Leadership News Hausa
No Result
View All Result
  • LABARAI
  • WASANNI
  • RAHOTANNI
  • SIYASA
  • KASUWANCI
  • ADABI
  • RA’AYINMU
  • TATTAUNAWA
  • BIDIYO
  • MAKALAR YAU
  • LABARAI
  • WASANNI
  • RAHOTANNI
  • SIYASA
  • KASUWANCI
  • ADABI
  • RA’AYINMU
  • TATTAUNAWA
  • BIDIYO
  • MAKALAR YAU
No Result
View All Result
Leadership News Hausa
No Result
View All Result

Real Madrid Za Ta Yi Zawarcin Dan Wasan Bayern Munchen Gnabry

by
3 years ago
in WASANNI
2 min read
WhatsAppShare on FacebookShare on TwitterShare on Telegram
ADVERTISEMENT

Rahotanni daga kasar Sipaniya sun bayyana cewa kungiyar kwallon kafa ta Real Madrid ta saka sunan dan wasan gaba na kungiyar kwallon kafa ta Bayern Munchen, Serge Gnabry a cikin ‘yan wasan da zata nema a kakar wasa mai zuwa kamar yadda rahotanni suka bayyana.

Dan wasan dai ya zura kwallaye hudu rigis a wasan da kungiyar kwallon kafa ta Bayern Munchen tayi fata-fata da kungiyar Tottenham har gida daci 7-2 a gasar cin kofin zakarun turai wanda hakan yasa ya zura kwallaye biyar sannan ya taimaka aka zura guda hudu cikin wasanni takwas daya buga  a wannan kakar.

Kamar yadda rahotanni suka bayyana kokarin da dan wasan yayi shine yaja hankalin shugabannin kungiyar kwallon kafa ta Real Madrid suka saka shi acikin jerin sunayen ‘yan wasan da zasu nema a karshen wannan kakar.

Labarai Masu Nasaba

Chiellini Ya Bar Juventus

Wasan Damben Cin Mota: An Fara Fafatawa A Kano

Gnabry dai tsohon dan wasan kungiyar kwallon kafa ta Arsenal ne sai dai tauraruwarsa bata haskawa ba tsawon zamansa a kungiyar wanda hakan yasa ya koma kungiyar Werder Bremen ta kasar Jamus kuma a kakar wasa ta 2016 zuwa 2017 kokarinsa yasa kungiyar Bayern Munchen taga yakamata ta daukeshi.

Har ila yau dan wasa Gnabry yana daya daga cikin manyan ‘yan wasan da tawagar ‘yan wasan kasar Jamus take ji dasu inda ya zura kwallo tara cikin wasanni goma cikin wasannin da kociyan tawagar Joachim Low ya gayyacishi.

Sai dai abune mai wahala kungiyar kwallon kafa ta Bayern Munchen ta hakura ta rabu da matashin dan wasan wanda take ganin shine zai kasance jagoran kungiyar a nan gaba saboda har yanzu shekararsa 24 a duniya.

Like this:

Like Loading...
SendShareTweetShare
Previous Post

An Ci Tarar Liverpool Kan Amfani Da Dan Wasan Da Bai Dace Ba

Next Post

Ba Zan Gayyaci Abraham Da Tamori Ba Yanzu – Kocin Super Eagles

Labarai Masu Nasaba

Chiellini

Chiellini Ya Bar Juventus

by Abba Ibrahim Wada
8 hours ago
0

...

dambe

Wasan Damben Cin Mota: An Fara Fafatawa A Kano

by Abba Ibrahim Wada
1 week ago
0

...

klopp

Har Yanzu Ban Hakura Da Lashe Firimiya Ba, Cewar Klopp

by Abba Ibrahim Wada
1 week ago
0

...

barcelona

Barcelona Ta Sa Hukumar La Liga Asarar Makudan Kudade

by Abba Ibrahim Wada
1 week ago
0

...

Next Post

Ba Zan Gayyaci Abraham Da Tamori Ba Yanzu – Kocin Super Eagles

Leave Comment

Domin bayar da talla ko neman ƙarin bayani a tuntuɓe mu a: +2348039216372

  • LABARAI
  • WASANNI
  • RAHOTANNI
  • SIYASA
  • KASUWANCI
  • ADABI
  • RA’AYINMU
  • TATTAUNAWA
  • BIDIYO
  • MAKALAR YAU
Advertise with us | English Edition | Fashion Magazine | Business News

© 2022 Leadership Media Group .

No Result
View All Result
  • LABARAI
  • WASANNI
  • RAHOTANNI
  • SIYASA
  • KASUWANCI
  • ADABI
  • RA’AYINMU
  • TATTAUNAWA
  • BIDIYO
  • MAKALAR YAU

© 2022 Leadership Media Group .

Go to mobile version
%d bloggers like this: