiwar Sin A Fannin Kara Fadada Bude Kofa Bisa Babban Matsayi

Binciken CGTN Ya Nuna Gamsuwa Da Yadda Baje Kolin CIFTIS Ke Shaida Karfin Gwiwar Sin A Fannin Kara Fadada Bude Kofa Bisa Babban Matsayi

September 8, 2026
Yadda Taron Tattalin Arziki Da Zuba Jari Na Kwana Biyu Ya Gudana A Katsina

Gwamna Radda Ya Gabatar Da Kasafin N828.6bn Na 2027

September 8, 2026
Sin Za Ta Yi Aiki Tare Da Sassa Daban Daban Domin Mayar Da Fasahar AI Wata Dama Ta Cin Gajiya Mai Dorewa

Sin Za Ta Yi Aiki Tare Da Sassa Daban Daban Domin Mayar Da Fasahar AI Wata Dama Ta Cin Gajiya Mai Dorewa

September 8, 2026
Gwamnan Kebbi Ya Bayyana Shirin Sake Duba Albashin Malaman Firamare

Gwamna Idris Ya Rushe Majalisar Shugabannin Hukumar Zaɓe Ta Kebbi

September 8, 2026
Han Zheng Ya Halarci Baje Kolin CIFIT Karo Na 26 Tare Da Gabatar Da Jawabi

Han Zheng Ya Halarci Baje Kolin CIFIT Karo Na 26 Tare Da Gabatar Da Jawabi

September 8, 2026
Wani Soja Ya Kashe Kansa Bayan Kashe Matarsa A Jihar Neja

Kano Za Ta Kafa Sansanonin Sojoji A Ƙananan Hukumomin Da Ke Fuskantar Barazanar Tsaro

September 8, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.