• English
  • Business News
Sunday, July 6, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Remi Tinubu Ta Sanya Wa Babban Dakin Taron Cibiyar Mata Ta Abuja Sunan Maryam Abacha

by Bello Hamza
2 years ago
in Labarai
0
Remi Tinubu Ta Sanya Wa Babban Dakin Taron Cibiyar Mata Ta Abuja Sunan Maryam Abacha
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Uwargidan shugaban kasa Oluremi Tinubu, ta sauya sunan babban dakin taron ‘Maryam Babangida National Centre for Women Development’ zuwa sunan Dr. Maryam Abacha, matar tsohon shugaban kasa a mulkin soja, marigayi Janaral Sani Abacha.

 

Zauren wanda a da ake kira da ‘African Peace Mission Hall’, uwargidan shugaban kasar ce ta kaddamar da shi kuma aka canza masa suna zuwa Maryam Abacha, saboda irin gudummawar da ta bayar wajen samar da zaman lafiya a nahiyar Afrika.

  • Uwargidan Shugaban kasa, Remi Tinubu Ta Ziyarci Buhari A Daura

A jawabinta, uwargidan shugaban kasa, Sanata Oluremi Tinubu, ta ce taron muhimmi ne a kokarin hadin gwiwa wajen karfafa alaka tare da bunkasa ci gaban da aka samu wajen samun hadin kai da dawwamammen dangantaka a tsakanin mata.

 

Labarai Masu Nasaba

‘Yan Adawa Sun Dunkule A ADC Don Tunkarar Tinubu A 2027

Ku Manta Da 2027, Tinubu Zai Ci Gaba Da Mulki Har 2031 — Fadar Shugaban Ƙasa Ga ADC

Ta bayyana Maryam Abacha a matsayin mace mai hazaka kuma jajirtacciya wajen ci gaban nahiyar Afrika baki daya.

 

“Shawararta ne ya samar da ma’aikatar harkokin mata ta tarayya tare da nada mace a matsayin minista, wanda hakan ya fadada zuwa jihohi daban-daban tare da girmama al’amuran matan Nijeriya.

 

“A kwanan nan a yayin sauya sunan wannan cibiya, na jaddada wa mata cewa su dinke barakar da ke tsakaninsu, su nuna halaye masu kyau da kuma mayar da hankali fiye da bambance-bambancen da ke tsakaninmu, kasancewar hadin kan mu a matsayin mata ya fi muhimmanci. Wannan taron yana da mahimmanci a yayin da ya zama babban dama na kafa tarihi wajen samar da dawwamammen zaman lafiya a cikin al’ummarmu.

 

“A yayin cimma burinmu, yana da kyau mu fahimta tare da karrama mutanen da suka taka muhimmiyar rawa wajen bunkasa da zaman lafiya da kwanciyar hankali.”

 

Bayanin na uwargidan shugaban kasar ya yi daidai da tunanin sauran masu jawabi a wurin taron, ciki har da Darakta Janar na cibiyar, Misis Asabe Vilita Bashir, da Sakatariyar Ma’aikatar harkokin mata, Misis Monilola Udoh.

 

Dukkanninsu sun yi murnar yadda mata ke samun tagomashi a gwamnatance a fagen sake gina kasa.

 

A nata jawabin, Dakta Maryam Abacha ta yi addu’a ga kasar nan da kuma wannan gwamnati mai ci a karkashin jagorancin shugaban kasa Bola Tinubu da mataimakin shugaban kasa Kashim Shettima akan Allah ya ba su ikon cimma nasara.

 

Ta ce galibin matan da ke rike da madafun iko a yau suna da ilimi sosai, inda ta shawarce su a kan su yi amfani da damar da suka samu wajen yin ci gaban al’umma.

 

Ta yi fatan cewa uwargidan shugaban kasa, Sanata Oluremi Tinubu za ta yi aiki mai kyau.

 

Ta kuma ba da shawarar cewa ya kamata a karfafa wa dukkan mata gwiwa su zama masu amfani da kuma dacewa wajen ci gaban kasa.

 

“Ina so na roke ku da cewa ka da a bar mace a baya wajen daukar nauyi. Na yi farin ciki da na kasance jigo wajen kafa wannan cibiya kuma ina godiya ga uwargidan shugaban kasa da cibiyar bisa ganin na cancanci a sanya sunana a wannan katafaren gini haka”.

 

“Zan tattaro wasu tattaunawarmu da wasu ayyukanmu a cikin kundi kuma ina ƙarfafa ku da ku zama masu ƙwazo domin a zamaninmu, yawancin mu ba mu kammala karatun digiri ba. Mun yi iya bakin kokarinmu muka bar sauran amma yanzu muna da wadanda suka samu ilimi da wayewa da za su kai ‘yan Nijeriya mafi kyawun wuri ga mata”.

 

Taron ya kasance babban wuri wajen bayyana bayanan zaman lafiya da goyon baya a tsakanin mata.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

ShareTweetSendShare
Previous Post

Juyin Mulki: Tinubu Ya Gana Da Gwamnonin Jihohin Da Ke Kan Iyaka Da Jamhuriyar Nijar

Next Post

‘Yansanda Sun Tabbatar Da Sace Basarake Da Matarsa A Jihar Nasarawa. 

Related

‘Yan Adawa Sun Dunkule A ADC Don Tunkarar Tinubu A 2027
Labarai

‘Yan Adawa Sun Dunkule A ADC Don Tunkarar Tinubu A 2027

9 hours ago
Ku Manta Da 2027, Tinubu Zai Ci Gaba Da Mulki Har 2031 — Fadar Shugaban Ƙasa Ga ADC
Manyan Labarai

Ku Manta Da 2027, Tinubu Zai Ci Gaba Da Mulki Har 2031 — Fadar Shugaban Ƙasa Ga ADC

10 hours ago
ALGON Ta Taya Gwamnan Sani Murnar Samun Lambar Yabo Ta Kasa
Labarai

ALGON Ta Taya Gwamnan Sani Murnar Samun Lambar Yabo Ta Kasa

17 hours ago
Kwankwaso Ba Zai Sake Yi Mana Takarar Shugabancin Ƙasa Ba A Zaɓen 2027 Ba – NNPP
Manyan Labarai

Kwankwaso Ba Zai Sake Yi Mana Takarar Shugabancin Ƙasa Ba A Zaɓen 2027 Ba – NNPP

17 hours ago
An Yi Wa ‘Yar Shekara 18 Fyade Har Lahira A Taraba
Kotu Da Ɗansanda

An Kama Matashin Da Ya Yi Garkuwa Da Abokinsa Tare Da Karbar Kudin Fansa

20 hours ago
Gwamna Ademola Adeleke Ya Ƙaryata Jita-Jitar Sauya Sheƙa Daga PDP Zuwa APC
Manyan Labarai

Gwamna Ademola Adeleke Ya Ƙaryata Jita-Jitar Sauya Sheƙa Daga PDP Zuwa APC

21 hours ago
Next Post
Da Dumi-duminsa: ‘Yan Bindiga Sun Yi Garkuwa Da Basarake A Ondo

‘Yansanda Sun Tabbatar Da Sace Basarake Da Matarsa A Jihar Nasarawa. 

LABARAI MASU NASABA

Gobe Za A Fara Wasannin Kofin Afirka Na Mata

Gobe Za A Fara Wasannin Kofin Afirka Na Mata

July 6, 2025
Wang Yi: Amfani Da Karfin Soji Ba Bisa Ka’ida Ba Na Ingiza Karuwar Tashin Hankali

Wang Yi: Amfani Da Karfin Soji Ba Bisa Ka’ida Ba Na Ingiza Karuwar Tashin Hankali

July 5, 2025
Shawarar Ziri Daya Da Hanya Daya Na Cike Da Hangen Nesa Da Burikan Samar Da Ci Gaba In Ji Firaministan Kasar Senegal

Shawarar Ziri Daya Da Hanya Daya Na Cike Da Hangen Nesa Da Burikan Samar Da Ci Gaba In Ji Firaministan Kasar Senegal

July 5, 2025
‘Yan Adawa Sun Dunkule A ADC Don Tunkarar Tinubu A 2027

‘Yan Adawa Sun Dunkule A ADC Don Tunkarar Tinubu A 2027

July 5, 2025
Wakilin Sin Ya Yi Jawabi Game Da Raya Hidimomi Ga Nakasassu Ta Hanyar Fasahar AI A Madadin Wakilan Kasashe Fiye Da 70

Wakilin Sin Ya Yi Jawabi Game Da Raya Hidimomi Ga Nakasassu Ta Hanyar Fasahar AI A Madadin Wakilan Kasashe Fiye Da 70

July 5, 2025
Ku Manta Da 2027, Tinubu Zai Ci Gaba Da Mulki Har 2031 — Fadar Shugaban Ƙasa Ga ADC

Ku Manta Da 2027, Tinubu Zai Ci Gaba Da Mulki Har 2031 — Fadar Shugaban Ƙasa Ga ADC

July 5, 2025
Zan Dade Ban Manta Da Mahaifinmu Ba -Abba Sadau

Zan Dade Ban Manta Da Mahaifinmu Ba -Abba Sadau

July 5, 2025
Kuri’ar Jin Ra’ayin Jama’a Ta CGTN Ta Nuna Goyon Baya Ga Fadadar Kungiyar BRICS A Matsayin Hanyar Bunkasa Hadin Gwiwa

Kuri’ar Jin Ra’ayin Jama’a Ta CGTN Ta Nuna Goyon Baya Ga Fadadar Kungiyar BRICS A Matsayin Hanyar Bunkasa Hadin Gwiwa

July 5, 2025
Gidajen Gala Ne Kadai Mafita Ga Masana’antar Kannywood – Falalu Dorayi

Gidajen Gala Ne Kadai Mafita Ga Masana’antar Kannywood – Falalu Dorayi

July 5, 2025
Wang Yi Da Takwaransa Na Ghana Sun Aikewa Juna Sakon Murnar Cika Shekaru 65 Da Kulla Dangantakar Diplomasiyya A Tsakanin Kasashensu

Wang Yi Da Takwaransa Na Ghana Sun Aikewa Juna Sakon Murnar Cika Shekaru 65 Da Kulla Dangantakar Diplomasiyya A Tsakanin Kasashensu

July 5, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.